• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Ta Yi  Allah-wadai Da Harin Da Ake Kai Wa ‘Yan Jarida A Gaza, Ta Yi Kira A Gaggauta Tsagaita Wuta 

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Nijeriya Ta Yi  Allah-wadai Da Harin Da Ake Kai Wa ‘Yan Jarida A Gaza, Ta Yi Kira A Gaggauta Tsagaita Wuta 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yi Allah-wadai da harin da sojojin Isra’ila ke kai wa ‘yan jarida a rikicin da ke gudana a ƙasar Falasɗinu, yana mai jaddada cewa, matakin na nuna take haƙƙin ‘yan jarida da kuma haƙƙin ɗan Adam.

 

A cikin wata sanarwa da ya raba wa manema labarai, Mataimaki na Musamman kan Harkokin Yaɗa Labarai ga Ministan, Rabi’u Ibrahim, ya ce Idris ya bayyana hakan ne a jawabin sa a Taro na Musamman na Ministocin Yaɗa Labarai na Ƙasashen Musulmi mai taken: “Bayar Da Labarin Ƙarya Da Kuma Kisan ‘Yan Jarida Da Gwamnatin Isra’ila ke yi a Lokacin Mamayar da Isra’ila ta yi wa Falasɗinu,” wanda aka gudanar a ranar Asabar, 24 ga Fabrairu, 2024 a birnin Istanbul na ƙasar Turkiyya.

  • Wani Sojan Amurka Ya Bankawa Kansa Wuta Don Nuna Goyon Bayansa Ga Falasdinawa
  • Gobara Ta Ƙone Gidan Ƙaramar Ministar Birnin Tarayya Abuja, Mariya Bunkure

Ministan, wanda ya samu wakilcin Shugaban Ofishin Jakadancin Nijeriya a ƙasar Turkiyya, Ambasada Zayyad Abdul-Salam, ya bayyana cewa tun farkon rikicin, ‘yan jarida na ta fuskantar matsantawa, tsoratarwa da tashin hankali, har ma da kisa saboda kawai suna gudanar da aikin su na sanar da jama’a da kiyaye ƙa’idojin gaskiya da adalci.

 

Labarai Masu Nasaba

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

Ya ce: “Daga ƙididdigar da Kwamitin Kare Haƙƙin ‘Yan Jarida na duniya (CPJ) ya bayar, an kashe ‘yan jarida da ma’aikatan kafafen watsa labarai kusan tamanin da takwas tun lokacin da aka fara yaƙin a ranar 7 ga Oktoba, 2023.

 

“A matsayin mu na Ministocin Yaɗa Labarai da ke wakiltar ƙasashe a Ƙungiyar Ƙasashen Musulunci, ya zama wajibi a gare mu da mu yi Allah-wadai da irin wannan ta’asa da tauye haƙƙin ‘yan jarida da ke gudanar da ayyukan su a Falasɗinu.

 

“Dole ne mu tsaya tsayin daka don goyon bayan abokan aikin mu na kafafen yaɗa labarai waɗanda suke sadaukar da rayukan su a kullum don bayar da rahoton rikici a Falasɗinu wacce aka mamaye da kuma ba da murya ga marasa murya.”

 

Idris, wanda ya buƙaci takwarorin sa a ko da yaushe da su dage kan ganin an tabbatar da gaskiya a kowane lokaci ta hanyar neman yanayi mai kyau don bai wa ‘yan jarida damar gudanar da ayyukan su, ya yi tir da duk wani yunƙuri na karkatar da gaskiya tare da rashin bayyana haƙiƙanin halin da mutane ke ciki a Falasɗinu.

 

Ya shawarci ministocin da ke halartar taron da su binciko dabarun sadarwa, goyon baya, da haɗin gwiwa don faɗaɗa muryar ‘yan jarida waɗanda ke da ƙarfin halin tattara bayanan take haƙƙin bil’adama da cin zarafi da ake yi wa al’ummar Falasɗinu.

 

Ya ce: “Babban martanin mu dole ne ya kasance sadaukarwa don kiyaye ƙa’idojin ‘yancin ‘yan jarida, ‘yancin faɗin albarkacin baki, da ‘yancin samun bayanai. Waɗannan muhimman haƙƙoƙin ɗan’adam waɗanda ke cikin dokokin ƙasa da ƙasa sun zama ginshiƙan dimokiraɗiyya da kyakkyawan shugabanci.

 

“Ba za mu ƙyale waɗanda ke neman su murƙushe saɓanin ra’ayi su tattake su kuma su sarrafa labarin ba.”

 

Ministan ya yi kira da a tsagaita buɗe wuta cikin gaggawa a Gaza kuma ya jaddada matsayin Nijeriya kan samar da ƙasashe biyu don magance rikicin Falasɗinu, da tabbatar da an mutunta haƙƙi da ‘yancin al’ummar Falasɗinu da Isra’ila.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Rikicin Falasɗinu da Isra'ilaYakin Rasha Da UkraineYakin zirin gaza
ShareTweetSendShare
Previous Post

Manyan Jami’an JKS Sun Mika Rahoton Ayyukansu Ga Kwamitin Kolin Jam’iyyar

Next Post

Manzon Musamman Na Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Jana’izar Marigayi Shugaba Kasar Namibia Hage Geingob

Related

JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

2 minutes ago
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka
Ra'ayi Riga

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

58 minutes ago
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata
Labarai

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

3 hours ago
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

5 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

7 hours ago
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa
Labarai

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

8 hours ago
Next Post
Manzon Musamman Na Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Jana’izar Marigayi Shugaba Kasar Namibia Hage Geingob

Manzon Musamman Na Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Jana'izar Marigayi Shugaba Kasar Namibia Hage Geingob

LABARAI MASU NASABA

JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

May 14, 2025
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

May 14, 2025
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

May 14, 2025
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.