ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Da UNODC Sun Gabatar Da Rahoton Binciken Kwararar ‘Yan Nijeriya Zuwa Ƙasashen Ƙetare

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
UNODC

Hukumar shige da fice ta ƙasa (NIS) tare da haɗin gwiwar Ofishin Majalisar Ɗinkin Duniya da ke yaƙi da shan miyagun ƙwayori da aikata laifuka (UNODC) sun gabatar da rahoton binciken da suka yi a kan ‘yan Nijeriya da ke kwarara zuwa ƙasashen ƙetare.

Rahoton da aka yi masa laƙabi da SOM an ƙaddamar da shi ne a shelkwatan NIS da ke Abuja a ranar Talata.

UNODC

ADVERTISEMENT

Da yake gabatar da jawabin maraba, shugaban hukumar NIS, CGI, Idris Isa Jere ya bayyana cewa duk wani bincike yana da sakamakon. Don haka suka ƙaddamar da wannan rahoton wanda yake buƙatar ɗaukan mataki bayan an kammala nazari tare da yin aiki da shi.

  • Katafaren Jirgin Ruwa Ya Kife Da Mutane A Kogin Ibi Da Ke Jihar Taraba

CGI Isah Jere, wanda ya samu wakilcin DCG Haliru ya jinjina wa UNODC bisa gudanar da kyakkyawan aiki na samun nasarar bankaɗo yawan ‘yan Nijeriya da ke yin hijira zuwa ƙasashen ƙetare ba bisa ƙa’ida ba.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

UNODC

A cewarsa, hukumarsa za ta yi aiki da wannan rahoton wajen yaƙi da safarar ‘yan Nijeriya zuwa ƙasashen ƙetare. Sannan ya yi kira da dukkan jami’an hukumar NIS da su gudanar da ayyukansu kamar yadda doka ta tanada.

A nasa jawabin, wakilin UNODC, Oliver Stolpe ya bayyana cewa an gudanar da wannan bincike ne domin samun nasarar daƙile safarar mutane ba bisa ƙa’ida ba. Ya ce wannan rahoton zai taimaka wa ƙasashe wajen toshe ɓarnar safarar mutane ta mummunar hanya.

UNODC

Ya ƙara da cewa UNODC tana ƙoƙarin taimaka wa mambobin ƙasashe da ke cikin Majalisar Ɗinkin Duniya wajen hana safarar mutane ba bisa ƙa’ida ba, wanda zai haddasa haɗin kai a tsakanin ƙasa da ƙasa wajen gudanar da sintirin yaƙi da safarar mutane.

Ya ce wannan bincike ba zai taɓa samun nasara ba sai da haɗin gwiwar shugabancin hukumar NIS da gwamnatin ƙasashen Kanada da Danmak wajen bayar da kuɗaɗe domin samun nasara.

Wakilin ya ce binciken ya samar da alƙamuman yawan ‘yan Nijeriya da ke karara zuwa ƙasashen waje domin faɗakar da gwamnatin Nijeriya da sarakuna da malaman addinai da dukkkan sauran al’umma.

UNODC

Ya ce ‘yan Nijeriya ne suka fi yin balaguro zuwa ƙasashen Turai da Asiya a tsakanin ƙasashen yammacin Afirka.  Ya ƙara da cewa sun haɗa kai ne da hukumar NIS da sauran hukumomi da ƙungiyoyin fararen hula domin yaƙi da safarar ‘yan Nijeriya ta mummunar hanya.

Shi ma ministan harkokin cikin gida, Ogbeni Rauf Aregbesola ya bayyana cewa safarar mutane ba bisa ƙa’ida ya zama ruwan dare a cikin al’umma saboda matsalolin tattalin arziki, wanda ke sauya asalin ɗabi’un al’umma. Ministan wanda ya samu wakilcin babbar jami’an ma’aikatan harkokin cikin gida Atiruke Ajiboye. Ya ce yana gode wa dukkan waɗanda suka bayar da goyon baya har wannan rahoton ya kammala na safarar mutane ba bisa ƙa’ida ba.

UNODC

Ya nuna farin cikinsa game da wannan shirin da zai tsaftace al’umma wajen faɗakar da mutane illar safarar mutane domin ceto rayukansu.

  • https://www.unodc.org/

Rahoton na NIS da UNODC zai bude sabon babi na bullo da sabbin hanyoyin dakile safarar mutane ba bisa ka’ida ba

 

UNODC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Gargadi Gwamnati Kan Ta Inganta Ilimin Bai-Daya

Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Gargadi Gwamnati Kan Ta Inganta Ilimin Bai-Daya

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.