Tawagar Super Eagles ta Nijeriya ta samu nasarar lashe kofin Unity Cup bayan doke kasar Jamaica da ci 5-4 a bugun daga kai sai mai tsaron raga da suka buga bayan an tashi canjaras a mintuna 90.
Kyaftin din Nijeriya Moses Simon ne ya fara zurawa Nijeriya kwallo a minti na 9 da fara wasan kafin Dixon ya farkewa Jamaica mintuna 7 tsakani, bayan dawowa daga hutun rabin lokaci Samuel Chukwueze ya ci wa Nijeriya kwallo ta biyu .
- Mutane 21 Sun Mutu A Tawagar Ƴan Wasannin Kano A Hatsarin Mota
- Ƙungiyar Gwamnoni Sun Yi Ta’aziya Kan Rasuwar Ƴan Wasan Kano 21
A minti na 67 Jonathan Russell ya ci wa Jamaica kwallo ta biyu, an shafe sauran mintuna 20 na wasan ana bata kashi yayinda kasashen biyu ke kai munanan hare hare ga raga.
Bayan mintuna 90 na wasan ba tareda wani ya doke wani ba sai alkalin wasa ya bayar da damar bugun daga kai sai mai tsaron raga, Jamaica ta ci kwallaye 4 inda Nijeriya ta ci dukkan kwallaye 5 da yan wasan suka buga, hakan ya sa yaran na Eric Chelle suka lashe gasar Unity Cup ta bana da ta kunshi kasashen Ghana, Trinidad And Tobago, Jamaica da Nijeriya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp