• English
  • Business News
Saturday, August 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Za Ta Bunkasa Noman Rogo Zuwa Tan Miliyan 120

by Abubakar Abba
1 year ago
in Noma Da Kiwo
0
Nijeriya Za Ta Bunkasa Noman Rogo Zuwa Tan Miliyan 120
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya ta bayyana shirinta na kara bunkasa noman Rogo domin samar wa masana’antu da kuma fitarwa zuwa waje.

Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche Nnaji ne ya bayyana haka a lokacin da ya kai ziyarar gani da ido a cibiyar gwamnatin tarayya da ke  gudanar da bincike kan masana’antu (FIIRO) da ke garin  Oshodi a Jihar Legas.

  • Mun Gano Famfo 5,570 Da Ake Amfani Da Su Wajen Satar Danyen Mai — NNPCL
  • Uwargidan Shugaban Kasa Ta Bude Makaranta Ga Matan Da Aka Kora A  Manyan Makarantu A Bauchi

Darakta Janar ta cibiyar, Jummai Tutuwa ce ta zagaya da ministan cikin sassan cibiyar baki-daya, don gane wa idonsa.

Har ila yau, bayan kammala ziyarar, ministan ya kuma koka a kan rashin kula da injinan sarrafa rogon da ke cikin hukumar.

Sannan ya sanar da cewa, idan har ana bai wa injinan sarrafa Rogon kulawar da ta dace, hakan zai taimaka wajen kara bunkasa noman Rogon tare da kara samar da ayyukan yi a fadin wannan kasa baki-daya.

Labarai Masu Nasaba

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji

“Muna da injinan sarrafa Rogo a wannan cibiya, wadanda za a iya amfani da su wajen kara habaka sarrafa Rogon, wanda hakan zai bai wa wannan kasa damar kara sarrafa shi daga tan miliyan 64 zuwa tan miliyan 120 a duk shekara”, a cewar Nnaji.

Kazalika ya kara da cewa, ma’aikatarsa za ta yi dukkanin mai yiwuwa; don ganin ta taimaka wa cibiyar domin amfana da kimiyyar zamani, wanda hakan zai ba ta damar karfafa sarrafa Rogo zuwa Fulawar da za a rinka fitar da ita zuwa kasashen ketare tare da kuma kara samar da wadataccen abinci a fadin Nijeriya baki-daya.

Haka zalika ministan ya bayyana cewa, “Nan ba da jimawa ba; za mu fara sarrafa abin da muke bukata a cikin wannan kasa ba tare da mun yi amfani amfani da Dalar Amurka,  don shigo da kaya daga kasashen waje ba”.

Ya kara da cewa, “Daya daga cikin abin da muka mayar da hankali a kai shi ne; fara yin shuka ta hanyar gwaji, domin samar da Rogon da dama tare da samar da ganyen Filanten, don sarrafa shi zuwa Takarda” .

A nata jawabin tun da farko, Darakta Janar ta cibiyar; Jummai Tutuwa, ta sheda wa ministan kokarin da cibiyar ta ke yi don tabbatar da sarrafa abinci tare da wadatuwarsa a fadin kasar nan, inda ta kara da cewa, cibiyar na da karfin samar da Tumatir da Rogon da za a sarrafa zuwa Biredi da kuma Filanten.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Matsayin Ci Gaban Rayuwar Jama’a Ta Kasar Sin Ta Kasance A Kan Gaba A Duniya

Next Post

Amurka Ta Dade Tana Yada Karairayi Game Da Kasar Sin 

Related

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya
Noma Da Kiwo

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

42 minutes ago
Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji
Noma Da Kiwo

Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji

1 day ago
Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje
Noma Da Kiwo

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

6 days ago
Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir
Noma Da Kiwo

Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir

1 week ago
Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona
Noma Da Kiwo

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

2 weeks ago
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

2 weeks ago
Next Post
Amurka Ta Dade Tana Yada Karairayi Game Da Kasar Sin 

Amurka Ta Dade Tana Yada Karairayi Game Da Kasar Sin 

LABARAI MASU NASABA

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

August 9, 2025
Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

August 9, 2025
Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

August 9, 2025
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

August 9, 2025
Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

August 9, 2025
Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

August 9, 2025
Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

August 9, 2025
Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

August 9, 2025
An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

August 9, 2025
Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.