• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Ƙara Ƙaimin Aiki, Inda Shugabanta Ya Buɗe Sabon Ofishin Ingancin Aiki

by Abdulrazaq Yahuza
3 years ago
in Labarai
0
NIS Ta Ƙara Ƙaimin Aiki, Inda Shugabanta Ya Buɗe Sabon Ofishin Ingancin Aiki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa bisa jagorancin shugabanta, CGI Isah Jere Idris, ta ƙara matsa ƙaimin tabbatar da ingancin aikin da take yi wa al’umma a cibiyoyin mu’amalolinta da ‘yan ƙasa.

Aiki

A sakamakon wannan sabon yunƙurin, shugabanta Isah Jere ya ƙaddamar da sabon katafaren ginin sashen kula da ingancin aiki da ake wa laƙabi da “SERVCOM”.

Aiki

Da yake jawabi a yayin bikin, Isah Jere ya sanar da sabbin abubuwan da suke ɓullo da shi domin tabbatar da ingancin aikin samar da fasfo da sauran sassan ayyuka na hukumar.

Labarai Masu Nasaba

Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta

NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159

Ya ƙara da cewa, “An samar da Sashen SERƁICOM na Hukumar Shige da Fice ta Nijeriya don ingancin aiki mai alfanu don tabbatar da gamsuwar abokan ciniki da kuma cike giɓin da za a iya samu a tsakanin NIS da abokan hulɗarta wajen gudanar da aiki.

aiki

“Gabaɗaya dai, Serɓicom a matsayin sashe tana aiki ne bisa muradin Fadar Shugaban Kasa da Tsarin Sauƙaƙa Yin Kasuwanci, Inda NIS ta yi aiki kuma tana ci gaba da aiki sosai. Ya kasance a rubuce a tarihi cewa NIS ta zo na farko a kan tsarin sauƙaƙa Yin Kasuwanci na Shugaban Ƙasa har sau shida (bi-da-bi).

Aiki

“Gwamnati aba ce da ta shafi jama’a kuma saboda jama’a, don haka, NIS ta mayar da hankali sosai a kan ingancin hidimar da ake yi wa ‘yan ƙasa da yadda ake biyan irin waɗannan buƙatu. Cibiyoyin gwamnati wakilci ne na gwamnati a matakai daban-daban. Galibi su ne tsarin ginshiƙan gwamnati, waɗanda ke zama wurin tuntuɓar jama’a da masu zaman kansu. A kan wannan NIS ba daban ba ce, ita ma tana ciki.

  • Barazanar Kone-konen Ofisoshin INEC Ga Zaben 2023

“Bari in tabbatar muku da cewa NIS ta himmatu wajen samar da sakamakon da ya dace da bukatun al’ummarmu ta yau ta amfani da kayan aikin da take da su a hannunta. Za mu kuma yi ƙoƙari mu yi wa duk masu ruwa da tsaki hidima cikin ƙayyadaddun lokuta mafi dacewa cikin ƙwarewarmu daidai gwargwado. Don haka muna kira ga jama’a da su ba mu goyon bayan da ya dace a ƙoƙarin da muke yi na bayar da gudunmawarmu ga samun ingantacciyar Nijeriya.” Ya bayyana.

Aiki

Wakazalika, CGI Isah Jere ya hori jami’an hukumar manya da ƙananan kowa ya yi ƙoƙarin inganta ƙwarewar aiki, domin a cewarsa, babu wurin ɓuya ga raggwaye.

“Ina kira ga duk Jami’ai da su yi amfani da wannan damar don haɓaka ƙwarewar ayyukansu. Ina kuma iya sanar da dukkan Jami’anmu cewa daga yanzu, a yanzu babu wurin buya ga duk wanda yake wasa da gudanar da aiki mai inganci. Yarjejeniyar tsarin aiki da aka sake fasali, yunƙuri ne na hana ragwanci da gazawar aiki saboda ta bayar da cikakkun bayanai a kan yadda za a bi a riƙa mu’amalar aiki da hukumar, ko neman ƙarin bayani, ko gabatar da korafe-korafe da kuma yadda za a nemi gyara wani abu da aka tafka ba daidai ba.

“Ina so in yi amfani da wannan damar wajen sanar da jama’a cewa a wani bangare na kokarin tsaftace tsarin fasfo, Hukumarmu ta bullo da tsari wanda zai ba masu neman fasfo damar zabar ranar da za a dauki bayansu a cibiyoyin hukumar. Wannan zai taimaka wa masu aiki su daidaita tsarin fasfo yayin da kuma masu neman fasfo za su samu damar zaɓen ranar da suka ga ta fi kwanciyar musu a a kai.

 

“A madadin manya da ƙananan jami’an Hukumar Shige da Fice ta Nijeriya, ina jinjina wa gwamnati da al’ummar Jihar Filato bisa goyon bayan da suke bai wa ma’aikatanmu tsawon shekaru. Muna mika godiya ta musamman ga mai girma gwamna bisa goyon baya irin na uban ƙasa da yake bai wa Kwanturola na jihar da kuma sauran hidima da ake wa hukumar.” Kamar yadda ya bayyana.

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3, Sun Kone Gidaje 22 A Gombe 

Next Post

Buhari Ya Yi Allah Wadai Da Sace Jarirai Sabbin Haihuwa A Anambra 

Related

An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa
Tsaro

Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta

1 hour ago
Kotu
Tsaro

NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159

2 hours ago
Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4
Tsaro

Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

3 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

5 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

16 hours ago
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
Rahotonni

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

18 hours ago
Next Post
Buhari Ya Yi Allah Wadai Da Sace Jarirai Sabbin Haihuwa A Anambra 

Buhari Ya Yi Allah Wadai Da Sace Jarirai Sabbin Haihuwa A Anambra 

LABARAI MASU NASABA

An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta

July 26, 2025
WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

July 26, 2025
Kotu

NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159

July 26, 2025
Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

July 26, 2025
Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

July 26, 2025
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

July 26, 2025
Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

July 26, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

July 26, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

July 26, 2025
Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.