• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Shiyyar Arewa Maso Gabas Ta Kaddamar Da “Operation Tsaron Iyaka”

by yahuzajere
2 years ago
in Labarai
0
NIS

ACG James Sunday (a tsakiya) da sauran kwanturololin jihohin arewa maso gabas a wurin taron kaddamar da shirin

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban Ofishin Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa (NIS) mai kula da Shiyya ta Uku (Zone C) da ke da shalkwata a Bauchi, ya kaddamar ma da wani aiki mai lakabin “Operation Tsaron Iyaka”, jim kadan bayan babban jami’in shiyya na hukumar, ACG James Sunday yak ama aiki.

An gudanar da taro a tsakanin babban jami’in da kwanturololin NIS da ke jihohin Adamawa, Bauchi, Borno, Gombe, Filato da kuma Yobe da nufin karfafa ayyukan jami’an shige da fice a shiyyar arewa maso gabas da Filato.

Kamar yadda ACG James Sunday ya yi wa LEADERSHIP Hausa bayani, sun bullo da tsarin aikin ne bisa irin hobbasar da shugabar hukumar ta NIS, Caroline Wuaola Adepoju da Ministan Cikin Gida, Tunji Ojo suke yi a kan tsaron iyaka, “kuma shi ya sa jami’anmu suka mike haikan don sauke nauyin da ke wuyansu, shi ya sa muka gudanar da taron a Gombe ba a shalkwatarmu ta Bauchi ba.”

Da yake Karin haske kan dalilin bullo da aikin, ACG James Sunday ya ce, “A matsayina na Babban Jami’in Shiyya, an kawo ni ne don na yi aiki tukuru ba na zauna a ofis ba, wajibi ne kwamandojinmu da sauran jami’anmu su nuna shugabanci nagari da kansu ba sako ba domin karfafa gwiwar jami’ai. Ina da manyan ofishoshin jihohi guda shida a karkashina ciki har da shalkwatar shiyyar da kanta, tare da jami’ai dubu 3,081 a karkashin kulawata. Ba zan iya barinsu ba tare da fuskantar wata alkibla ba da kyakkyawan jagoranci a wannan aiki da Allah ya ba mu amanarsa a kasarmu.

“Ba za mu iya kunyata kasarmu ba da kuma amanar da aka ba mu ta aiki wurin tabbatar da cewa muna aiki da kwarewa bisa bin doka da kuma kare tsaron kasa. Don haka inaw a dukkan kwanturololi barka da zuwa tare da ba su tabbacin cewa mun bullo da wannan aiki ne saboda samun nasara da kara kare martabar aikinmu wanda za mu cimma burin haka bisa tabbacin da muke samu daga kwanturololin jihohi.”

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

ACG James Sunday, ya bayyana cewa taron nasu ya kudiri aniyar waiwaye game da tarihin ayyukan NIS da kuma la’akari da tsarin gudanar da tsaron Nijeriya domin su lalubo bakin zaren tabbatar da tsaron iyaka a yankin arewa maso gabas da kuma Filato.

Ya kara da cewa a wannan lokacin, ‘yan ta’adda da masu sace mutane suna garkuwa da su na kokarin mayar da tsarin tsaron Nijeriya abin dariya da ba’a wanda ta hanyar hakan jami’ai masu kwazon aiki sun rasa rayukansu, haka nan ‘yan kasa nagari tare da asarar tarin dukiyoyi.

“Wadannan miyagu suna tafka ta’asa ta hanyar sace-sacen mutane don karbar kudin fansa kuma su kashe wadanda suka kama. Wannan ya kamata ya zama kalubale ga duk wani kwamanda da aka tura aikin tsaron rayuka da dukiyoyi domin sauya irin rayuwar da al’umma ke yi yanzu. Ya kamata a sauya tsarin gudanar da aiki domin mayar da martini kan shaidancin da miyagun nan ke yi da ke barazana ga al’umma da kuma gudanar da shugabanci nagari. Wannan yana daga cikin kudurorina na aiki a wannan shiyya.

NIS

“Taronmu na yau ba zai iya warware dukkan abubuwan da suka shafi tsaro da ke nasaba da aikin NIS ba nak are iyakokin kasa da kula da shige da ficen mutane, amma tabbas zai ba da dama a shawo kan wasu matsaloli da suka shafi iyakoki da shige da fice a arewa maso gabas da Filato wanda ni da sauran kwanturololin jihohin wannan shiyya cikin taimakon Allah za mu yi tsayin daka wajen aiwatarwa daidai da tsarin ayyuka na NIS a fadin kasa a karkashin jagorancin Kwanturola Janar Caroline Wuraola Adepoju.

“Rahotonmu na wannan taron ba zai tafi a banza ba ko a jefa a kwandon shara saboda abubuwan da za a bullo da sun a basirar aiki, babban burinmu shi ne tabbatar da tsaron iyaka a arewa maso gabas, mun matsa kaimi fiye da lokutan baya ta hanyar aiki da sauran hukumomin tsaro domin kyautata yanayin rayuwar al’ummar kasa. A yau mun samu damar kai ziyara ta musamman ga Shugaban Kungiyar Gwamnonin Arewa kuma Gwamnan Jihar Gombe, Alhaji Muhammad Inuwa Yahya wanda mataimakinsa, Dakta Manassah Daniel Jatau ya wakilta, mun bayyana masa dalilin haduwarmu a jihar nan wanda ya yi lale marhabin da shi. Muna fata Allah ya ci gaba da daukaka darajar kasarmu baki daya.” In ji shi

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArewaHukumar Shige Da FiceImmigrationNISNorth EastShiyyaTsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Umarci A Sake Cafko Mata Dakta Idris Dutsen Tanshi

Next Post

‘Yansanda Sun Cafke Wasu Mutane Biyu Da Ake Zargi Da Satar Keke-napep A Kano

Related

Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

5 minutes ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

12 hours ago
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
Rahotonni

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

13 hours ago
Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah
Labarai

Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah

14 hours ago
Jihohin Da Ke Shirin Rage Kudin Wutar Lantarki Su Shirya Biyan Tallafi – Ministan Wuta
Labarai

Jihohin Da Ke Shirin Rage Kudin Wutar Lantarki Su Shirya Biyan Tallafi – Ministan Wuta

15 hours ago
majalisar kasa
Labarai

‘Yan Majalisa Sun Zargi Hukumomin Gwamnati Da Wawure Sama Da Naira Biliyan 103.8

16 hours ago
Next Post
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Mutane Biyu Da Ake Zargi Da Satar Keke-napep A Kano

‘Yansanda Sun Cafke Wasu Mutane Biyu Da Ake Zargi Da Satar Keke-napep A Kano

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

July 26, 2025
Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

July 26, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

July 26, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

July 26, 2025
Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

July 25, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

July 25, 2025
Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

July 25, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

July 25, 2025
Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.