ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Gwamnatinsa Na Bai Wa Sojoji Haɗin Kai 

by Hussein Yero and Sulaiman
1 year ago
Gwamna Lawal

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya jaddada aniyar gwamnatinsa na ƙara haɗa kai da sojojin da ke aiki a jihar.

A ranar Alhamis ne gwamnan ya karɓi baƙuncin Babban Hafsan Sojin Sama Air Marshal Hassan Bala Abubakar a ziyarar aiki da ya kai jihar Zamfara.

  • Nazarin CGTN: Manufar Sanya Muradun Amurka Gaba Da Komai Na Lalata Dangantakar Dake Tsakaninta Da Turai
  • Yadda Ake Ayyukan Gina Ababen More Rayuwa A Jihar Zamfara 

Babban Hafsan sojin saman ya ziyarci Zamfara ne dangane da harin kuskure da aka kai wanda ya yi sanadin mutuwar fararen hula 11 a kusa da Gidan Makera a Ƙaramar Hukumar Zurmi a ranar 11 ga watan Janairun 2025.

ADVERTISEMENT

Fararen hular da suka rasa rayukansu ‘yan sintiri na yankin ne waɗanda aka yi kuskure ana zaton cewa ‘yan bindiga ne suka tsere daga farmakin da rundunar sojin sama ta Operation Fansar Yamma ta kai.

A nasa jawabin, Gwamna Dauda Lawal ya yaba da yadda rundunar sojin saman ta ɗauki matakin gaggawa kan kiraye-kirayen da ake yi a yankunan da ke fama da rikici a faɗin jihar Zamfara.

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

Gwamna Lawal

“Ina son in nuna jin daɗina ga Babban Hafsan Sojin Sama, wanda kafin ziyarar tasa a yau, ya aiko da wata tawaga mai ƙarfi ƙarƙashin jagorancin ɗaya daga cikin manyan hafsoshi daga hedikwatar domin jajanta mana da al’ummar Zamfara. Ya aika da tawaga zuwa Zamfara a lokuta biyu daban-daban.

“Ina son nanata cewa a lokacin da lamarin ya faru, mun yi magana da manema labarai, inda muka fayyace cewa ba da gangan ba ne, illa hatsari ne. Kasancewar Hafsan Sojin Sama a Zamfara na nuna ƙwarewa da kulawa ta musamman.

Gwamnan ya bayyana cewa rundunar sojin saman Nijeriya na da matuƙar muhimmanci wajen yaƙar ‘yan bindiga a Zamfara, Arewa maso Yamma, da ma kasa baki ɗaya. “Ina godiya da babban hafsan sojin sama bisa gudunmawar da rundunar ta bayar. Suna amsa kiran gaggawa a duk lokacin da muka buƙata.

“Mun fito ƙarara game da matsayinmu. Mun sanar da duk mai saurare cewa ba mu shirya ba kuma ba za mu taba yin sulhu da ‘yan bindiga ba. Kowa na iya tabbatar da cewa matsayinmu yana samun sakamako, domin mun fara ganin sakamako mai kyau, sannu a hankali zaman lafiya ya dawo Zamfara.

“Ina so in yi amfani da wannan damar in sanar da Air Marshal cewa muna gina filin jirgin sama a Zamfara. Ina roƙon cewa da zarar an kammala filin jirgin, muna son hangar sojojin sama don tabbatar da kowa ya tafi daidai a jihar.

Gwamna Lawal

“Za mu ci gaba da tuntubar ku saboda muna buƙatar sojojin sama. Ba za mu iya gode maka a a kan wannan ziyarar ba. A gare mu a Zamfara, mun jinjina wa wannan tattaki da ku ka yi tun daga Abuja. Daga bangarenmu, ina tabbatar muku cewa za mu ci gaba da yin cudanya da ku, kuma za mu yi duk mai yiwuwa don tallafa wa sojojin da ke yaƙi da ’yan bindiga. Ina yi muku fatan sauka lafiya a Abuja.”

A farko, Babban Hafsan Sojin sama Air Marshal Hassan Bala Abubakar, ya miƙa godiyarsa ga gwamna Dauda Lawal bisa haɗin kan da ya bayar wajen faɗakar da al’umma kan harin da aka kai bisa kuskure a Zamfara.

“Idan za ku iya tunawa a ranar 11 ga watan Junairu, 2025, an kai hare-hare ta sama a Zamfara sakamakon rahoton sirri na ‘yan bindiga a Gidan Makera a ƙaramar hukumar Maradun. An kai harin ne da nufin fatattakar ‘yan ta’addan da ke da alaƙa da ɗan fashin daji Bello Turji. Kwanaki kaɗan bayan harin, wani rahoto ya yi ikirarin cewa jirgin ya kai harin ne kan wasu ‘yan ƙungiyar ‘yan sintiri bisa kuskure.

“Saboda damuwa da wannan zargi, nan da nan na kafa kwamitin bincike kan harin. Tuni dai kwamitin binciken ya gabatar da rahotonsa da sakamakon binciken, wanda ya tabbatar da cewa an kashe ‘yan sintiri 11 ba da gangan ba.

“Ziyarar mu ta safiyar yau mun yi ta ne don jajanta wa iyalan waɗanda abin ya shafa, da kuma al’ummar Zamfara bisa wannan mummunan lamari.”

Gwamnan da hafsan sojin sama sun yi wata ganawar sirri da iyalan waɗanda harin jirgin ya rutsa da su, tare da wasu 11 da suka jikkata.

Gwamna Lawal
Hussein Yero
+ posts Bio
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Yaƙi Da Ta’addanci: Gwamnan Zamfara Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Bisa Ƙwato Ɗarurruwan Shanu
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    ’Yan Bindiga Sun Sace Dattawan Zamfara 50 Yayin Taron Sulhu A Cikin Daji
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Ɗan Takarar Sanata A Zamfara Ya Koka Kan Yi Wa Rayuwarsa Barazana
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Abdulaziz Yari Ya Bukaci Limamai Su Ƙara Addu’a Kan Yaƙi Da Ƴan Bindiga A Zamfara
Gwamna Lawal
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
  • Sulaiman
    Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
  • Sulaiman
    Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa
  • Sulaiman
    Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

MASU ALAKA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Next Post
Yajin aiki

Nijeriya Za Ta Fara Aiwatar Da Yarjejeniyoyin Haɗin Gwiwa Da Kafofin Watsa Labarai Na Sin – Ministan Yaɗa Labarai

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.