• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Ta Nemi Kasashe Su Tunkari Matsalolin Gudun Hijira Da Shige Da Fice Gadan-gadan

by Sulaiman
3 years ago
in Labarai
0
Nijeriya Ta Nemi Kasashe Su Tunkari Matsalolin Gudun Hijira Da Shige Da Fice Gadan-gadan
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Nijeriya ta yi kira ga sauran ƙasashe da su haɗa gwiwa domin nemo hanyoyin da za a bi a magance matsalolin da su ka danganci shige-da-fice da gudun hijira.

Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji Da Inganta Rayuwa, Hajiya Sadiya Umar Farouq, ita ce ta yi wannan kiran a jawabin da ta gabatar a ranar Litinin a wajen Taro na 73 na Babban Kwamitin Gudanarwa na Kwamishinan Hukumar ‘Yan Gudun Hijira ta Majalisar Ɗinkin Duniya (UNHCR) a birnin Geneva.

  • Ayyukanmu Duk Sun Karade Ko’ina A Fadin Nijeriya —Sadiya Farouq

Mai tallafa wa ministar a aikin jarida, Miss Nneka Ikem Anibeze, ta ruwaito cewa Hajiya Sadiya ta bayyana irin ƙoƙari da kuma da tsare-tsaren da gwamnatin Nijeriya ta ke fito da su domin inganta ayyukan agaji a Nijeriya musamman ma kan batun ‘yan gudun hijira da masu shige-da-fice tsakanin ƙasashe da kuma ‘yan gudun hijira na cikin ƙasa.

Ministar ta yi kira ga ƙasashe masu ruwa da tsaki a lamarin da su guji nuna bambanci da wariyar launin fata domin gina zaman lafiya mai ɗorewa tare da inganta hanyoyin samun abinci ga al’umma mabuƙata.

Ta ce: “Nijeriya ta na kira ga ƙasashe da su haɗa gwiwa tare da haɗa kai da ɗaukar nauyi da zama tsintsiya maɗaurin ki ɗaya musamman a kan yadda matsalar ke shafar ƙasashe inda ‘yan gudun hijira ke fitowa da ƙasashen da ke karɓar su. Wannan ya yi daidai da sadaukarwar mu a matsayin membobin Yarjejeniyar Ƙasashe Kan ‘Yan Gudun Hijira.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

“Nijeriya ta yabi ƙoƙarin UNHCR. Mu na kuma kira ga UNHCR da sauran masu ruwa da tsaki kan batun shige-da-fice da su ci gaba da su haɗa hannu da gwamnatin Nijeriya domin a daidaita tsare-tsare da manufofin mu na cigaban ƙasa da muradan ta.

“Matsalar da ake samu daga sauyin yanayi a Fadamar Tafkin Chadi ta haifar da ƙarin yawan mutanen da aka tilasta wa barin yankin.”

Ta lura da cewa a cikin ‘yan lokutan nan ambaliya da sauran manyan al’amuran sauyin yanayi sun ba da gudunmawa ga ƙaruwar ‘yan gudun hijira.

Ta ce, “A namu ɓangaren na gwamnati, mu na aiwatar da Shirin Ko-ta-kwana na Samar da Abincin Gaggawa domin inganta shiryawa da ƙarfafawa ga al’umma kamar yadda aka tsara a Tsarin Sendai.”

Hajiya Sadiya ta ce: “Mu na neman a haɗa gwiwa domin a rage tare da shirya zama da sauyin yanayi musamman a wajen batun tilasta wa mutane barin waje.

“Wariyar launin fata da nuna bambanci ba abubuwa ne da za a bar su su samu gindin zama a duniyar mu ta yau ba idan har mu na so mu gina zaman lafiya mai ɗorewa, samar da arziki da kuma inganta sana’o’i da juriya ta yadda za a kyautata ƙasa tare da kare al’umma marasa ƙarfi.”

A ƙarƙashin Yarjejeniya Uku da aka rattaba tsakanin Nijeriya, Kamaru da UNHCR, sama da ‘yan gudun hijira 5,000 ‘yan Nijeriya aka sake dawowa da su cikin ƙasar su bisa amincewar su.

Ta ce a cikin shekaru shidda da su ka gabata, Nijeriya ta samu ƙarin yawaitar masu neman mafaka da ‘yan gudun hijira daga ƙasashe da ke maƙwabtaka da mu.

Yanzu haka Nijeriya ta na mai masaukin baƙi na ‘yan gudun hijira su 84,314 da masu neman mafaka daga ƙasashe sama da 34, ga kuma ƙarin sama da ‘yan gudun hijira 5,000 daga Kamaru waɗanda ba su da rajista, waɗanda su ka iso kwanan nan.

“Akwai ‘yan gudun hijira ‘yan Nijeriya kimanin 341,642 a ƙasashen Nijar, Chadi da Kamaru,” inji ta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Peng Liyuan Ta Aike Da Sakon Taya Murna Ga Taron Karrama Wadanda Suka Yi Fice A Fannin Tallafawa Ilimin Mata

Next Post

Abinda Ya Sa Naki Amincewa Na Wa Obi Mataimaki —Shagari

Related

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

2 hours ago
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

4 hours ago
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

19 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

19 hours ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

20 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

20 hours ago
Next Post
Abinda Ya Sa Naki Amincewa Na Wa Obi Mataimaki —Shagari

Abinda Ya Sa Naki Amincewa Na Wa Obi Mataimaki —Shagari

LABARAI MASU NASABA

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

June 29, 2025
Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

June 29, 2025
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.