• English
  • Business News
Wednesday, July 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Na Fuskantar Koma-baya A Noman Alkama, Masara Da Gero – Rahoto

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Nijeriya Na Fuskantar Koma-baya A Noman Alkama, Masara Da Gero – Rahoto
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani rahoton hadaka na hasashen harkokin kasuwanci na yankin Afirka, wanda Hukumar Abinci da Aikin Gona ta Duniya (FAO), tare da shirin samar da abinci na duniya (WFP) suka wallafa a kwanan baya, an yi hasashen cewa, za a samu koma baya a bangaren noman kayan amfanin gona a Nijeriya, Nijar, Chadi da kuma Mali.

A cewar rahoton, an yi hasashen tashin farashin wadannan kayan amfanin gona a daukacin wannan nahiya, a yayin kuma da ake sa ran ci gaba da kara bukatarsu.

  • Bangaren Cinikayyar Waje Na Sin Ya Samu Babban Sakamako A 2023
  • Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Tantuna Don ‘Yan Gudun Hijira Da Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

Kazalika, rahoton ya danganta afkuwar hakan a kan kalubalen hada-hadar kasuwancin amfanin tare da kalubalen rashin tsaro da kuma matsin tattalin arzikin da ake fuskanta a wadannan nahiyoyi.

Sakamakon wannan hasashe da rahoton ya yi na samun koma baya a kan noman wadannan kayan abinci, hakan zai shafi farashin amfanin gonar kamar Masara, Alkama, Shinkafa, Gero da sauran makamantansu har nan da sama da shekaru biyar masu zuwa.

Misali, a Nijeriya idan aka yi la’akari da irin tafiyar hawainiyar da tattalin arzikin kasar yake yi, rahoton ya yi hasashen samun raguwar yin noma a fadin kasar baki-daya, wanda hakan kuma zai yi sanadiyyar tashin farashin kayan abincin ya ci gaba da yin tashin gwauron zabi.

Labarai Masu Nasaba

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Kazalika, rahoton ya yi hasashen cewa, za a samu matukar raguwa wajen noman Shinkafa, Masara, Dawa da kuma Gero. Bugu da kari kuma, za a samu raguwar noman amfanin gona a Nijeriya da Nijar da Chadi da kuma Mali.

Har ila yau, rahoton ya bayyana cewa, sakamakon kalubalen rashin tsaro da rikice-rikice, musamman a yankin Liptako-Gourma da kuma gabar Kogin Chadi, akwai yiwuwar a haramta fitar da kaya wanda Kungiyar Tattalin Arzikin Kasashen Afirka (ECOWAS), za ta kakaba wa yankunan; wanda hakan ya jawo a watannin baya kungiyar ta kakaba wa Kasar Nijar wannan takunkumi, wanda ya yi sanadiyyar dakatar da hada-hadar zirga-zirgar gudanar da kasuwanci a tsakaninsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Noman alkamaNoman GeroNoman rani
ShareTweetSendShare
Previous Post

Liu Jianchao Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Next Post

Gwamnatin Kaduna Za Ta Sa Kafar Wando Da Masu Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba

Related

Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika
Noma Da Kiwo

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

4 days ago
Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

5 days ago
Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

2 weeks ago
Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci

2 weeks ago
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar
Noma Da Kiwo

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

2 weeks ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

3 weeks ago
Next Post
Gwamnatin Kaduna Za Ta Sa Kafar Wando Da Masu Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba

Gwamnatin Kaduna Za Ta Sa Kafar Wando Da Masu Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka'ida Ba

LABARAI MASU NASABA

Kwalejin Digiri Na Biyu Ta ABU Ta Ƙaddamar Da Sabbin Ɗalibai A Zariya

Kwalejin Digiri Na Biyu Ta ABU Ta Ƙaddamar Da Sabbin Ɗalibai A Zariya

July 16, 2025
An Gudanar Da Taron Ministocin Wajen Kasashe Mambobin SCO A Tianjin

An Gudanar Da Taron Ministocin Wajen Kasashe Mambobin SCO A Tianjin

July 16, 2025
PDP Ba Za Ta Damu Da Rashin Atiku Ba – Gwamna Makinde

PDP Ba Za Ta Damu Da Rashin Atiku Ba – Gwamna Makinde

July 16, 2025
Fasahar Amfani Da ’Yan Sandan Mutum-Mutumi Ta Kasar Sin Na Iya Taimaka Wa Tsaro A Afirka

Fasahar Amfani Da ’Yan Sandan Mutum-Mutumi Ta Kasar Sin Na Iya Taimaka Wa Tsaro A Afirka

July 16, 2025
Farashin Kayayyaki Sun Sauka A Watan Yuni 2025

Farashin Kayayyaki Sun Sauka A Watan Yuni 2025

July 16, 2025
Kasar Sin Na Inganta Samun Nasara Ga Kowane Bangare A Fannin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki A Duniya

Kasar Sin Na Inganta Samun Nasara Ga Kowane Bangare A Fannin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki A Duniya

July 16, 2025
Afrika Ta Zama Kasuwar Sayar Da Man Fetur Mara Inganci – Dangote

Afrika Ta Zama Kasuwar Sayar Da Man Fetur Mara Inganci – Dangote

July 16, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Ta’aziyya Zuwa Ga Takwaransa Na Najeriya Bisa Rasuwar Muhammadu Buhari

Xi Jinping Ya Mika Sakon Ta’aziyya Zuwa Ga Takwaransa Na Najeriya Bisa Rasuwar Muhammadu Buhari

July 16, 2025
An Fara Binciken Mutuwar Wasu Ɗalibai 2 A Makarantar Kwana A Kano

An Fara Binciken Mutuwar Wasu Ɗalibai 2 A Makarantar Kwana A Kano

July 16, 2025
Atiku Abubakar Ya Fice Daga PDP, Duba Dalili

Atiku Abubakar Ya Fice Daga PDP, Duba Dalili

July 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.