ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Za Ta Bunkasa Noman Rogo Zuwa Tan Miliyan 120

by Abubakar Abba
2 years ago
Rogo

Gwamnatin tarayya ta bayyana shirinta na kara bunkasa noman Rogo domin samar wa masana’antu da kuma fitarwa zuwa waje.

Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche Nnaji ne ya bayyana haka a lokacin da ya kai ziyarar gani da ido a cibiyar gwamnatin tarayya da ke  gudanar da bincike kan masana’antu (FIIRO) da ke garin  Oshodi a Jihar Legas.

  • Mun Gano Famfo 5,570 Da Ake Amfani Da Su Wajen Satar Danyen Mai — NNPCL
  • Uwargidan Shugaban Kasa Ta Bude Makaranta Ga Matan Da Aka Kora A  Manyan Makarantu A Bauchi

Darakta Janar ta cibiyar, Jummai Tutuwa ce ta zagaya da ministan cikin sassan cibiyar baki-daya, don gane wa idonsa.

ADVERTISEMENT

Har ila yau, bayan kammala ziyarar, ministan ya kuma koka a kan rashin kula da injinan sarrafa rogon da ke cikin hukumar.

Sannan ya sanar da cewa, idan har ana bai wa injinan sarrafa Rogon kulawar da ta dace, hakan zai taimaka wajen kara bunkasa noman Rogon tare da kara samar da ayyukan yi a fadin wannan kasa baki-daya.

LABARAI MASU NASABA

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Taki Kyauta Ga Manoma 20,160

“Muna da injinan sarrafa Rogo a wannan cibiya, wadanda za a iya amfani da su wajen kara habaka sarrafa Rogon, wanda hakan zai bai wa wannan kasa damar kara sarrafa shi daga tan miliyan 64 zuwa tan miliyan 120 a duk shekara”, a cewar Nnaji.

Kazalika ya kara da cewa, ma’aikatarsa za ta yi dukkanin mai yiwuwa; don ganin ta taimaka wa cibiyar domin amfana da kimiyyar zamani, wanda hakan zai ba ta damar karfafa sarrafa Rogo zuwa Fulawar da za a rinka fitar da ita zuwa kasashen ketare tare da kuma kara samar da wadataccen abinci a fadin Nijeriya baki-daya.

Haka zalika ministan ya bayyana cewa, “Nan ba da jimawa ba; za mu fara sarrafa abin da muke bukata a cikin wannan kasa ba tare da mun yi amfani amfani da Dalar Amurka,  don shigo da kaya daga kasashen waje ba”.

Ya kara da cewa, “Daya daga cikin abin da muka mayar da hankali a kai shi ne; fara yin shuka ta hanyar gwaji, domin samar da Rogon da dama tare da samar da ganyen Filanten, don sarrafa shi zuwa Takarda” .

A nata jawabin tun da farko, Darakta Janar ta cibiyar; Jummai Tutuwa, ta sheda wa ministan kokarin da cibiyar ta ke yi don tabbatar da sarrafa abinci tare da wadatuwarsa a fadin kasar nan, inda ta kara da cewa, cibiyar na da karfin samar da Tumatir da Rogon da za a sarrafa zuwa Biredi da kuma Filanten.

Rogo
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilan Da Suka Sa Fannin Kiwo Ke Fuskantar Kalubale A Nijeriya —Gwamnatin Tarayya

MASU ALAKA

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe
Noma Da Kiwo

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Taki Kyauta Ga Manoma 20,160
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Taki Kyauta Ga Manoma 20,160

June 12, 2026
Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT
Noma Da Kiwo

Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT

June 6, 2026
Next Post
Amurka Ta Dade Tana Yada Karairayi Game Da Kasar Sin 

Amurka Ta Dade Tana Yada Karairayi Game Da Kasar Sin 

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.