ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Ta Yi  Allah-wadai Da Harin Da Ake Kai Wa ‘Yan Jarida A Gaza, Ta Yi Kira A Gaggauta Tsagaita Wuta 

by Sulaiman
2 years ago
Gaza

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yi Allah-wadai da harin da sojojin Isra’ila ke kai wa ‘yan jarida a rikicin da ke gudana a ƙasar Falasɗinu, yana mai jaddada cewa, matakin na nuna take haƙƙin ‘yan jarida da kuma haƙƙin ɗan Adam.

 

A cikin wata sanarwa da ya raba wa manema labarai, Mataimaki na Musamman kan Harkokin Yaɗa Labarai ga Ministan, Rabi’u Ibrahim, ya ce Idris ya bayyana hakan ne a jawabin sa a Taro na Musamman na Ministocin Yaɗa Labarai na Ƙasashen Musulmi mai taken: “Bayar Da Labarin Ƙarya Da Kuma Kisan ‘Yan Jarida Da Gwamnatin Isra’ila ke yi a Lokacin Mamayar da Isra’ila ta yi wa Falasɗinu,” wanda aka gudanar a ranar Asabar, 24 ga Fabrairu, 2024 a birnin Istanbul na ƙasar Turkiyya.

ADVERTISEMENT
  • Wani Sojan Amurka Ya Bankawa Kansa Wuta Don Nuna Goyon Bayansa Ga Falasdinawa
  • Gobara Ta Ƙone Gidan Ƙaramar Ministar Birnin Tarayya Abuja, Mariya Bunkure

Ministan, wanda ya samu wakilcin Shugaban Ofishin Jakadancin Nijeriya a ƙasar Turkiyya, Ambasada Zayyad Abdul-Salam, ya bayyana cewa tun farkon rikicin, ‘yan jarida na ta fuskantar matsantawa, tsoratarwa da tashin hankali, har ma da kisa saboda kawai suna gudanar da aikin su na sanar da jama’a da kiyaye ƙa’idojin gaskiya da adalci.

 

LABARAI MASU NASABA

Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato

Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027

Ya ce: “Daga ƙididdigar da Kwamitin Kare Haƙƙin ‘Yan Jarida na duniya (CPJ) ya bayar, an kashe ‘yan jarida da ma’aikatan kafafen watsa labarai kusan tamanin da takwas tun lokacin da aka fara yaƙin a ranar 7 ga Oktoba, 2023.

 

“A matsayin mu na Ministocin Yaɗa Labarai da ke wakiltar ƙasashe a Ƙungiyar Ƙasashen Musulunci, ya zama wajibi a gare mu da mu yi Allah-wadai da irin wannan ta’asa da tauye haƙƙin ‘yan jarida da ke gudanar da ayyukan su a Falasɗinu.

 

“Dole ne mu tsaya tsayin daka don goyon bayan abokan aikin mu na kafafen yaɗa labarai waɗanda suke sadaukar da rayukan su a kullum don bayar da rahoton rikici a Falasɗinu wacce aka mamaye da kuma ba da murya ga marasa murya.”

 

Idris, wanda ya buƙaci takwarorin sa a ko da yaushe da su dage kan ganin an tabbatar da gaskiya a kowane lokaci ta hanyar neman yanayi mai kyau don bai wa ‘yan jarida damar gudanar da ayyukan su, ya yi tir da duk wani yunƙuri na karkatar da gaskiya tare da rashin bayyana haƙiƙanin halin da mutane ke ciki a Falasɗinu.

 

Ya shawarci ministocin da ke halartar taron da su binciko dabarun sadarwa, goyon baya, da haɗin gwiwa don faɗaɗa muryar ‘yan jarida waɗanda ke da ƙarfin halin tattara bayanan take haƙƙin bil’adama da cin zarafi da ake yi wa al’ummar Falasɗinu.

 

Ya ce: “Babban martanin mu dole ne ya kasance sadaukarwa don kiyaye ƙa’idojin ‘yancin ‘yan jarida, ‘yancin faɗin albarkacin baki, da ‘yancin samun bayanai. Waɗannan muhimman haƙƙoƙin ɗan’adam waɗanda ke cikin dokokin ƙasa da ƙasa sun zama ginshiƙan dimokiraɗiyya da kyakkyawan shugabanci.

 

“Ba za mu ƙyale waɗanda ke neman su murƙushe saɓanin ra’ayi su tattake su kuma su sarrafa labarin ba.”

 

Ministan ya yi kira da a tsagaita buɗe wuta cikin gaggawa a Gaza kuma ya jaddada matsayin Nijeriya kan samar da ƙasashe biyu don magance rikicin Falasɗinu, da tabbatar da an mutunta haƙƙi da ‘yancin al’ummar Falasɗinu da Isra’ila.

Gaza
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sin Tana Matsayi Na Farko A Duniya A Fannin Kirkire-kirkiren Wutar Lantarki
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kunnen Doki Da Nijeriya A Gasar Kwallon Kafa Tsakanin Kasashe 4 Ta ‘Yan Kasa Da 17
  • Sulaiman
    Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Fitar Da Sanarwa Game Da Cika Shekaru 10 Da Fitar Da Hukuncin Takkadamar “Philippines Da China”
  • Sulaiman
    Mataimakin Firaministan Sin Ya Jadadda Bukatar Kare Rayuka Da Dukiyoyin Jama’a Yayin Rangadi A Beijing

MASU ALAKA

Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato
Manyan Labarai

Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato

July 12, 2026
Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027
Manyan Labarai

Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027

July 12, 2026
Atiku Ya Soki Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC Da NECO Zuwa N50,000
Labarai

Atiku Ya Soki Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC Da NECO Zuwa N50,000

July 12, 2026
Next Post
Manzon Musamman Na Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Jana’izar Marigayi Shugaba Kasar Namibia Hage Geingob

Manzon Musamman Na Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Jana'izar Marigayi Shugaba Kasar Namibia Hage Geingob

LABARAI MASU NASABA

Sin Tana Matsayi Na Farko A Duniya A Fannin Kirkire-kirkiren Wutar Lantarki

Sin Tana Matsayi Na Farko A Duniya A Fannin Kirkire-kirkiren Wutar Lantarki

July 12, 2026
Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato

Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato

July 12, 2026
Sin Ta Yi Kunnen Doki Da Nijeriya A Gasar Kwallon Kafa Tsakanin Kasashe 4 Ta ‘Yan Kasa Da 17

Sin Ta Yi Kunnen Doki Da Nijeriya A Gasar Kwallon Kafa Tsakanin Kasashe 4 Ta ‘Yan Kasa Da 17

July 12, 2026
FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

July 12, 2026
Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027

Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027

July 12, 2026
Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Fitar Da Sanarwa Game Da Cika Shekaru 10 Da Fitar Da Hukuncin Takkadamar “Philippines Da China”

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Fitar Da Sanarwa Game Da Cika Shekaru 10 Da Fitar Da Hukuncin Takkadamar “Philippines Da China”

July 12, 2026
Atiku Ya Soki Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC Da NECO Zuwa N50,000

Atiku Ya Soki Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC Da NECO Zuwa N50,000

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Daraktan Hollywood Carl Rinsch Zai Shafe Watanni 30 A Gidan Gyaran Hali

July 12, 2026
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jadadda Bukatar Kare Rayuka Da Dukiyoyin Jama’a Yayin Rangadi A Beijing

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jadadda Bukatar Kare Rayuka Da Dukiyoyin Jama’a Yayin Rangadi A Beijing

July 12, 2026
Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya

Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya

July 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.