• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Za Ta Bunkasa Noman Rogo Zuwa Tan Miliyan 120

by Abubakar Abba
1 year ago
in Noma Da Kiwo
0
Nijeriya Za Ta Bunkasa Noman Rogo Zuwa Tan Miliyan 120
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya ta bayyana shirinta na kara bunkasa noman Rogo domin samar wa masana’antu da kuma fitarwa zuwa waje.

Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche Nnaji ne ya bayyana haka a lokacin da ya kai ziyarar gani da ido a cibiyar gwamnatin tarayya da ke  gudanar da bincike kan masana’antu (FIIRO) da ke garin  Oshodi a Jihar Legas.

  • Mun Gano Famfo 5,570 Da Ake Amfani Da Su Wajen Satar Danyen Mai — NNPCL
  • Uwargidan Shugaban Kasa Ta Bude Makaranta Ga Matan Da Aka Kora A  Manyan Makarantu A Bauchi

Darakta Janar ta cibiyar, Jummai Tutuwa ce ta zagaya da ministan cikin sassan cibiyar baki-daya, don gane wa idonsa.

Har ila yau, bayan kammala ziyarar, ministan ya kuma koka a kan rashin kula da injinan sarrafa rogon da ke cikin hukumar.

Sannan ya sanar da cewa, idan har ana bai wa injinan sarrafa Rogon kulawar da ta dace, hakan zai taimaka wajen kara bunkasa noman Rogon tare da kara samar da ayyukan yi a fadin wannan kasa baki-daya.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

“Muna da injinan sarrafa Rogo a wannan cibiya, wadanda za a iya amfani da su wajen kara habaka sarrafa Rogon, wanda hakan zai bai wa wannan kasa damar kara sarrafa shi daga tan miliyan 64 zuwa tan miliyan 120 a duk shekara”, a cewar Nnaji.

Kazalika ya kara da cewa, ma’aikatarsa za ta yi dukkanin mai yiwuwa; don ganin ta taimaka wa cibiyar domin amfana da kimiyyar zamani, wanda hakan zai ba ta damar karfafa sarrafa Rogo zuwa Fulawar da za a rinka fitar da ita zuwa kasashen ketare tare da kuma kara samar da wadataccen abinci a fadin Nijeriya baki-daya.

Haka zalika ministan ya bayyana cewa, “Nan ba da jimawa ba; za mu fara sarrafa abin da muke bukata a cikin wannan kasa ba tare da mun yi amfani amfani da Dalar Amurka,  don shigo da kaya daga kasashen waje ba”.

Ya kara da cewa, “Daya daga cikin abin da muka mayar da hankali a kai shi ne; fara yin shuka ta hanyar gwaji, domin samar da Rogon da dama tare da samar da ganyen Filanten, don sarrafa shi zuwa Takarda” .

A nata jawabin tun da farko, Darakta Janar ta cibiyar; Jummai Tutuwa, ta sheda wa ministan kokarin da cibiyar ta ke yi don tabbatar da sarrafa abinci tare da wadatuwarsa a fadin kasar nan, inda ta kara da cewa, cibiyar na da karfin samar da Tumatir da Rogon da za a sarrafa zuwa Biredi da kuma Filanten.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Matsayin Ci Gaban Rayuwar Jama’a Ta Kasar Sin Ta Kasance A Kan Gaba A Duniya

Next Post

Amurka Ta Dade Tana Yada Karairayi Game Da Kasar Sin 

Related

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani
Noma Da Kiwo

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

6 days ago
Gwamnonin Arewa Na Kokarin Farfado Da Hadin Kan Yankin
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

6 days ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Nau’ikan Amfanin Gona Da Ke Saurin Girma Cikin ‘Yan Watanni

6 days ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Sama Wa Manoma Masu Renon Tsirrai Rancen Kudi

2 weeks ago
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi

2 weeks ago
Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

3 weeks ago
Next Post
Amurka Ta Dade Tana Yada Karairayi Game Da Kasar Sin 

Amurka Ta Dade Tana Yada Karairayi Game Da Kasar Sin 

LABARAI MASU NASABA

Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

June 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

June 6, 2025
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

June 6, 2025
Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.