ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Reshen Jihar Bayelsa Ta Yi Shirin Tunkarar Zaɓen 2023

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
NIS

Hukumar shige da fice ta ƙasa (NIS) reshen Jihar Bayelsa ta gudanar da taron ganawa da masu ruwa da tsaki da shugabannin al’ummar Nijar, Benin, Togo, Ghana da kuma na Mali a Yenagoa.

Hukumar NIS reshen Jihar Bayelsa ta bayyana taron ganawar ne a cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar 29 ga watan Satumbar 2022.

A zaman ganawarsa na musamman da kwanturololin hukumar na faɗin ƙasar nan a shalkwatan hukumar da ke Abuja, Shugaban hukumar NIS, CGI Isah Jere Idris ya ba su umurnin sa ido da duba waɗanda ba ‘yan Nijeriya ba domin shirin tunkarar zaɓen 2023, a cikin umurnin har da hana baƙin-haure yin zaɓe ko mallakar katin zaɓe ko kuma dukkan kayayyakin da ke da alaƙa da zane domin tsare iyakokin ƙasar nan.

ADVERTISEMENT
  • Shirin Zaɓe: Mun Ƙwace Katin Zaɓe Da Shaidar Ɗan Ƙasa 526 Daga ‘Yan Ƙasar Waje – Shugaban NIS

Domin ƙarin haske a kan wannan umurni, hukumar NIS reshin Jihar Bayelsa ta yi gaban kanta wajen sake ilmantarwa da wayar da kan bakin-haure da ke zaune a Jihar Bayelsa domin cika wannan umurni wajen saka ido da kulawa da kwararowar baƙin-haure a cikin jihar, inda ake binciken maɓoyansu da ke saƙo da lungu a Yenagoa.

Sanarwar ta nuna cewa wasu daga cikin baƙin-hauren suna gudanar da sana’o’in da suka haɗa da gadi, wankin takalma, tala, sayar da fiyowata da yin acaɓa a ciki da wajen garin Yenagoa.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Dukkan ɗaukacin rassan hukumar NIS an ba su umurnin sa ido da kulawa wajen bayyana wa hukumar rahoton sirri kan ayyukan da baƙin-haure suke gudanarwa a ƙananan hukumomi guda 8 da ke faɗin Jihar Bayelsa baya ga babban birnin jihar Yenago, wannan ƙoƙari ne na faɗaɗa umurnin da shugaban hukumar NIS ya bayar na ganin ya sauke nauyin da ya rataya a wuyansa, a matsayinsa na shugaban hukumar da ke kulawa da iyakokin Nijeriya.

Sanarwar ta ƙara da cewa wannan tsare-tsare zai ci gaba da gudana har zuwa zaɓen 2023 da ake fuskanta da kuma bayan zaɓen.

NIS
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
Next Post
Kasar Sin Ta Samu Babban Ci Gaba A Fannin Raya Karkara Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata

Kasar Sin Ta Samu Babban Ci Gaba A Fannin Raya Karkara Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.