• English
  • Business News
Sunday, October 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Kafa Tarihin Horas Da Jami’ai Inda Ta Yaye 1,800 Lokaci Guda A Kano 

by Abdulrazaq Yahuza
3 years ago
Kano

Hukumar Shige da Fice ta Ƙasa (NIS) ta yaye jami’ai dubu ɗaya da ɗari takwas daga Makarantar Horas Da Jami’an Shige da Fice ta Kano (ITSK) da kuma Kwalejin Horaswa ta Hukumar Kwastam (CTC).

Jami’an da aka yaye waɗanda da suka yi kwas na 23 na share fage, an yaye su ne a makarantar ta ITSK ranar Asabar 14 ga Janairun 2023.

Da yake jawabi, Shugaban NIS, Isah Jere Idris ya taya waɗanda aka yaye murna tare da yin kira a gare su, su yi cikakken aiki da horon da suka samu bisa dokoki da ƙa’idojin aiki na hukumar.

CGI Isah Jere wanda Mataimakin Kwanturola Janar, mai kula da sha’anin ma’aikata, Babangida Usman ya wakilta tare da duba faretin waɗanda aka yaye, ya bayyana cewa, mahukuntan hukumar na yanzu na ci gaba da duƙufa ka’in da na’in wajen inganta sha’anin jami’ai ta hanyar horaswa domin samar da ƙwararrun jami’ai da za su iya fuskantar ƙalubalen da ke tasowa a ɓangaren kula da tsaron iyakokin ƙasa da harkar shige da fice.

  • Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

CGI Isah Jere ya kuma nanata buƙatar da ake wa jami’an su kauce wa sakaci da zubar da mutuncin aikin musamman yanzu da ake fuskantar zaɓen 2023, kana ya jaddada cewa hukumar ba za ta lamunci komawa ‘yar gidan jiya ba. Ya buƙace su, su kasance ‘yan ba ruwana tare da tabbatar da cewa babu wani baƙo ɗan ƙasar waje da aka bari ya shiga cikin harkokin zaɓen.

LABARAI MASU NASABA

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

Kano
Wakilin CGI Isah Jere, ACGI Usman s bikin

Ya bayyana cewa, yaye ɗaliban na wannan karon ya kafa tarihi a NIS domin ba a taɓa samun adadin waɗanda hukumar ta horas da suka kai wannan adadin ba a lokaci guda. Ya jinjina Wa kwamandojin Makarantun horaswa na ITSK da NITSOL bisa tsara horaswar kamar yadda ya kamata.

Kano
Jami’an da aka yaye

CGI Isah Jere ya kuma gode wa Ministan Cikin Gida, Ogbeni Rauf Aregbesola da Gwamnatin Tarayya bisa goyon bayan da suke ci gaba da bai wa hukumar a ayyukanta tare da ƙara yawan jami’ai.
Sanarwar da ta fito daga Jami’in hulɗa da jama’a na NIS, Tony Akuneme ta yi ƙarin hasken cewa, cikin manyan baƙin da suka halarci bikin har da jakadan Nijeriya a Benin da Jakadan Nijeriya a Nijer, da Kodinetan Shiyya ta Biyu, Kwamandan Birget ta 3 da ke Kano da sauran manyan jami’an Gwamnatin Kano da sauran wakilan rundunonin tsaro da ke jihar.

 

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Tsaro

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja
Tsaro

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Next Post
Ali Rashid Al Nuaimi: Xinjiang Na Tafiya Kan Tafarki Na Gari 

Ali Rashid Al Nuaimi: Xinjiang Na Tafiya Kan Tafarki Na Gari 

LABARAI MASU NASABA

gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
ASUU

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.