ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ayyukanmu Duk Sun Karade Ko’ina A Fadin Nijeriya —Sadiya Farouq

by Sulaiman
4 years ago
Sadiya

Ministar Harkokin Jin kai, Agaji da Inganta Rayuwa, Sadiya Farouq ta bayyana cewa ba gaskiya ba ne ikirarin da wasu ke yi cewa wai ba ta rarraba ayyukan ta a dukkan sassan Nijeriya ba, sai wani yanki kadai, sannan kuma wai ba ta yin aikin ta yadda ya kamata.

Ta ce ita ayyukanta ta na gudanar da su ne a kowace jiha a kasar nan da kuma Gundumar Babban Birnin Tarayya.

  • Miyetti Allah Ta Maka Gwamna Ortom A Kotu Kan Kwace Wuraren Yin Kiwo A Jihar Benuwai

Ministar ta yi wannan kalami ne yayin maida martani kan Ikirarin Bibi Dogo wanda ya saka talla a jaridar Daily Trust ta ranar Litinin, 9 ga Agusta, 2022 inda ya yi kira ga Shugaba Buhari da ya kore ta saboda wai ba ta yin aikin ta yadda ya kamata.

ADVERTISEMENT

A sanarwar da mai taimakawa ministar a fagen yada labarai, Nneka Ikem Anibeze ta fitar, ta bayyana cewa a zahiri Dogo, wanda ya ce shi dattijo ne a jam’iyyar PDP a Karamar Hukumar Bauchi, ya yi magana ne a madadin wasu wadanda ke adawa da ministar, wadanda za a iya gane su ta hanyar karairayin da su ke yadawa.

Ta ce ikirarin da ya yi ba gaskiya ba ne ko kadan, kawai ya wawuko shaci-fadi ne a kan ministar da ofishin ta.

LABARAI MASU NASABA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

Misali, Dogo ya ce wai ministar ta na amfani da dukiyar gwamnati ta na yin “katsalandan” a siyasar Jihar Bauchi, sannan wai ta na yin haka ne domin mara wa siyasar mijin ta baya a takarar zama gwamnan jihar da ya ke yi a ƙarƙashin tutar jam’iyyar APC.

Haka kuma ya ce ministar ba ta yi komai ba wajen taimakon matan jihar ta ta Zamfara.

A cewar Anibeze, manufar wannan mutum wanda bai ma san kakakin jam’iyyar su na yanzu ba, shi da masu ɗaukar nauyin sa, ita ce su yaudari mutane da labaran ƙanzon kurege tare da haifar da tsana da gaba, sannan su ɗauke hankalin ma’aikatar tare da shafa wa aikin ta kashin kaji.

Ta ce in ba domin kada wasu tsiraru su gaskata ƙarairayin sa ba, to da ma’aikatar ba ta ce masa ƙala ba, amma ya zama wajibi a amsa masa don gyara illar da ya ke son kawowa kuma a tabbatar wa da masu ruwa da tsaki da kuma miliyoyin mabuƙata masu amfana da ma’aikatar a faɗin ƙasar nan cewa zargin sa ba gaskiya ba ne.

Ta ce a Arewa-maso-gabas akwai jimillar masu cin moriyar shirin N-Power su 167,412 kuma a cikin su mutum 31,942 ‘yan Bauchi ne, yayin da ‘yan makarantar firamare da ma’aikatar ke ciyarwa a yankin sun kai 1,603,617 waɗanda yara 444,099 daga Bauchi ne.

Na biyu, wannan dattijon ya yi ƙaryar wai mutanen yankin Kudu-maso-gabas su na zargin ministar da nuna masu wariya, wai ba ta kai aikin tallafi a jihohin su ba.

Akasin hakan, a cewar mataimakiyar,
akwai ‘yan makarantar firamare 778,450 da ake ciyarwa, sannan a ƙarƙashin shirin N-Power akwai mutum 136,629 a yankin.

Na uku, ya yi iƙirarin wai sama da masu cin moriyar N-Power su 80,000 ba a biya su kuɗin su na watanni biyar ba.

Ta ce wannan ma ƙarya ce domin mutum 14,021 da ba a biya kuɗin wata biyar ba su ne su ka jawo, domin komfutar tsarin biyan alawus na Gwamnatin Tarayya da ake kira ‘Payment system Government Integrated Financial Management Information System’ (GIFMIS) ita ce ta dakatar da biyan su a watan Maris na 2020 saboda dalilai daban-daban.

Dalilan sun haɗa da: mallakar asusun banki sama da ɗaya, da yadda masu cin moriyar shirin su ke amfani da asusun wajen karɓar kuɗaɗe (na albashi ko alawus) daga hukimomi daban-daban na Gwamnatin Tarayya ko kuma su ma’aikatan dindindin ne ko sun shiga wasu shirye-shiryen na gwamnati.

Ta ba da misali da Jihar Bauchi, inda tsarin GIFMIS ya warware matsalolin mutum 191 masu cin moriyar shirin har an biya su kuma sun fita daga shirin.

Su kuma ‘yan N-Power na rukunin ‘Batch C’ an kasa su gida biyu ne, wato C1 da C2. A cikin Satumba 2021 aka ɗauki ‘yan C1 kuma za su kammala shirin a wannan watan na Agusta 2022 bayan sun cika wa’adin watanni 12 a cikin shirin.

Ta ce babu wata ƙumbiya-ƙumbiya wajen biyan, kawai mutum ya yi amfani da tsarin da gwamnati ta amince da shi wajen biya, wato NASIMS, inda duk wani mai cin moriyar shirin zai iya ganin dalilin da ya sa aka biya shi ko aka ƙi biyan shi, misali saboda ƙin zama ya yi aiki.

Su kuma ‘yan rukunin C2 da aka zaɓa, sun gama tirenin da tantancewar gani da ido ta hanyar abokan aikin ma’aikatar na hukumar NYSC. An fara tura mutum 490,000 aiki a ranar 1 ga Agusta inda za su fara shiga gurbin masu cin moriyar N-Power mutum miliyan ɗaya da Shugaban Ƙasa ya amince a ɗauka.

A ƙarshe, ta tabbatar wa da jama’a da abokan hulɗa cewa wannan ma’aikatar ta na nan ba gudu ba ja da baya wajen sauke nauyin da aka ɗora mata.

Ta ce ta lura da yadda ake ɗaukar nauyin wasu domin su kai wa ma’aikatar da ministar hari a kafafen yaɗa labarai don a ɓata masu suna, amma wannan duk yarfen siyasa ne maras amfani. Saboda haka ba za ta tsorata ba ko a ɗauke mata hankali daga kan turbar da ta ke a kai ta kai wa mabuƙata agajin da su ke buƙata.

Sadiya
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
Rahotonni

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Rahotonni

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
Next Post
Kaso 6 Na Al’umma Ne Kadai Ke Ganin Duniya Za Ta Kasance Karkashin Ikon Amurka

Kaso 6 Na Al’umma Ne Kadai Ke Ganin Duniya Za Ta Kasance Karkashin Ikon Amurka

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.