• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Na Fuskantar Koma-baya A Noman Alkama, Masara Da Gero – Rahoto

by Abubakar Abba
2 years ago
Nijeriya

A wani rahoton hadaka na hasashen harkokin kasuwanci na yankin Afirka, wanda Hukumar Abinci da Aikin Gona ta Duniya (FAO), tare da shirin samar da abinci na duniya (WFP) suka wallafa a kwanan baya, an yi hasashen cewa, za a samu koma baya a bangaren noman kayan amfanin gona a Nijeriya, Nijar, Chadi da kuma Mali.

A cewar rahoton, an yi hasashen tashin farashin wadannan kayan amfanin gona a daukacin wannan nahiya, a yayin kuma da ake sa ran ci gaba da kara bukatarsu.

  • Bangaren Cinikayyar Waje Na Sin Ya Samu Babban Sakamako A 2023
  • Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Tantuna Don ‘Yan Gudun Hijira Da Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

Kazalika, rahoton ya danganta afkuwar hakan a kan kalubalen hada-hadar kasuwancin amfanin tare da kalubalen rashin tsaro da kuma matsin tattalin arzikin da ake fuskanta a wadannan nahiyoyi.

Sakamakon wannan hasashe da rahoton ya yi na samun koma baya a kan noman wadannan kayan abinci, hakan zai shafi farashin amfanin gonar kamar Masara, Alkama, Shinkafa, Gero da sauran makamantansu har nan da sama da shekaru biyar masu zuwa.

Misali, a Nijeriya idan aka yi la’akari da irin tafiyar hawainiyar da tattalin arzikin kasar yake yi, rahoton ya yi hasashen samun raguwar yin noma a fadin kasar baki-daya, wanda hakan kuma zai yi sanadiyyar tashin farashin kayan abincin ya ci gaba da yin tashin gwauron zabi.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

Kazalika, rahoton ya yi hasashen cewa, za a samu matukar raguwa wajen noman Shinkafa, Masara, Dawa da kuma Gero. Bugu da kari kuma, za a samu raguwar noman amfanin gona a Nijeriya da Nijar da Chadi da kuma Mali.

Har ila yau, rahoton ya bayyana cewa, sakamakon kalubalen rashin tsaro da rikice-rikice, musamman a yankin Liptako-Gourma da kuma gabar Kogin Chadi, akwai yiwuwar a haramta fitar da kaya wanda Kungiyar Tattalin Arzikin Kasashen Afirka (ECOWAS), za ta kakaba wa yankunan; wanda hakan ya jawo a watannin baya kungiyar ta kakaba wa Kasar Nijar wannan takunkumi, wanda ya yi sanadiyyar dakatar da hada-hadar zirga-zirgar gudanar da kasuwanci a tsakaninsu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Ɓarayi 13 Tare Da Ƙwato Shanu 27 A Kaduna
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

October 18, 2025
Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI
Noma Da Kiwo

Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI

October 18, 2025
Next Post
Gwamnatin Kaduna Za Ta Sa Kafar Wando Da Masu Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba

Gwamnatin Kaduna Za Ta Sa Kafar Wando Da Masu Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka'ida Ba

LABARAI MASU NASABA

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa

November 1, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu

Jerin Gwarazan Taurarinmu

November 1, 2025
CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.