• English
  • Business News
Tuesday, July 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Da UNODC Sun Gabatar Da Rahoton Binciken Kwararar ‘Yan Nijeriya Zuwa Ƙasashen Ƙetare

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Labarai
0
NIS Da UNODC Sun Gabatar Da Rahoton Binciken Kwararar ‘Yan Nijeriya Zuwa Ƙasashen Ƙetare
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar shige da fice ta ƙasa (NIS) tare da haɗin gwiwar Ofishin Majalisar Ɗinkin Duniya da ke yaƙi da shan miyagun ƙwayori da aikata laifuka (UNODC) sun gabatar da rahoton binciken da suka yi a kan ‘yan Nijeriya da ke kwarara zuwa ƙasashen ƙetare.

Rahoton da aka yi masa laƙabi da SOM an ƙaddamar da shi ne a shelkwatan NIS da ke Abuja a ranar Talata.

UNODC

Da yake gabatar da jawabin maraba, shugaban hukumar NIS, CGI, Idris Isa Jere ya bayyana cewa duk wani bincike yana da sakamakon. Don haka suka ƙaddamar da wannan rahoton wanda yake buƙatar ɗaukan mataki bayan an kammala nazari tare da yin aiki da shi.

  • Katafaren Jirgin Ruwa Ya Kife Da Mutane A Kogin Ibi Da Ke Jihar Taraba

CGI Isah Jere, wanda ya samu wakilcin DCG Haliru ya jinjina wa UNODC bisa gudanar da kyakkyawan aiki na samun nasarar bankaɗo yawan ‘yan Nijeriya da ke yin hijira zuwa ƙasashen ƙetare ba bisa ƙa’ida ba.

Labarai Masu Nasaba

Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

UNODC

A cewarsa, hukumarsa za ta yi aiki da wannan rahoton wajen yaƙi da safarar ‘yan Nijeriya zuwa ƙasashen ƙetare. Sannan ya yi kira da dukkan jami’an hukumar NIS da su gudanar da ayyukansu kamar yadda doka ta tanada.

A nasa jawabin, wakilin UNODC, Oliver Stolpe ya bayyana cewa an gudanar da wannan bincike ne domin samun nasarar daƙile safarar mutane ba bisa ƙa’ida ba. Ya ce wannan rahoton zai taimaka wa ƙasashe wajen toshe ɓarnar safarar mutane ta mummunar hanya.

UNODC

Ya ƙara da cewa UNODC tana ƙoƙarin taimaka wa mambobin ƙasashe da ke cikin Majalisar Ɗinkin Duniya wajen hana safarar mutane ba bisa ƙa’ida ba, wanda zai haddasa haɗin kai a tsakanin ƙasa da ƙasa wajen gudanar da sintirin yaƙi da safarar mutane.

Ya ce wannan bincike ba zai taɓa samun nasara ba sai da haɗin gwiwar shugabancin hukumar NIS da gwamnatin ƙasashen Kanada da Danmak wajen bayar da kuɗaɗe domin samun nasara.

Wakilin ya ce binciken ya samar da alƙamuman yawan ‘yan Nijeriya da ke karara zuwa ƙasashen waje domin faɗakar da gwamnatin Nijeriya da sarakuna da malaman addinai da dukkkan sauran al’umma.

UNODC

Ya ce ‘yan Nijeriya ne suka fi yin balaguro zuwa ƙasashen Turai da Asiya a tsakanin ƙasashen yammacin Afirka.  Ya ƙara da cewa sun haɗa kai ne da hukumar NIS da sauran hukumomi da ƙungiyoyin fararen hula domin yaƙi da safarar ‘yan Nijeriya ta mummunar hanya.

Shi ma ministan harkokin cikin gida, Ogbeni Rauf Aregbesola ya bayyana cewa safarar mutane ba bisa ƙa’ida ya zama ruwan dare a cikin al’umma saboda matsalolin tattalin arziki, wanda ke sauya asalin ɗabi’un al’umma. Ministan wanda ya samu wakilcin babbar jami’an ma’aikatan harkokin cikin gida Atiruke Ajiboye. Ya ce yana gode wa dukkan waɗanda suka bayar da goyon baya har wannan rahoton ya kammala na safarar mutane ba bisa ƙa’ida ba.

UNODC

Ya nuna farin cikinsa game da wannan shirin da zai tsaftace al’umma wajen faɗakar da mutane illar safarar mutane domin ceto rayukansu.

  • https://www.unodc.org/

Rahoton na NIS da UNODC zai bude sabon babi na bullo da sabbin hanyoyin dakile safarar mutane ba bisa ka’ida ba

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

IAEA: Za A Tattauna Batun Hadin Gwiwa Tsakanin Amurka Da Birtaniya Da Australiya

Next Post

Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Gargadi Gwamnati Kan Ta Inganta Ilimin Bai-Daya

Related

Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina
Manyan Labarai

Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati

40 minutes ago
Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa
Da ɗumi-ɗuminsa

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

9 hours ago
Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci
Da ɗumi-ɗuminsa

Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

10 hours ago
Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

13 hours ago
Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas, Ya Yi Jimamin Rasuwar Buhari, Ya Ce Mutuwa Ce Da Ta Girgiza Shi
Da ɗumi-ɗuminsa

SDP: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yi Wa El-Rufai Shaguɓe Da Ayyana Shi A Matsayin Ɗan Gudun Hijirar Siyasa

15 hours ago
Sojoji, DSS Sun Hallaka Ƴan Bindiga 45 A Neja
Manyan Labarai

Sojoji, DSS Sun Hallaka Ƴan Bindiga 45 A Neja

17 hours ago
Next Post
Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Gargadi Gwamnati Kan Ta Inganta Ilimin Bai-Daya

Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Gargadi Gwamnati Kan Ta Inganta Ilimin Bai-Daya

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina

Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati

July 29, 2025
An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

July 28, 2025
Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

July 28, 2025
Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa

Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa

July 28, 2025
Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

July 28, 2025
An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden

An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden

July 28, 2025
Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana

July 28, 2025
Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

July 28, 2025
Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

July 28, 2025
Gwamnatin Sakkwato Ta Ƙaddamar Da Sababbin Motoci 30, Don Bunƙasa Sha’anin Sufuri A Jihar

Super Falcons Sun Iso Abuja Ɗauke Da Kofin WAFCON

July 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.