• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Kafa Tarihin Horas Da Jami’ai Inda Ta Yaye 1,800 Lokaci Guda A Kano 

by Abdulrazaq Yahuza
2 years ago
in Labarai
0
NIS Ta Kafa Tarihin Horas Da Jami’ai Inda Ta Yaye 1,800 Lokaci Guda A Kano 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Shige da Fice ta Ƙasa (NIS) ta yaye jami’ai dubu ɗaya da ɗari takwas daga Makarantar Horas Da Jami’an Shige da Fice ta Kano (ITSK) da kuma Kwalejin Horaswa ta Hukumar Kwastam (CTC).

Jami’an da aka yaye waɗanda da suka yi kwas na 23 na share fage, an yaye su ne a makarantar ta ITSK ranar Asabar 14 ga Janairun 2023.

Da yake jawabi, Shugaban NIS, Isah Jere Idris ya taya waɗanda aka yaye murna tare da yin kira a gare su, su yi cikakken aiki da horon da suka samu bisa dokoki da ƙa’idojin aiki na hukumar.

CGI Isah Jere wanda Mataimakin Kwanturola Janar, mai kula da sha’anin ma’aikata, Babangida Usman ya wakilta tare da duba faretin waɗanda aka yaye, ya bayyana cewa, mahukuntan hukumar na yanzu na ci gaba da duƙufa ka’in da na’in wajen inganta sha’anin jami’ai ta hanyar horaswa domin samar da ƙwararrun jami’ai da za su iya fuskantar ƙalubalen da ke tasowa a ɓangaren kula da tsaron iyakokin ƙasa da harkar shige da fice.

  • Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

CGI Isah Jere ya kuma nanata buƙatar da ake wa jami’an su kauce wa sakaci da zubar da mutuncin aikin musamman yanzu da ake fuskantar zaɓen 2023, kana ya jaddada cewa hukumar ba za ta lamunci komawa ‘yar gidan jiya ba. Ya buƙace su, su kasance ‘yan ba ruwana tare da tabbatar da cewa babu wani baƙo ɗan ƙasar waje da aka bari ya shiga cikin harkokin zaɓen.

Labarai Masu Nasaba

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

Kano
Wakilin CGI Isah Jere, ACGI Usman s bikin

Ya bayyana cewa, yaye ɗaliban na wannan karon ya kafa tarihi a NIS domin ba a taɓa samun adadin waɗanda hukumar ta horas da suka kai wannan adadin ba a lokaci guda. Ya jinjina Wa kwamandojin Makarantun horaswa na ITSK da NITSOL bisa tsara horaswar kamar yadda ya kamata.

Kano
Jami’an da aka yaye

CGI Isah Jere ya kuma gode wa Ministan Cikin Gida, Ogbeni Rauf Aregbesola da Gwamnatin Tarayya bisa goyon bayan da suke ci gaba da bai wa hukumar a ayyukanta tare da ƙara yawan jami’ai.
Sanarwar da ta fito daga Jami’in hulɗa da jama’a na NIS, Tony Akuneme ta yi ƙarin hasken cewa, cikin manyan baƙin da suka halarci bikin har da jakadan Nijeriya a Benin da Jakadan Nijeriya a Nijer, da Kodinetan Shiyya ta Biyu, Kwamandan Birget ta 3 da ke Kano da sauran manyan jami’an Gwamnatin Kano da sauran wakilan rundunonin tsaro da ke jihar.

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

NNPC Zai Fara Aikin Hakar Man Fetur A Jihar Nasarawa A Watan Maris

Next Post

Ali Rashid Al Nuaimi: Xinjiang Na Tafiya Kan Tafarki Na Gari 

Related

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

5 hours ago
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano
Labarai

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

6 hours ago
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta
Labarai

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

8 hours ago
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

9 hours ago
EFCC Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Ɓullar Sabbin Hanyoyin Damfarar Kuɗi
Labarai

EFCC Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Ɓullar Sabbin Hanyoyin Damfarar Kuɗi

10 hours ago
Dangote Ya Yaba Wa Tinubu Kan Samar Da Ababen More Rayuwa A Nijeriya
Labarai

Dangote Ya Yaba Wa Tinubu Kan Samar Da Ababen More Rayuwa A Nijeriya

12 hours ago
Next Post
Ali Rashid Al Nuaimi: Xinjiang Na Tafiya Kan Tafarki Na Gari 

Ali Rashid Al Nuaimi: Xinjiang Na Tafiya Kan Tafarki Na Gari 

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

July 10, 2025
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

July 10, 2025
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

July 10, 2025
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

July 10, 2025
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.