• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Ta Yi Nasara A Kotun Ingila Kan Rikicinta Da Kamfanin P&ID

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Nijeriya Ta Yi Nasara A Kotun Ingila Kan Rikicinta Da Kamfanin P&ID
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Nijeriya ta yi gagarumar nasara a kotun Ingila wajen sa kotun ta jingine umarnin biyan wani kamfanin kasashen ketare diyyar dala biliyan 11 saboda soke kwangilar da aka ba shi na samar da iskar gas. 

A shekarar 2010 gwamnatin Nijeriya ta bai wa kamfanin P&ID kwangilar shekaru 20 na ginawa tare da sarrafa iskar gas a sansaninsa da ke kudancin kasar nan, a yunkurin ganin an samu cin gajiyar arzikin makamashin da ake da shi.

  • Nijeriya Ta Yi Nasara A Kotun Ingila Kan Rikicinta Da Kamfanin P&ID
  • Kwastam Za Ta Rungumi Aiki Da Fasahar Zamani Domin Habaka Harkokinta – Adeniyi

Daga bisani, Nijeriya ta nuna rashin gamsuwarta da aikin kamfanin abin da ya sa ta sanar da soke kwangilar, kuma nan take kamfanin ya ruga kotu a Landan a 2017 domin neman a bi masa hakkinsa.

Kotun da ke birnin Landan ta bada umarnin cewar Nijeriya ta biya kamfanin P&ID dala biliyan shida da miliyan 600 a matsayin asarar da ya yi na ribar aikin, yayin kudin ruwan da ya yi ta karuwa kuma ya sa adadin kudin da za a biya kamfanin ya tashi zuwa sama da dala biliyan 11, kudin da ya zarce kasafin kudin Nijeriya na bangaren kula da lafiyar jama’a na shekarar 2019.

Sai dai lauyoyin Nijeriya sun ce ba a yi wa kasar nan adalci ba wajen wancan hukunci, saboda abin da suka kira bata sunan da kamfanin P&ID ya yi da kuma makudan kudaden da ya bayar a matsayin cin hanci ga wasu manyan jami’an gwamnati domin samun kwangilar tare da bai wa lauyoyin gwamnati cin hanci domin karbar wasu muhimman takardu domin gabatarwa kotun.

Labarai Masu Nasaba

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

Shi dai P&ID ya musanta cewar ya samu kwangilar ce ta hanyar bada cin hanci da kuma musanta bai wa lauyoyin Nijeriya cin hanci domin samun takardun bayanai, inda ya zargi hukumomin kasar da rashin iya aiki a matsayin abin da ya haifar da matsalar da aka soke kwangilar da aka ba shi.

Alkalin kotun, Robin Knowles ya jingine hukuncin biyan kamfanin P&ID diyyar dala biliyan 11 tare da bai wa Nijeriya damar kalubalantar hukuncin da aka yi a baya lokacin gabatar da na shi hukuncin a ranar Litinin, yayin da ya tabbatar da cewar an samar da wannan kwangilar da ake takaddama a kai ne ta haramcaciyar hanyar da ta sabawa manufofin jama’a.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KamfaniKotuKwangilaLandanNijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Wani Saurayi Da Budurwa Suka Daura Wa Kansu Aure A Jigawa

Next Post

Jikar Dantata Ta Rasu Tana Da Shekaru 40 A Duniya

Related

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

15 hours ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

1 day ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

1 day ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

1 day ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

2 days ago
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 
Manyan Labarai

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

2 days ago
Next Post
Jikar Dantata Ta Rasu Tana Da Shekaru 40 A Duniya

Jikar Dantata Ta Rasu Tana Da Shekaru 40 A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.