• English
  • Business News
Thursday, October 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Reshen Bayelsa Ta Fara Horar Da Jami’anta Kan Tsarin Aiki Da Sarrafa Makamai

by Khalid Idris Doya
3 years ago
NIS

Hukumar kula da shige da fice ta kasa (NIS) reshen jihar Bayelsa a karkashin jagorancin Kwanturola James Sunday, ta fara horas da manyan jami’anta kan tsari da inganta aiki yayin da kuma ake horas da kananan jami’ai kan yadda za su kware wajen saffara makamai a Yenagoa da ke jihar.

  • 2023: Manyan ‘Yan Takara Na Shafa Wa Juna Kashin Kaji

Horaswar wacce ta kasance na kwana guda ga manyan jami’an yayin da su kuma kananan jami’an da ake horas da su kan saffara makamai za su shafe tsawon mako guda su na amsar horon.

Da ya ke tofa albarkacin bakinsa kan wannan horaswar, Kwanturola James Sunday, ya ce an dauki wannan matakin ne domin yadda za a kara wa manyan jami’an ilimin yadda za su gudanar da aiki a yayin babban zaben 2023 cikin kwanciyar hankali da kwarewa.

Ya ce, “Haramun ne wani jami’i ya tsunduma cikin siyasa, aikinmu a fayyayace yake a kan zabe shi ne yi aikin wucin gadi ko na musamman domin tabbatar da komai sun tafi daidai. Tare da hadin guiwa da sauran takwarorinmu na tsaro, za mu bayar da gudunmawa wajen tabbatar da zaben ya gudana cikin inganci da sahihanci. Don haka wannan horaswar ta za taimaka sosai wa kowani jami’i ya samu gogewar yadda zai tafiyar da aikinsa a kowani lokaci.”

A sanarwar da Kakakin hukumar NIS reshen jihar Bayelsa ya fitar tare da aiko da kwafinta wa LEADERSHIP Hausa, ya kara da cewa, “Ba za mu yi sako-sako da kyautata tsaro a yayin zaben da ke tafe ba, babban aikin da ke gabanmu shi ne mu tabbatar cewa babu wani dan wata kasa (da ba Nijeriya ba) da ya shiga ko tsoma kansa cikin harkokin zaben Nijeriya. Kan hakan an jawo hankalin jami’anmu da su kara kwazo waje kula da masu shige da masu fice domin tabbatar da tsaro a dukkanin iyakokin shige da fice.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

“Kuma a tabbatar an cafke wani dan wata kasa da ya yi kokarin kutse cikin harkokin zaben kasar nan.”

Ya gargadi jami’ansu da su tabbatar sun tafiyar da komai bisa kwarewa da bin dokokin aiki a kowani lokacin.

Dangane da masu samun horo kan makamai kuwa, an shawarce da su maida hankali domin cimma manufar da ake ba su horon a kai na ganin sun samu cikakken kwarewar yadda za su tafiyar da makaman da su hannunsu a yayin da suke bakunan aikinsu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Asuu
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

October 29, 2025
Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro
Labarai

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

October 29, 2025
majalisar kasa
Labarai

Majalisar Wakilai Ta Amince Da Bukatar Amso Bashin Dala Biliyan 2.34 A Kasuwar Jari Ta Duniya

October 29, 2025
Next Post
Bukatar Daukar Mataki Kan Kisan Da ‘Yansanda Ke Wa Fararen Hula

Bukatar Daukar Mataki Kan Kisan Da ‘Yansanda Ke Wa Fararen Hula

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

October 29, 2025
Asuu

Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

October 29, 2025
Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

October 29, 2025
Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

October 29, 2025
An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

October 29, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Amince Da Bukatar Amso Bashin Dala Biliyan 2.34 A Kasuwar Jari Ta Duniya

October 29, 2025
An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

October 29, 2025
Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

October 29, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

October 29, 2025
COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

October 29, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.