ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Kafa Dokar-ta-baci Kan Yaduwar Jabun Magunguna

by Leadership Hausa
1 year ago
Jabun

A kwanan baya ne Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta kasa NAFDAC, ta rinka kai samame ba kakkautawa, a manyan kasuwannin da ke a daukacin fadin kasar nan, wanda hakan a zahirance, ya tona asirin irin hatsarin da Nijeriya ke ciki na masu hada-hadar jabun magunguna.

Hukumar a yayin samamen nata, ta bankado yadda ake hada-hadar sayar da jabun magunguna wadanda kuma suka lalace a kasuwar Aba a Onitsha da kuma ta Idumota da ke a jihar Legas, wadanda kudinsu ya kai na biliyoyin Naira.

  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 92, Sun Kubutar Da Mutane 75 A Cikin Mako Guda – DHQ
  • Yadda Fadada Bude Kofar Kasar Sin Ke Haifar Da Damammaki Ga Duniya

Baya ga irin wannan bakar hada-hadar ta jabun magungunan = da irin wadannan mugayen mutanen keyi a wadannan kasuwannin, bankado wadannan gurbatattun magungunan na bliyoyin Naira a wadannan kasuwannin ya nuna karara yadda tsarin kiwon lafiyar na kasar nan yake tafiya a kan tarkon mutuwa.

ADVERTISEMENT

A nan ya zama wajbi, mu jinjinawa kokarin na Hukumar NAFDAC ke yi, na jajircewar bankado wadannan kasuwanin, amma duk da haka za a iya cewa, Hukumar ta dan gaza duba da cewa, tana gudanar da irin wannan samamen ne, kawai daga wani lokaci zuwa wani lokaci.

A ra’ayin wannan jaridar, wannan binciken na Hukumar a kasuwannin ba komai bane, tamkar na tayar da hankalin ‘yan Nijeriya, duba da irin tulin jabun magungunan da hukumar ta bakado a kasuwannin.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

A kasuwar Ariaria da ke Aba, NAFDAC, sun gano jabun magunguna da kudinsu ya kai na miliyoyin Naira.

Bugu da kari, a kasuwar Idumota da ke a jihar Legas, NAFDAC sun garkame Shanguna sama da 3,000 bayan sun gano Shagunan shake da jabun magunguna.

A kasuwar kan Gadar Onitsha, nan ma Hukumar ta sun kama manyan motoci goma shake da jabun magungana, inda a bayan kamen dilolin magungunan suka yi yunkurin bai wa jami’an na NAFDAC cin hancin Naira miliyan 135.

Har ila yau, a kasurgumar kasuwar Cemetery da ke Aba, nan ma NAFDAC ta kama tare da kwace jabun magunguna da kudinsu ya kai na sama da Naira miliyan biyar.

Bisa batun gaskiya, irin wannan bakar hada-hadar jabun magunguna, ya wuce maganar alkaluma, domin kuwa, abinda yafi dacewa, shi ne, yankewa irin masu wannan bakar harkalar hukuncin ta hanyar rataye su, duba da yaddda suka kara jefa rayuwar marasa lafiya a cikin wata ukuba ta hanyar sayar da jabun magunguna.

Abinda ya kara jefa fargaba a zukakan jama’a ne, shi ne, kan irin hanyoyin da irin wadannan bata garin ke bi wajen sarrafa jabun magungunan, musamman ganin yadda suke da kayan aikin da suke sake sarrafa magungunan da suka riga suka lalace.

Kazalika, a wani gwaji da NAFDAC kan mangunan yara, da wadannan bata garin ke sarrafawa suke kuma sayar da shi, kan farashi mai sauki, NAFDAC bata iya gano wani abu da ba daidai ba.

Wannan rashin iya ganowar na NAFDAC ya nuna yadda sarrafa magungunan na jabu, sun jima suna yin sanadiyar mutuwar yara, ba tare da yin amfani da bakin Bindiga ba.

Wannan matsalar dai, ba wai kawai ta tsaya kan daidaikun ‘yan kasuwa masu sarrafa jabun magungunan bane, domin abu ne, da ya karade daukacin miyagun masana’tun da ke da ke sarrafa jabun, inda suka fakewa a matsayin Shaguna suna cikin Karensu babu babbaka ciki har da sarrafa jabun magunguna na yakar cuta mai karya garkuwar jiki.

A yayin samamane na NAFDAC, sama da haramtattun masana’antu 240 da ake sarrafa jabun magunguna aka bankado a kasuwar Cemetery.

A ra’ayin mu wadannan matakan da aka dauka na kai samame a kasuwannin bai isa ba, duba da cewa, hukuncin shigo da kwayar maganin Tramadol zuwa cikin kasar nan ta haramtacciyar hanya, shi ne, kodai yin shekaru biyar a gidan gyran hali ko kuma biyan tararar Naira 250,000, domin kuwa dole mu mayar da hankali wajen kare kiwon lafiyar yan kasar nan.

Mojisola Adeyeye, Darakta Janar ta kasa ta Hukumar NAFDAC, ta bukaci da a rinka yanke hukuncin kisa ga masu sarrafa jabun magunguna, duba da yadda suke jefa rayuwar alumma a cikin matsala da kuma jefa tsarin kiwon lafiya a cikin barazana.

Yawan samun irin wadannan kasuwannin na sarrafa jabun magungunnan duk da kokarin da NAFDAC ke kan yin a rage sarrafa jabun magungunan akalla zuwa kaso biyar a cikin dari a 2025, hakan na ci gaba da zama wani babban kalubale ga hukumar, musamman duba da yadda ake ci gaba da samun karuwar a kasar.

Wani abin bakin ciki shi ne, yadda halastatun kungiyoyin dilolin sarrafa magunguna kamar irin su, EKUMI Plaza Patent Medicine, suma suka bi sahu wajen shiga kazamar hanyar ta hada-hadar kasuwancin jabun magunguna da suka kai na Naira miliyan 50.

Karafafa yakar wannan lamarin bai wadatar ba, domin kuwa kamata ya yi a yiwa fannin rabar da magunna na kasar nan garanbawul baki daya.

Ci gaba da samun wanzuwar irin wadannan kasuwannin na sayar da jabun magunguna na kara haifar da gibi a bangaren tsarin kiwon lafiyar kasar.

Ya zama wajbi Gwamnatin Tarayya ta sake yin nazari kan bayar da takardun fito na shigo da magunguna cikin kasar, musamman domin a tallafawa halastattun masana’atun cikin gida da ke sarrafa magungunan.

Ya kuma kamata a kara karfafa shirin Inshorar kiwon lafiya na kasa NHIS, wanda hakan zai taimaka a rinka samar da ingantatun magunguna kuma a cikin farashi mai sauki, wanda hakan kuma zai sanya, durkushewar bakar kasuwar ta sayar da jabun magunnan a kasar.

Kazalika, akwai bukatar a rinka ilimantar da alummar gari kan illar irin wadannan jabun magungunan.

Bai kamata bangaren Shari’a ya rinka yin hukunci mai sauki ga masu wannan dabi’ar ba, musamman duba da yadda kawai irin masu wannan dabi’ar da suka shiga hannun hukuma ake cin su tara ‘yar kadan.

Dole kutuna sun tilatsa tsauraran hukunci, ciki har da yanke hukunci zaman gidan Yari da kuma yanke hukuncin haramtawa wadanda aka kama suna sarrafa jabun magunguna kara yin duk wata sana’a da ta shafi sarrafa magunguna.

Yawon da irin wadannna jabun magungunan a cikin alumma, tamkar yankewa iyalai hukuncin kisa ne.

Bugu da kari, ya zama wajbi daukacin ‘yan Nijeriya su tashi tsaye mu yi aiki tukuro domin kawo karshen wannan bakar dabi’ar, mu kuma jajirce har sai mun ga an a sayar da ingantatun magunguna a kasar.

Jabun
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Karin Kudin Lantarki Da Na Kira: Kungiyar Kwadago Ta Yi Barazanar Shirya Zanga-zanga A Fadin Nijeriya

Karin Kudin Lantarki Da Na Kira: Kungiyar Kwadago Ta Yi Barazanar Shirya Zanga-zanga A Fadin Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.