Nijeriya na ƙoƙarin samun rancen Dala biliyan biyar daga ƙasar Saudiyya, amma an samu tsaiko a tattaunawar saboda sauyin farashin ɗanyen mai a kasuwannin duniya.
Wannan rancen ana sa ran cewa kamfanin man fetur na Saudiyya, Aramco, ne zai bayar, kuma Nijeriya za ta biya da ɗanyen mai.
- Wang Yi Ya Gabatar Da Jawabi Albarkacin “Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa” Karo Na Farko Na MDD
- Sin Na Maraba Da Karin ‘Yan Kasuwar Ketare Dake Son Gudanar Da Hada-hada Don Cimma Moriyar Juna
Wani rahoto daga kamfanin dillancin labarai na Reuters ya bayyana cewa faɗuwar farashin ɗanyen mai nau’in Brent daga Dala 82 zuwa Dala 65 tun daga watan Janairu ya sa bankunan da za su taimaka wajen aiwatar da rancen suka fara nuna shakku.
Idan aka ci gaba da wannan tattaunawa, Nijeriya za ta ƙara yawan mai da za ta biya da shi don biyan bashin.
Tatttaunawa kan wannan rance dai ta fara ne tun cikin watan Nuwamban 2024 lokacin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya gana da Yarima Muhammad Bin Salman a taron tattalin arziƙi tsakanin Saudiyya da ƙasashen Afrika.
Amma har zuwa yanzu, babu cikakken bayani daga Gwamnatin Tarayya.
A watan Mayun 2025 ne Tinubu ya miƙa buƙatar samun amincewar majalisa domin karɓar rancen Dala biliyan 21 daga ƙasashen waje, ciki har da Dala biliyan biyar daga Aramco.
Rahoton Reuters bai bayyana sunayen bankunan da za su taimaka ba, amma majiyoyi sun ce ɗaya daga cikin bankunan na nahiyar Afrika ne, sauran kuma daga Gabas ta Tsakiya.
Idan aka cimma yarjejeniyar, wannan zai zama mafi girma daga cikin bashin da Nijeriya ta taɓa karɓa a irin wannan hanya daga Saudiyya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp