ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Reshen Bayelsa Ta Fara Horar Da Jami’anta Kan Tsarin Aiki Da Sarrafa Makamai

by Khalid Idris Doya
4 years ago
NIS

Hukumar kula da shige da fice ta kasa (NIS) reshen jihar Bayelsa a karkashin jagorancin Kwanturola James Sunday, ta fara horas da manyan jami’anta kan tsari da inganta aiki yayin da kuma ake horas da kananan jami’ai kan yadda za su kware wajen saffara makamai a Yenagoa da ke jihar.

  • 2023: Manyan ‘Yan Takara Na Shafa Wa Juna Kashin Kaji

Horaswar wacce ta kasance na kwana guda ga manyan jami’an yayin da su kuma kananan jami’an da ake horas da su kan saffara makamai za su shafe tsawon mako guda su na amsar horon.

Da ya ke tofa albarkacin bakinsa kan wannan horaswar, Kwanturola James Sunday, ya ce an dauki wannan matakin ne domin yadda za a kara wa manyan jami’an ilimin yadda za su gudanar da aiki a yayin babban zaben 2023 cikin kwanciyar hankali da kwarewa.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Haramun ne wani jami’i ya tsunduma cikin siyasa, aikinmu a fayyayace yake a kan zabe shi ne yi aikin wucin gadi ko na musamman domin tabbatar da komai sun tafi daidai. Tare da hadin guiwa da sauran takwarorinmu na tsaro, za mu bayar da gudunmawa wajen tabbatar da zaben ya gudana cikin inganci da sahihanci. Don haka wannan horaswar ta za taimaka sosai wa kowani jami’i ya samu gogewar yadda zai tafiyar da aikinsa a kowani lokaci.”

A sanarwar da Kakakin hukumar NIS reshen jihar Bayelsa ya fitar tare da aiko da kwafinta wa LEADERSHIP Hausa, ya kara da cewa, “Ba za mu yi sako-sako da kyautata tsaro a yayin zaben da ke tafe ba, babban aikin da ke gabanmu shi ne mu tabbatar cewa babu wani dan wata kasa (da ba Nijeriya ba) da ya shiga ko tsoma kansa cikin harkokin zaben Nijeriya. Kan hakan an jawo hankalin jami’anmu da su kara kwazo waje kula da masu shige da masu fice domin tabbatar da tsaro a dukkanin iyakokin shige da fice.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

“Kuma a tabbatar an cafke wani dan wata kasa da ya yi kokarin kutse cikin harkokin zaben kasar nan.”

Ya gargadi jami’ansu da su tabbatar sun tafiyar da komai bisa kwarewa da bin dokokin aiki a kowani lokacin.

Dangane da masu samun horo kan makamai kuwa, an shawarce da su maida hankali domin cimma manufar da ake ba su horon a kai na ganin sun samu cikakken kwarewar yadda za su tafiyar da makaman da su hannunsu a yayin da suke bakunan aikinsu.

NIS
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Cafke Tsoho Mai Shekara 70 Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 8 Fyaɗe A Bauchi

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Bukatar Daukar Mataki Kan Kisan Da ‘Yansanda Ke Wa Fararen Hula

Bukatar Daukar Mataki Kan Kisan Da ‘Yansanda Ke Wa Fararen Hula

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.