• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Reshen Jihar Bayelsa Ta Yi Shirin Tunkarar Zaɓen 2023

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Labarai
0
NIS Reshen Jihar Bayelsa Ta Yi Shirin Tunkarar Zaɓen 2023
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar shige da fice ta ƙasa (NIS) reshen Jihar Bayelsa ta gudanar da taron ganawa da masu ruwa da tsaki da shugabannin al’ummar Nijar, Benin, Togo, Ghana da kuma na Mali a Yenagoa.

Hukumar NIS reshen Jihar Bayelsa ta bayyana taron ganawar ne a cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar 29 ga watan Satumbar 2022.

A zaman ganawarsa na musamman da kwanturololin hukumar na faɗin ƙasar nan a shalkwatan hukumar da ke Abuja, Shugaban hukumar NIS, CGI Isah Jere Idris ya ba su umurnin sa ido da duba waɗanda ba ‘yan Nijeriya ba domin shirin tunkarar zaɓen 2023, a cikin umurnin har da hana baƙin-haure yin zaɓe ko mallakar katin zaɓe ko kuma dukkan kayayyakin da ke da alaƙa da zane domin tsare iyakokin ƙasar nan.

  • Shirin Zaɓe: Mun Ƙwace Katin Zaɓe Da Shaidar Ɗan Ƙasa 526 Daga ‘Yan Ƙasar Waje – Shugaban NIS

Domin ƙarin haske a kan wannan umurni, hukumar NIS reshin Jihar Bayelsa ta yi gaban kanta wajen sake ilmantarwa da wayar da kan bakin-haure da ke zaune a Jihar Bayelsa domin cika wannan umurni wajen saka ido da kulawa da kwararowar baƙin-haure a cikin jihar, inda ake binciken maɓoyansu da ke saƙo da lungu a Yenagoa.

Sanarwar ta nuna cewa wasu daga cikin baƙin-hauren suna gudanar da sana’o’in da suka haɗa da gadi, wankin takalma, tala, sayar da fiyowata da yin acaɓa a ciki da wajen garin Yenagoa.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

Dukkan ɗaukacin rassan hukumar NIS an ba su umurnin sa ido da kulawa wajen bayyana wa hukumar rahoton sirri kan ayyukan da baƙin-haure suke gudanarwa a ƙananan hukumomi guda 8 da ke faɗin Jihar Bayelsa baya ga babban birnin jihar Yenago, wannan ƙoƙari ne na faɗaɗa umurnin da shugaban hukumar NIS ya bayar na ganin ya sauke nauyin da ya rataya a wuyansa, a matsayinsa na shugaban hukumar da ke kulawa da iyakokin Nijeriya.

Sanarwar ta ƙara da cewa wannan tsare-tsare zai ci gaba da gudana har zuwa zaɓen 2023 da ake fuskanta da kuma bayan zaɓen.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Da Argentina Sun Sha Alwashin Yayata Manufar Samar Da Al’umma Mai Makomar Bai Daya

Next Post

Kasar Sin Ta Samu Babban Ci Gaba A Fannin Raya Karkara Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

7 minutes ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

3 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

4 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

13 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

15 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

16 hours ago
Next Post
Kasar Sin Ta Samu Babban Ci Gaba A Fannin Raya Karkara Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata

Kasar Sin Ta Samu Babban Ci Gaba A Fannin Raya Karkara Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.