• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Reshen Bayelsa Ta Fara Horar Da Jami’anta Kan Tsarin Aiki Da Sarrafa Makamai

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
NIS Reshen Bayelsa Ta Fara Horar Da Jami’anta Kan Tsarin Aiki Da Sarrafa Makamai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar kula da shige da fice ta kasa (NIS) reshen jihar Bayelsa a karkashin jagorancin Kwanturola James Sunday, ta fara horas da manyan jami’anta kan tsari da inganta aiki yayin da kuma ake horas da kananan jami’ai kan yadda za su kware wajen saffara makamai a Yenagoa da ke jihar.

  • 2023: Manyan ‘Yan Takara Na Shafa Wa Juna Kashin Kaji

Horaswar wacce ta kasance na kwana guda ga manyan jami’an yayin da su kuma kananan jami’an da ake horas da su kan saffara makamai za su shafe tsawon mako guda su na amsar horon.

Da ya ke tofa albarkacin bakinsa kan wannan horaswar, Kwanturola James Sunday, ya ce an dauki wannan matakin ne domin yadda za a kara wa manyan jami’an ilimin yadda za su gudanar da aiki a yayin babban zaben 2023 cikin kwanciyar hankali da kwarewa.

Ya ce, “Haramun ne wani jami’i ya tsunduma cikin siyasa, aikinmu a fayyayace yake a kan zabe shi ne yi aikin wucin gadi ko na musamman domin tabbatar da komai sun tafi daidai. Tare da hadin guiwa da sauran takwarorinmu na tsaro, za mu bayar da gudunmawa wajen tabbatar da zaben ya gudana cikin inganci da sahihanci. Don haka wannan horaswar ta za taimaka sosai wa kowani jami’i ya samu gogewar yadda zai tafiyar da aikinsa a kowani lokaci.”

A sanarwar da Kakakin hukumar NIS reshen jihar Bayelsa ya fitar tare da aiko da kwafinta wa LEADERSHIP Hausa, ya kara da cewa, “Ba za mu yi sako-sako da kyautata tsaro a yayin zaben da ke tafe ba, babban aikin da ke gabanmu shi ne mu tabbatar cewa babu wani dan wata kasa (da ba Nijeriya ba) da ya shiga ko tsoma kansa cikin harkokin zaben Nijeriya. Kan hakan an jawo hankalin jami’anmu da su kara kwazo waje kula da masu shige da masu fice domin tabbatar da tsaro a dukkanin iyakokin shige da fice.

Labarai Masu Nasaba

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

“Kuma a tabbatar an cafke wani dan wata kasa da ya yi kokarin kutse cikin harkokin zaben kasar nan.”

Ya gargadi jami’ansu da su tabbatar sun tafiyar da komai bisa kwarewa da bin dokokin aiki a kowani lokacin.

Dangane da masu samun horo kan makamai kuwa, an shawarce da su maida hankali domin cimma manufar da ake ba su horon a kai na ganin sun samu cikakken kwarewar yadda za su tafiyar da makaman da su hannunsu a yayin da suke bakunan aikinsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yansanda Sun Ceto Sarkin Da Aka Yi Garkuwa Da Shi A Filato

Next Post

Bukatar Daukar Mataki Kan Kisan Da ‘Yansanda Ke Wa Fararen Hula

Related

Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

14 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

14 hours ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

15 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

15 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

18 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

19 hours ago
Next Post
Bukatar Daukar Mataki Kan Kisan Da ‘Yansanda Ke Wa Fararen Hula

Bukatar Daukar Mataki Kan Kisan Da ‘Yansanda Ke Wa Fararen Hula

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.