• English
  • Business News
Monday, October 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Da UNODC Sun Gabatar Da Rahoton Binciken Kwararar ‘Yan Nijeriya Zuwa Ƙasashen Ƙetare

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
UNODC

Hukumar shige da fice ta ƙasa (NIS) tare da haɗin gwiwar Ofishin Majalisar Ɗinkin Duniya da ke yaƙi da shan miyagun ƙwayori da aikata laifuka (UNODC) sun gabatar da rahoton binciken da suka yi a kan ‘yan Nijeriya da ke kwarara zuwa ƙasashen ƙetare.

Rahoton da aka yi masa laƙabi da SOM an ƙaddamar da shi ne a shelkwatan NIS da ke Abuja a ranar Talata.

UNODC

Da yake gabatar da jawabin maraba, shugaban hukumar NIS, CGI, Idris Isa Jere ya bayyana cewa duk wani bincike yana da sakamakon. Don haka suka ƙaddamar da wannan rahoton wanda yake buƙatar ɗaukan mataki bayan an kammala nazari tare da yin aiki da shi.

  • Katafaren Jirgin Ruwa Ya Kife Da Mutane A Kogin Ibi Da Ke Jihar Taraba

CGI Isah Jere, wanda ya samu wakilcin DCG Haliru ya jinjina wa UNODC bisa gudanar da kyakkyawan aiki na samun nasarar bankaɗo yawan ‘yan Nijeriya da ke yin hijira zuwa ƙasashen ƙetare ba bisa ƙa’ida ba.

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”

UNODC

A cewarsa, hukumarsa za ta yi aiki da wannan rahoton wajen yaƙi da safarar ‘yan Nijeriya zuwa ƙasashen ƙetare. Sannan ya yi kira da dukkan jami’an hukumar NIS da su gudanar da ayyukansu kamar yadda doka ta tanada.

A nasa jawabin, wakilin UNODC, Oliver Stolpe ya bayyana cewa an gudanar da wannan bincike ne domin samun nasarar daƙile safarar mutane ba bisa ƙa’ida ba. Ya ce wannan rahoton zai taimaka wa ƙasashe wajen toshe ɓarnar safarar mutane ta mummunar hanya.

UNODC

Ya ƙara da cewa UNODC tana ƙoƙarin taimaka wa mambobin ƙasashe da ke cikin Majalisar Ɗinkin Duniya wajen hana safarar mutane ba bisa ƙa’ida ba, wanda zai haddasa haɗin kai a tsakanin ƙasa da ƙasa wajen gudanar da sintirin yaƙi da safarar mutane.

Ya ce wannan bincike ba zai taɓa samun nasara ba sai da haɗin gwiwar shugabancin hukumar NIS da gwamnatin ƙasashen Kanada da Danmak wajen bayar da kuɗaɗe domin samun nasara.

Wakilin ya ce binciken ya samar da alƙamuman yawan ‘yan Nijeriya da ke karara zuwa ƙasashen waje domin faɗakar da gwamnatin Nijeriya da sarakuna da malaman addinai da dukkkan sauran al’umma.

UNODC

Ya ce ‘yan Nijeriya ne suka fi yin balaguro zuwa ƙasashen Turai da Asiya a tsakanin ƙasashen yammacin Afirka.  Ya ƙara da cewa sun haɗa kai ne da hukumar NIS da sauran hukumomi da ƙungiyoyin fararen hula domin yaƙi da safarar ‘yan Nijeriya ta mummunar hanya.

Shi ma ministan harkokin cikin gida, Ogbeni Rauf Aregbesola ya bayyana cewa safarar mutane ba bisa ƙa’ida ya zama ruwan dare a cikin al’umma saboda matsalolin tattalin arziki, wanda ke sauya asalin ɗabi’un al’umma. Ministan wanda ya samu wakilcin babbar jami’an ma’aikatan harkokin cikin gida Atiruke Ajiboye. Ya ce yana gode wa dukkan waɗanda suka bayar da goyon baya har wannan rahoton ya kammala na safarar mutane ba bisa ƙa’ida ba.

UNODC

Ya nuna farin cikinsa game da wannan shirin da zai tsaftace al’umma wajen faɗakar da mutane illar safarar mutane domin ceto rayukansu.

  • https://www.unodc.org/

Rahoton na NIS da UNODC zai bude sabon babi na bullo da sabbin hanyoyin dakile safarar mutane ba bisa ka’ida ba

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum
Manyan Labarai

Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

October 26, 2025
“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”
Labarai

“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”

October 26, 2025
Dalilin Da Suka Sa Hisbah Ta Dakatar Da Auren Ƴan TikTok A Kano
Manyan Labarai

Dalilin Da Suka Sa Hisbah Ta Dakatar Da Auren Ƴan TikTok A Kano

October 26, 2025
Next Post
Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Gargadi Gwamnati Kan Ta Inganta Ilimin Bai-Daya

Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Gargadi Gwamnati Kan Ta Inganta Ilimin Bai-Daya

LABARAI MASU NASABA

Tunawa Da Dawowar Taiwan Kasar Sin Shekaru 80 Da Suka Wuce Yana Da Ma’ana Sosai

Tunawa Da Dawowar Taiwan Kasar Sin Shekaru 80 Da Suka Wuce Yana Da Ma’ana Sosai

October 26, 2025
Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

October 26, 2025
Kara Bude Kofofin Sin Zai Samar Da Karin Gajiya A Fannin Bunkasar Duniya

Kara Bude Kofofin Sin Zai Samar Da Karin Gajiya A Fannin Bunkasar Duniya

October 26, 2025
“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”

“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”

October 26, 2025
Ya Zuwa Satumban Bana Adadin Lantarki Da Sin Ta Samar Ya Karu Da Kaso 17.5%

Ya Zuwa Satumban Bana Adadin Lantarki Da Sin Ta Samar Ya Karu Da Kaso 17.5%

October 26, 2025
Dalilin Da Suka Sa Hisbah Ta Dakatar Da Auren Ƴan TikTok A Kano

Dalilin Da Suka Sa Hisbah Ta Dakatar Da Auren Ƴan TikTok A Kano

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati Na Shekarar 2025, Dakta Zacch Adedeji

October 26, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Mai Taken “Shugabancin Duniya Da Samun Wadata Tare A Yankin Asiya Da Pasifik” A Beijing

An Yi Taron Tattaunawa Mai Taken “Shugabancin Duniya Da Samun Wadata Tare A Yankin Asiya Da Pasifik” A Beijing

October 26, 2025
Sin Da Amurka Sun Cimma Matsaya Dangane Da Tsare-Tsaren Warware Batutuwan Cinikayya Da Suke Mayar Da Hankali A Kai

Sin Da Amurka Sun Cimma Matsaya Dangane Da Tsare-Tsaren Warware Batutuwan Cinikayya Da Suke Mayar Da Hankali A Kai

October 26, 2025
Sharhi: Wannan Manufar Sin Za Ta Sa Kaimin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

Sharhi: Wannan Manufar Sin Za Ta Sa Kaimin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

October 26, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.