• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Za Ta Fara Aiwatar Da Yarjejeniyoyin Haɗin Gwiwa Da Kafofin Watsa Labarai Na Sin – Ministan Yaɗa Labarai

by Sulaiman
7 months ago
in Labarai
0
Yajin aiki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Nijeriya za ta fara aiwatar da yarjejeniyoyin fahimtar juna guda biyu da aka rattaba wa hannu tsakanin Hukumar Watsa Labarai ta ƙasar Sin (China Media Group) da Hukumar Talabijin ta Nijeriya (NTA) da Hukumar Rediyon Tarayyar Nijeriya (FRCN) a Taron Haɗin Gwiwa tsakanin Sin da Afrika (FOCAC) wanda aka gudanar a birnin Beijing.

 

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya tabbatar da hakan yayin da ya karɓi jakadan Chana a Nijeriya, Mista Yu Dunhai, a wata ziyarar ban-girma da ya kai masa a ofishin sa ranar Alhamis.

  • Kasar Sin A Matsayin Katafariyar Cibiyar Kere-Keren Mutum-Mutumi A Duniya
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 92, Sun Kubutar Da Mutane 75 A Cikin Mako Guda – DHQ

Ya bayyana cewa yarjejeniyoyin za su ƙarfafa dangantaka tsakanin ƙasashen biyu ta fuskar kafofin watsa labarai da sadarwa.

 

Labarai Masu Nasaba

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

Ya ce: “Nijeriya da Chana sun kai matakin haɗin gwiwa mafi girma a tarihin dangantakar su. Wannan ne ya sa aka rattaba hannu kan yarjejeniyoyi guda goma a taron FOCAC, kuma guda biyu daga cikin su suna da alaƙa da ma’aikatar nan.

 

“NTA ita ce babbar tashar talbijin a Afrika baki ɗaya, tana da tashoshi sama da ɗari a faɗin ƙasar nan, tana isar da shirye-shiryen ta ga sama da mutane miliyan 200.

 

“Hakan ya sa muke da buƙatar amfani da wannan haɗin gwiwa don musayar bayanai da fasaha, tare da amfana da juna.”

 

Ministan ya bayyana cewa yarjejeniyoyin sun haɗa da musayar bayanai, shirye-shirye, da fasaha domin inganta ayyukan gidajen watsa labarai na Nijeriya tare da ƙarfafa aikin jarida bisa kyawawan ƙa’idojin duniya.

 

Haka nan, ya jaddada buƙatar haɗin gwiwa da Chana domin yaƙi da labaran ƙarya da yaudara ta hanyar yaɗa bayanai marasa tushe.

 

Ya ce: “Labaran ƙarya da yaudara manyan barazana ne ga duniya. Mun san cewa ƙasar Chana tana da matuƙar damuwa game da wannan batu, haka nan kuma Nijeriya.

 

“Wannan ba matsala ce da ta shafi ƙasashen mu biyu kawai ba, matsala ce ta duniya baki ɗaya. Saboda haka, muna son yin aiki tare da ƙasar Chana domin yaƙi da labaran bogi da yaɗa ingantattun bayanai da za su amfani al’umma.”

 

Idris ya tabbatar wa jakaden na Chana cewa Nijeriya na kiyaye ‘yancin ‘yan jarida, wanda wani muhimmin ɓangare ne na jajircewar Shugaban Ƙasa Bola Tinubu wajen ƙarfafa dimokiraɗiyya.

 

Ya ce: “A Nijeriya, ‘yan jarida suna da ‘yancin aikin su. Duk da yake akwai matsaloli a wasu lokuta, muna aiki a kai a kai domin gyara su. Nijeriya tana da ‘yancin watsa labarai mai yawa, kuma muna son ci gaba da hakan.”

 

Har ila yau, ya buƙaci kamfanonin ƙasar Chana da su yi amfani da damar da manufofin Tinubu ke samarwa wajen zuba jari a Nijeriya.

 

A nasa jawabin, Jakada Yu Dunhai ya jaddada aniyar sa ta ƙara ƙarfafa alaƙa tsakanin Nijeriya da Chana, tare da yaba wa Ajandar Sabunta Fata ta Shugaba Ƙasa Tinubu.

 

Ya ce: “Ina da sa’a sosai kasancewa jakada a lokacin da Shugaban Ƙasa Tinubu yake aiwatar da Ajandar Sabunta Fata don ƙarfafa Nijeriya. Haka nan, a ƙasar Chana, Shugaba Xi Jinping yana jagorantar ƙasar zuwa cigaba ta hanyar sauye-sauyen zamani na ƙasar Chana.”

 

Jakaden ya bayyana cewa a taron FOCAC da ya gabata a Beijing, Shugabannin Nijeriya da Chana sun amince da ɗaukaka alaƙar ƙasashen zuwa matakin haɗin gwiwar dabarun cigaba.

 

Haka nan, ya nuna muhimmancin aiwatar da yarjejeniyoyin tsakanin NTA, FRCN, da China Media Group, yana mai cewa kafofin watsa labarai suna taka muhimmiyar rawa wajen gina al’umma.

 

Ya kuma yaba da yadda kafofin watsa labarai na Nijeriya ke gudanar da ayyukan su bisa gaskiya, daidaito, da riƙon amana.

 

A ɓangaren zuba jari, jakaden ya bayyana cewa Shugaba Xi Jinping ya ware dala biliyan 50 ($50bn) domin zuba jari a Afrika cikin shekaru uku masu zuwa a matsayin wani ɓangare na yarjejeniyoyin da aka cimma a taron FOCAC.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Gwamnatinsa Na Bai Wa Sojoji Haɗin Kai 

Next Post

Bukatar Kafa Dokar-ta-baci Kan Yaduwar Jabun Magunguna

Related

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita
Labarai

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

7 hours ago
NNPP
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

9 hours ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

11 hours ago
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

11 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Labarai

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

14 hours ago
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye
Labarai

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

16 hours ago
Next Post
Bukatar Kafa Dokar-ta-baci Kan Yaduwar Jabun Magunguna

Bukatar Kafa Dokar-ta-baci Kan Yaduwar Jabun Magunguna

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.