• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Ta Nemi Kasashe Su Tunkari Matsalolin Gudun Hijira Da Shige Da Fice Gadan-gadan

bySulaiman
3 years ago
Nijeriya

Nijeriya ta yi kira ga sauran ƙasashe da su haɗa gwiwa domin nemo hanyoyin da za a bi a magance matsalolin da su ka danganci shige-da-fice da gudun hijira.

Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji Da Inganta Rayuwa, Hajiya Sadiya Umar Farouq, ita ce ta yi wannan kiran a jawabin da ta gabatar a ranar Litinin a wajen Taro na 73 na Babban Kwamitin Gudanarwa na Kwamishinan Hukumar ‘Yan Gudun Hijira ta Majalisar Ɗinkin Duniya (UNHCR) a birnin Geneva.

  • Ayyukanmu Duk Sun Karade Ko’ina A Fadin Nijeriya —Sadiya Farouq

Mai tallafa wa ministar a aikin jarida, Miss Nneka Ikem Anibeze, ta ruwaito cewa Hajiya Sadiya ta bayyana irin ƙoƙari da kuma da tsare-tsaren da gwamnatin Nijeriya ta ke fito da su domin inganta ayyukan agaji a Nijeriya musamman ma kan batun ‘yan gudun hijira da masu shige-da-fice tsakanin ƙasashe da kuma ‘yan gudun hijira na cikin ƙasa.

Ministar ta yi kira ga ƙasashe masu ruwa da tsaki a lamarin da su guji nuna bambanci da wariyar launin fata domin gina zaman lafiya mai ɗorewa tare da inganta hanyoyin samun abinci ga al’umma mabuƙata.

Ta ce: “Nijeriya ta na kira ga ƙasashe da su haɗa gwiwa tare da haɗa kai da ɗaukar nauyi da zama tsintsiya maɗaurin ki ɗaya musamman a kan yadda matsalar ke shafar ƙasashe inda ‘yan gudun hijira ke fitowa da ƙasashen da ke karɓar su. Wannan ya yi daidai da sadaukarwar mu a matsayin membobin Yarjejeniyar Ƙasashe Kan ‘Yan Gudun Hijira.

LABARAI MASU NASABA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

“Nijeriya ta yabi ƙoƙarin UNHCR. Mu na kuma kira ga UNHCR da sauran masu ruwa da tsaki kan batun shige-da-fice da su ci gaba da su haɗa hannu da gwamnatin Nijeriya domin a daidaita tsare-tsare da manufofin mu na cigaban ƙasa da muradan ta.

“Matsalar da ake samu daga sauyin yanayi a Fadamar Tafkin Chadi ta haifar da ƙarin yawan mutanen da aka tilasta wa barin yankin.”

Ta lura da cewa a cikin ‘yan lokutan nan ambaliya da sauran manyan al’amuran sauyin yanayi sun ba da gudunmawa ga ƙaruwar ‘yan gudun hijira.

Ta ce, “A namu ɓangaren na gwamnati, mu na aiwatar da Shirin Ko-ta-kwana na Samar da Abincin Gaggawa domin inganta shiryawa da ƙarfafawa ga al’umma kamar yadda aka tsara a Tsarin Sendai.”

Hajiya Sadiya ta ce: “Mu na neman a haɗa gwiwa domin a rage tare da shirya zama da sauyin yanayi musamman a wajen batun tilasta wa mutane barin waje.

“Wariyar launin fata da nuna bambanci ba abubuwa ne da za a bar su su samu gindin zama a duniyar mu ta yau ba idan har mu na so mu gina zaman lafiya mai ɗorewa, samar da arziki da kuma inganta sana’o’i da juriya ta yadda za a kyautata ƙasa tare da kare al’umma marasa ƙarfi.”

A ƙarƙashin Yarjejeniya Uku da aka rattaba tsakanin Nijeriya, Kamaru da UNHCR, sama da ‘yan gudun hijira 5,000 ‘yan Nijeriya aka sake dawowa da su cikin ƙasar su bisa amincewar su.

Ta ce a cikin shekaru shidda da su ka gabata, Nijeriya ta samu ƙarin yawaitar masu neman mafaka da ‘yan gudun hijira daga ƙasashe da ke maƙwabtaka da mu.

Yanzu haka Nijeriya ta na mai masaukin baƙi na ‘yan gudun hijira su 84,314 da masu neman mafaka daga ƙasashe sama da 34, ga kuma ƙarin sama da ‘yan gudun hijira 5,000 daga Kamaru waɗanda ba su da rajista, waɗanda su ka iso kwanan nan.

“Akwai ‘yan gudun hijira ‘yan Nijeriya kimanin 341,642 a ƙasashen Nijar, Chadi da Kamaru,” inji ta.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu
Siyasa

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Next Post
Abinda Ya Sa Naki Amincewa Na Wa Obi Mataimaki —Shagari

Abinda Ya Sa Naki Amincewa Na Wa Obi Mataimaki —Shagari

LABARAI MASU NASABA

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version