• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Reshen Jihar Ribas Ta Kaddamar Da “Operation Tsaron Iyaka”

by yahuzajere
2 years ago
in Labarai
0
NIS Reshen Jihar Ribas Ta Kaddamar Da “Operation Tsaron Iyaka”
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanturolan Hukumar Kula da Shige da Fice ta Jihar Ribas (NIS) James Sunday, ya yi wa manema labarai karin haske kan fara aikin “Operation Tsaron Iyaka” a Jihar Ribas.

Kwanturolan ya ce hakan ya samo asali ne daga ganawar da suka yi a jihar Akwa Ibom da mukaddashiyar kwanturola Janar ta Hukumar Shige da Fice, Caroline Wuraola Adepoju wadda ta kai ziyarar aiki ta kwanaki 2 a Akwa Ibom kuma ta ziyarci ofishin kula da iyakoki na ruwa a jihar.
Sauran manyan jami’ai masu mukamin Kwanturola na Shiyyar E na Hukumar Shige da Fice ta Nijeriya na cikin tawagarta, musamman Kwanturola Akwa Ibom, Abia, Cross River, Ebonyi, Rivers da na Sashen Kula da Iyaka ta Ruwa da ke Jihar Akwa Ibom.

  • “Da Mijina Ya Yi Min Kishiya, Gwamma Ya Rika Kwanciya Da ‘Ya`yanmu”

An yi ziyarar ce domin tantance ayyukan bakin iyaka, ayyuka da ayyukan tattalin arziki da aka gudanar a jihar Rivers kasancewar jihar a gabar ruwa.

Kwanturola James Sunday, ya ce “Operation Tsaron Iyaka” wanda ke nuni da karfafa tsaron kan iyaka shi ne abin da zai fi mayar da hankali a kai sakamakon taron da suka yi da kuma amfani da umarnin da mukaddashiyar Kwanturola Janar ta Hukumar Kula da Shige da Fice Caroline Wuraola Adepoju ta bayar, shi ya sa na yanke shawarar fara aikin tare da jami’anmu a Jihar Ribas.

“Jami’amu za su kai samame a wurare da maboya da tashar jiragen ruwa inda ake zargin ‘yan kasar waje da suka shigo Nijeriya ba bisa ka’ida ba suna boye a nan, tare da cafke su da gurfanar da duk wani mutum ko rukuni na bakin haure da aka gano suna zaune ba tare da ingantattun takardu na shigowa ba.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

“Za mu bazama aiki a wannan yunkuri na kawar da ‘yan ci-rani ba bisa ka’ida ba a Jihar Ribas wadanda za su iya shiga aikata cikin munanan ayyuka tare da gujewa gano su a duk lokacin da suka aikata wani laifi ko kuma suka shiga cikin wani abu mara kyau wanda na iya kaiwa ga rashin tsaro ga rayuwa da dukiyoyin mutane a Ribas.” In ji shi.

Sanarwar manema labarai da jami’in hulda da jama’a na reshen hukumar ta NIS da ke JIhar Ribas, ASI Nwosu Chukwu ya fitar, ta kara da cewa hukumar ta fara aiki nan take, kuma za ta ci gaba da aiki har sai ta gamsu da cewa ‘yan ci-rani ba bisa ka’ida ba sun tafi da kansu wuraren da suka kamata domin tsara takardunsu da kuma al’ummarsu ta bin ka’idar ECOWAS da sauran su, da aka shimfida bisa tanade-tanade na Dokar Shige da Fice ta 2015 da Dokokin 2017 da sauran manyan dokokin kasar.

Kwanturola James ya ba da tabbacin masu bin doka da oda daa cikin ‘yan ci-ranin a kullum suna ba su kariya da harkokin kasuwancinsu da rayuwarsu da dukiyoyinsu a Ribas sannan ya shawarci al’umma ko shugabannin kungiyoyi da su fito da jerin sunayen mambobinsu na jihar Ribas domin tabbatar da cewa kowa ya yi rajistar da ta kamata a hukumar ta Shige da Fice (NIS).


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Jihar RibasNISShige Da FiceTsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnan Gombe Ya Tura Sunayen Kwamishinoni 17 Ga Majalisar Jihar

Next Post

Tsadar Mai: Ba Gudu Ba Ja Da Baya Kan Zanga-Zanga -NLC

Related

Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

8 minutes ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

12 hours ago
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
Rahotonni

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

13 hours ago
Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah
Labarai

Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah

14 hours ago
Jihohin Da Ke Shirin Rage Kudin Wutar Lantarki Su Shirya Biyan Tallafi – Ministan Wuta
Labarai

Jihohin Da Ke Shirin Rage Kudin Wutar Lantarki Su Shirya Biyan Tallafi – Ministan Wuta

15 hours ago
majalisar kasa
Labarai

‘Yan Majalisa Sun Zargi Hukumomin Gwamnati Da Wawure Sama Da Naira Biliyan 103.8

16 hours ago
Next Post
Tsadar Mai: Ba Gudu Ba Ja Da Baya Kan Zanga-Zanga -NLC

Tsadar Mai: Ba Gudu Ba Ja Da Baya Kan Zanga-Zanga -NLC

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

July 26, 2025
Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

July 26, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

July 26, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

July 26, 2025
Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

July 25, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

July 25, 2025
Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

July 25, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

July 25, 2025
Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.