• English
  • Business News
Sunday, July 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Ta Yi  Allah-wadai Da Harin Da Ake Kai Wa ‘Yan Jarida A Gaza, Ta Yi Kira A Gaggauta Tsagaita Wuta 

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Nijeriya Ta Yi  Allah-wadai Da Harin Da Ake Kai Wa ‘Yan Jarida A Gaza, Ta Yi Kira A Gaggauta Tsagaita Wuta 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yi Allah-wadai da harin da sojojin Isra’ila ke kai wa ‘yan jarida a rikicin da ke gudana a ƙasar Falasɗinu, yana mai jaddada cewa, matakin na nuna take haƙƙin ‘yan jarida da kuma haƙƙin ɗan Adam.

 

A cikin wata sanarwa da ya raba wa manema labarai, Mataimaki na Musamman kan Harkokin Yaɗa Labarai ga Ministan, Rabi’u Ibrahim, ya ce Idris ya bayyana hakan ne a jawabin sa a Taro na Musamman na Ministocin Yaɗa Labarai na Ƙasashen Musulmi mai taken: “Bayar Da Labarin Ƙarya Da Kuma Kisan ‘Yan Jarida Da Gwamnatin Isra’ila ke yi a Lokacin Mamayar da Isra’ila ta yi wa Falasɗinu,” wanda aka gudanar a ranar Asabar, 24 ga Fabrairu, 2024 a birnin Istanbul na ƙasar Turkiyya.

  • Wani Sojan Amurka Ya Bankawa Kansa Wuta Don Nuna Goyon Bayansa Ga Falasdinawa
  • Gobara Ta Ƙone Gidan Ƙaramar Ministar Birnin Tarayya Abuja, Mariya Bunkure

Ministan, wanda ya samu wakilcin Shugaban Ofishin Jakadancin Nijeriya a ƙasar Turkiyya, Ambasada Zayyad Abdul-Salam, ya bayyana cewa tun farkon rikicin, ‘yan jarida na ta fuskantar matsantawa, tsoratarwa da tashin hankali, har ma da kisa saboda kawai suna gudanar da aikin su na sanar da jama’a da kiyaye ƙa’idojin gaskiya da adalci.

 

Labarai Masu Nasaba

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

Ya ce: “Daga ƙididdigar da Kwamitin Kare Haƙƙin ‘Yan Jarida na duniya (CPJ) ya bayar, an kashe ‘yan jarida da ma’aikatan kafafen watsa labarai kusan tamanin da takwas tun lokacin da aka fara yaƙin a ranar 7 ga Oktoba, 2023.

 

“A matsayin mu na Ministocin Yaɗa Labarai da ke wakiltar ƙasashe a Ƙungiyar Ƙasashen Musulunci, ya zama wajibi a gare mu da mu yi Allah-wadai da irin wannan ta’asa da tauye haƙƙin ‘yan jarida da ke gudanar da ayyukan su a Falasɗinu.

 

“Dole ne mu tsaya tsayin daka don goyon bayan abokan aikin mu na kafafen yaɗa labarai waɗanda suke sadaukar da rayukan su a kullum don bayar da rahoton rikici a Falasɗinu wacce aka mamaye da kuma ba da murya ga marasa murya.”

 

Idris, wanda ya buƙaci takwarorin sa a ko da yaushe da su dage kan ganin an tabbatar da gaskiya a kowane lokaci ta hanyar neman yanayi mai kyau don bai wa ‘yan jarida damar gudanar da ayyukan su, ya yi tir da duk wani yunƙuri na karkatar da gaskiya tare da rashin bayyana haƙiƙanin halin da mutane ke ciki a Falasɗinu.

 

Ya shawarci ministocin da ke halartar taron da su binciko dabarun sadarwa, goyon baya, da haɗin gwiwa don faɗaɗa muryar ‘yan jarida waɗanda ke da ƙarfin halin tattara bayanan take haƙƙin bil’adama da cin zarafi da ake yi wa al’ummar Falasɗinu.

 

Ya ce: “Babban martanin mu dole ne ya kasance sadaukarwa don kiyaye ƙa’idojin ‘yancin ‘yan jarida, ‘yancin faɗin albarkacin baki, da ‘yancin samun bayanai. Waɗannan muhimman haƙƙoƙin ɗan’adam waɗanda ke cikin dokokin ƙasa da ƙasa sun zama ginshiƙan dimokiraɗiyya da kyakkyawan shugabanci.

 

“Ba za mu ƙyale waɗanda ke neman su murƙushe saɓanin ra’ayi su tattake su kuma su sarrafa labarin ba.”

 

Ministan ya yi kira da a tsagaita buɗe wuta cikin gaggawa a Gaza kuma ya jaddada matsayin Nijeriya kan samar da ƙasashe biyu don magance rikicin Falasɗinu, da tabbatar da an mutunta haƙƙi da ‘yancin al’ummar Falasɗinu da Isra’ila.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Rikicin Falasɗinu da Isra'ilaYakin Rasha Da UkraineYakin zirin gaza
ShareTweetSendShare
Previous Post

Manyan Jami’an JKS Sun Mika Rahoton Ayyukansu Ga Kwamitin Kolin Jam’iyyar

Next Post

Manzon Musamman Na Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Jana’izar Marigayi Shugaba Kasar Namibia Hage Geingob

Related

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya
Labarai

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

10 hours ago
Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025
Labaran Kasuwanci

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

12 hours ago
Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista
Labarai

Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

14 hours ago
Gwamnan Katsina Ya Dakatar Da Ma’aikatan Gidan Gyaran Hali Saboda Azabtar Da Wani Matashi
Labarai

Gwamnan Katsina Ya Dakatar Da Ma’aikatan Gidan Gyaran Hali Saboda Azabtar Da Wani Matashi

16 hours ago
2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu
Manyan Labarai

2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu

17 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Shettima Ya Ziyarci Buhari A Landan Cikin Sirri Don Duba Lafiyarsa

18 hours ago
Next Post
Manzon Musamman Na Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Jana’izar Marigayi Shugaba Kasar Namibia Hage Geingob

Manzon Musamman Na Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Jana'izar Marigayi Shugaba Kasar Namibia Hage Geingob

LABARAI MASU NASABA

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

July 12, 2025
Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

July 12, 2025
Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

July 12, 2025
Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

July 12, 2025
Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

July 12, 2025
Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

July 12, 2025
Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

July 12, 2025
Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

July 12, 2025
Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

July 12, 2025
Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

July 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.