• English
  • Business News
Thursday, August 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Za Ta Fara Aiwatar Da Yarjejeniyoyin Haɗin Gwiwa Da Kafofin Watsa Labarai Na Sin – Ministan Yaɗa Labarai

by Sulaiman
5 months ago
in Labarai
0
Yajin aiki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Nijeriya za ta fara aiwatar da yarjejeniyoyin fahimtar juna guda biyu da aka rattaba wa hannu tsakanin Hukumar Watsa Labarai ta ƙasar Sin (China Media Group) da Hukumar Talabijin ta Nijeriya (NTA) da Hukumar Rediyon Tarayyar Nijeriya (FRCN) a Taron Haɗin Gwiwa tsakanin Sin da Afrika (FOCAC) wanda aka gudanar a birnin Beijing.

 

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya tabbatar da hakan yayin da ya karɓi jakadan Chana a Nijeriya, Mista Yu Dunhai, a wata ziyarar ban-girma da ya kai masa a ofishin sa ranar Alhamis.

  • Kasar Sin A Matsayin Katafariyar Cibiyar Kere-Keren Mutum-Mutumi A Duniya
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 92, Sun Kubutar Da Mutane 75 A Cikin Mako Guda – DHQ

Ya bayyana cewa yarjejeniyoyin za su ƙarfafa dangantaka tsakanin ƙasashen biyu ta fuskar kafofin watsa labarai da sadarwa.

 

Labarai Masu Nasaba

Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

Ya ce: “Nijeriya da Chana sun kai matakin haɗin gwiwa mafi girma a tarihin dangantakar su. Wannan ne ya sa aka rattaba hannu kan yarjejeniyoyi guda goma a taron FOCAC, kuma guda biyu daga cikin su suna da alaƙa da ma’aikatar nan.

 

“NTA ita ce babbar tashar talbijin a Afrika baki ɗaya, tana da tashoshi sama da ɗari a faɗin ƙasar nan, tana isar da shirye-shiryen ta ga sama da mutane miliyan 200.

 

“Hakan ya sa muke da buƙatar amfani da wannan haɗin gwiwa don musayar bayanai da fasaha, tare da amfana da juna.”

 

Ministan ya bayyana cewa yarjejeniyoyin sun haɗa da musayar bayanai, shirye-shirye, da fasaha domin inganta ayyukan gidajen watsa labarai na Nijeriya tare da ƙarfafa aikin jarida bisa kyawawan ƙa’idojin duniya.

 

Haka nan, ya jaddada buƙatar haɗin gwiwa da Chana domin yaƙi da labaran ƙarya da yaudara ta hanyar yaɗa bayanai marasa tushe.

 

Ya ce: “Labaran ƙarya da yaudara manyan barazana ne ga duniya. Mun san cewa ƙasar Chana tana da matuƙar damuwa game da wannan batu, haka nan kuma Nijeriya.

 

“Wannan ba matsala ce da ta shafi ƙasashen mu biyu kawai ba, matsala ce ta duniya baki ɗaya. Saboda haka, muna son yin aiki tare da ƙasar Chana domin yaƙi da labaran bogi da yaɗa ingantattun bayanai da za su amfani al’umma.”

 

Idris ya tabbatar wa jakaden na Chana cewa Nijeriya na kiyaye ‘yancin ‘yan jarida, wanda wani muhimmin ɓangare ne na jajircewar Shugaban Ƙasa Bola Tinubu wajen ƙarfafa dimokiraɗiyya.

 

Ya ce: “A Nijeriya, ‘yan jarida suna da ‘yancin aikin su. Duk da yake akwai matsaloli a wasu lokuta, muna aiki a kai a kai domin gyara su. Nijeriya tana da ‘yancin watsa labarai mai yawa, kuma muna son ci gaba da hakan.”

 

Har ila yau, ya buƙaci kamfanonin ƙasar Chana da su yi amfani da damar da manufofin Tinubu ke samarwa wajen zuba jari a Nijeriya.

 

A nasa jawabin, Jakada Yu Dunhai ya jaddada aniyar sa ta ƙara ƙarfafa alaƙa tsakanin Nijeriya da Chana, tare da yaba wa Ajandar Sabunta Fata ta Shugaba Ƙasa Tinubu.

 

Ya ce: “Ina da sa’a sosai kasancewa jakada a lokacin da Shugaban Ƙasa Tinubu yake aiwatar da Ajandar Sabunta Fata don ƙarfafa Nijeriya. Haka nan, a ƙasar Chana, Shugaba Xi Jinping yana jagorantar ƙasar zuwa cigaba ta hanyar sauye-sauyen zamani na ƙasar Chana.”

 

Jakaden ya bayyana cewa a taron FOCAC da ya gabata a Beijing, Shugabannin Nijeriya da Chana sun amince da ɗaukaka alaƙar ƙasashen zuwa matakin haɗin gwiwar dabarun cigaba.

 

Haka nan, ya nuna muhimmancin aiwatar da yarjejeniyoyin tsakanin NTA, FRCN, da China Media Group, yana mai cewa kafofin watsa labarai suna taka muhimmiyar rawa wajen gina al’umma.

 

Ya kuma yaba da yadda kafofin watsa labarai na Nijeriya ke gudanar da ayyukan su bisa gaskiya, daidaito, da riƙon amana.

 

A ɓangaren zuba jari, jakaden ya bayyana cewa Shugaba Xi Jinping ya ware dala biliyan 50 ($50bn) domin zuba jari a Afrika cikin shekaru uku masu zuwa a matsayin wani ɓangare na yarjejeniyoyin da aka cimma a taron FOCAC.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Gwamnatinsa Na Bai Wa Sojoji Haɗin Kai 

Next Post

Bukatar Kafa Dokar-ta-baci Kan Yaduwar Jabun Magunguna

Related

Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II
Manyan Labarai

Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II

21 minutes ago
Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025
Labarai

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

9 hours ago
Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna
Labarai

Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

9 hours ago
Tinubu
Labarai

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Bayar Da Kiwon Lafiya Kyauta Ga ‘Yan Fansho Masu Karamin Karfi 

10 hours ago
Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano
Labarai

Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano

11 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Labarai

“Ku Yi Murabus Idan Baza Ku Iya Rike Amanar Jama’a ba” – Gargadin Gwamna Abba Ga Kwamishinoninsa

12 hours ago
Next Post
Bukatar Kafa Dokar-ta-baci Kan Yaduwar Jabun Magunguna

Bukatar Kafa Dokar-ta-baci Kan Yaduwar Jabun Magunguna

LABARAI MASU NASABA

Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II

Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II

August 7, 2025
Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

August 6, 2025
Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

August 6, 2025
Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

August 6, 2025
Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

August 6, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Bayar Da Kiwon Lafiya Kyauta Ga ‘Yan Fansho Masu Karamin Karfi 

August 6, 2025
Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

August 6, 2025
Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano

Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano

August 6, 2025
Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

August 6, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

“Ku Yi Murabus Idan Baza Ku Iya Rike Amanar Jama’a ba” – Gargadin Gwamna Abba Ga Kwamishinoninsa

August 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.