• English
  • Business News
Monday, September 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Ta Yi Nasara A Kotun Ingila Kan Rikicinta Da Kamfanin P&ID

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Nijeriya Ta Yi Nasara A Kotun Ingila Kan Rikicinta Da Kamfanin P&ID
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Nijeriya ta yi gagarumar nasara a kotun Ingila wajen sa kotun ta jingine umarnin biyan wani kamfanin kasashen ketare diyyar dala biliyan 11 saboda soke kwangilar da aka ba shi na samar da iskar gas. 

A shekarar 2010 gwamnatin Nijeriya ta bai wa kamfanin P&ID kwangilar shekaru 20 na ginawa tare da sarrafa iskar gas a sansaninsa da ke kudancin kasar nan, a yunkurin ganin an samu cin gajiyar arzikin makamashin da ake da shi.

  • Nijeriya Ta Yi Nasara A Kotun Ingila Kan Rikicinta Da Kamfanin P&ID
  • Kwastam Za Ta Rungumi Aiki Da Fasahar Zamani Domin Habaka Harkokinta – Adeniyi

Daga bisani, Nijeriya ta nuna rashin gamsuwarta da aikin kamfanin abin da ya sa ta sanar da soke kwangilar, kuma nan take kamfanin ya ruga kotu a Landan a 2017 domin neman a bi masa hakkinsa.

Kotun da ke birnin Landan ta bada umarnin cewar Nijeriya ta biya kamfanin P&ID dala biliyan shida da miliyan 600 a matsayin asarar da ya yi na ribar aikin, yayin kudin ruwan da ya yi ta karuwa kuma ya sa adadin kudin da za a biya kamfanin ya tashi zuwa sama da dala biliyan 11, kudin da ya zarce kasafin kudin Nijeriya na bangaren kula da lafiyar jama’a na shekarar 2019.

Sai dai lauyoyin Nijeriya sun ce ba a yi wa kasar nan adalci ba wajen wancan hukunci, saboda abin da suka kira bata sunan da kamfanin P&ID ya yi da kuma makudan kudaden da ya bayar a matsayin cin hanci ga wasu manyan jami’an gwamnati domin samun kwangilar tare da bai wa lauyoyin gwamnati cin hanci domin karbar wasu muhimman takardu domin gabatarwa kotun.

Labarai Masu Nasaba

Majalisar Dokokin Kano Ta Amince Da Ƙarin Kasafin Naira Biliyan 215.3 A Na 2025

Tinubu Ya Yi Adalci Ga Dukkan Yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

Shi dai P&ID ya musanta cewar ya samu kwangilar ce ta hanyar bada cin hanci da kuma musanta bai wa lauyoyin Nijeriya cin hanci domin samun takardun bayanai, inda ya zargi hukumomin kasar da rashin iya aiki a matsayin abin da ya haifar da matsalar da aka soke kwangilar da aka ba shi.

Alkalin kotun, Robin Knowles ya jingine hukuncin biyan kamfanin P&ID diyyar dala biliyan 11 tare da bai wa Nijeriya damar kalubalantar hukuncin da aka yi a baya lokacin gabatar da na shi hukuncin a ranar Litinin, yayin da ya tabbatar da cewar an samar da wannan kwangilar da ake takaddama a kai ne ta haramcaciyar hanyar da ta sabawa manufofin jama’a.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KamfaniKotuKwangilaLandanNijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Wani Saurayi Da Budurwa Suka Daura Wa Kansu Aure A Jigawa

Next Post

Jikar Dantata Ta Rasu Tana Da Shekaru 40 A Duniya

Related

Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure
Manyan Labarai

Majalisar Dokokin Kano Ta Amince Da Ƙarin Kasafin Naira Biliyan 215.3 A Na 2025

1 hour ago
Tinubu Ya Yi Adalci Ga Dukkan Yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Manyan Labarai

Tinubu Ya Yi Adalci Ga Dukkan Yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

5 hours ago
Gwamnan Neja Ya Kori Kwamishinoninsa Gaba ÆŠaya
Manyan Labarai

Gwamnan Neja Ya Kori Kwamishinoninsa Gaba ÆŠaya

9 hours ago
Rashin Amincewa Da Tsarin Ƴan Kudancin Kaduna Ya Sa Suka Yi Min Mummunar Fassara – El-Rufai
Manyan Labarai

Rashin Amincewa Da Tsarin Ƴan Kudancin Kaduna Ya Sa Suka Yi Min Mummunar Fassara – El-Rufai

13 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Shiri Da Ƴan Bindiga, Tana Ba Su Biliyoyi — El-Rufai
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Shiri Da Ƴan Bindiga, Tana Ba Su Biliyoyi — El-Rufai

14 hours ago
An Lalata Tamfatsetsiyar Gonar Wiwi A Taraba Tare Da Kama Dan Shekaru 70 A Anambra 
Manyan Labarai

An Lalata Tamfatsetsiyar Gonar Wiwi A Taraba Tare Da Kama Dan Shekaru 70 A Anambra 

1 day ago
Next Post
Jikar Dantata Ta Rasu Tana Da Shekaru 40 A Duniya

Jikar Dantata Ta Rasu Tana Da Shekaru 40 A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Tottenham Ta Dauki Aron Kolo Muani Daga PSG

Tottenham Ta Dauki Aron Kolo Muani Daga PSG

September 1, 2025
AU: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Bunkasa Noma Na Da Matukar Muhimmanci

AU: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Bunkasa Noma Na Da Matukar Muhimmanci

September 1, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure

Majalisar Dokokin Kano Ta Amince Da Ƙarin Kasafin Naira Biliyan 215.3 A Na 2025

September 1, 2025
Shugaban Zimbabwe Ya Sauka Beijing Domin Halartar Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan

Shugaban Zimbabwe Ya Sauka Beijing Domin Halartar Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan

September 1, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda, Sun Ceto Mata Da Yara A Zamfara

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda, Sun Ceto Mata Da Yara A Zamfara

September 1, 2025
Xi Ya Gabatar Da Jawabin Bude Taron Majalisar Shugabannin Kasashe Membobin Kungiyar SCO

Xi Ya Gabatar Da Jawabin Bude Taron Majalisar Shugabannin Kasashe Membobin Kungiyar SCO

September 1, 2025
NAPTIP Da Hisbah Sun Ceto Mata 12 Da Aka Yi Safararsu A Kano Zuwa Saudiyya

NAPTIP Da Hisbah Sun Ceto Mata 12 Da Aka Yi Safararsu A Kano Zuwa Saudiyya

September 1, 2025
Antonio Guterres: Xi Jinping Shugaban Kasa Ne Mai Sanin Ya Kamata

Antonio Guterres: Xi Jinping Shugaban Kasa Ne Mai Sanin Ya Kamata

September 1, 2025
Tinubu Ya Yi Adalci Ga Dukkan Yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

Tinubu Ya Yi Adalci Ga Dukkan Yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

September 1, 2025
Firaministan Kasar Pakistan: Xi Jinping Shugaban Kasa Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Kasar Pakistan: Xi Jinping Shugaban Kasa Ne Mai Hangen Nesa

September 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.