• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Za Ta Bunkasa Noman Rogo Zuwa Tan Miliyan 120

by Abubakar Abba
1 year ago
in Noma Da Kiwo
0
Nijeriya Za Ta Bunkasa Noman Rogo Zuwa Tan Miliyan 120
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya ta bayyana shirinta na kara bunkasa noman Rogo domin samar wa masana’antu da kuma fitarwa zuwa waje.

Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche Nnaji ne ya bayyana haka a lokacin da ya kai ziyarar gani da ido a cibiyar gwamnatin tarayya da ke  gudanar da bincike kan masana’antu (FIIRO) da ke garin  Oshodi a Jihar Legas.

  • Mun Gano Famfo 5,570 Da Ake Amfani Da Su Wajen Satar Danyen Mai — NNPCL
  • Uwargidan Shugaban Kasa Ta Bude Makaranta Ga Matan Da Aka Kora A  Manyan Makarantu A Bauchi

Darakta Janar ta cibiyar, Jummai Tutuwa ce ta zagaya da ministan cikin sassan cibiyar baki-daya, don gane wa idonsa.

Har ila yau, bayan kammala ziyarar, ministan ya kuma koka a kan rashin kula da injinan sarrafa rogon da ke cikin hukumar.

Sannan ya sanar da cewa, idan har ana bai wa injinan sarrafa Rogon kulawar da ta dace, hakan zai taimaka wajen kara bunkasa noman Rogon tare da kara samar da ayyukan yi a fadin wannan kasa baki-daya.

Labarai Masu Nasaba

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma

“Muna da injinan sarrafa Rogo a wannan cibiya, wadanda za a iya amfani da su wajen kara habaka sarrafa Rogon, wanda hakan zai bai wa wannan kasa damar kara sarrafa shi daga tan miliyan 64 zuwa tan miliyan 120 a duk shekara”, a cewar Nnaji.

Kazalika ya kara da cewa, ma’aikatarsa za ta yi dukkanin mai yiwuwa; don ganin ta taimaka wa cibiyar domin amfana da kimiyyar zamani, wanda hakan zai ba ta damar karfafa sarrafa Rogo zuwa Fulawar da za a rinka fitar da ita zuwa kasashen ketare tare da kuma kara samar da wadataccen abinci a fadin Nijeriya baki-daya.

Haka zalika ministan ya bayyana cewa, “Nan ba da jimawa ba; za mu fara sarrafa abin da muke bukata a cikin wannan kasa ba tare da mun yi amfani amfani da Dalar Amurka,  don shigo da kaya daga kasashen waje ba”.

Ya kara da cewa, “Daya daga cikin abin da muka mayar da hankali a kai shi ne; fara yin shuka ta hanyar gwaji, domin samar da Rogon da dama tare da samar da ganyen Filanten, don sarrafa shi zuwa Takarda” .

A nata jawabin tun da farko, Darakta Janar ta cibiyar; Jummai Tutuwa, ta sheda wa ministan kokarin da cibiyar ta ke yi don tabbatar da sarrafa abinci tare da wadatuwarsa a fadin kasar nan, inda ta kara da cewa, cibiyar na da karfin samar da Tumatir da Rogon da za a sarrafa zuwa Biredi da kuma Filanten.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Matsayin Ci Gaban Rayuwar Jama’a Ta Kasar Sin Ta Kasance A Kan Gaba A Duniya

Next Post

Amurka Ta Dade Tana Yada Karairayi Game Da Kasar Sin 

Related

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Noma Da Kiwo

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

5 hours ago
Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma

6 days ago
Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja
Noma Da Kiwo

Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja

6 days ago
Sin Ta Gina Cibiyoyin Fasahar Aikin Gona Na Gwaji Guda 24 A Afirka
Noma Da Kiwo

Muhimman Dalilan Kirkiro Da Shirin Inganta Aikin Noma ‘SAPZ’

2 weeks ago
Dalilin Nijeriya Na Kulla Yarjejeniya Da Kasar Sin Kan Noman Rake
Noma Da Kiwo

Dalilin Nijeriya Na Kulla Yarjejeniya Da Kasar Sin Kan Noman Rake

2 weeks ago
Nazari Kan Amfanin Noman Kanumfari
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Amfanin Noman Kanumfari

2 weeks ago
Next Post
Amurka Ta Dade Tana Yada Karairayi Game Da Kasar Sin 

Amurka Ta Dade Tana Yada Karairayi Game Da Kasar Sin 

LABARAI MASU NASABA

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.