ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Kafa Tarihin Horas Da Jami’ai Inda Ta Yaye 1,800 Lokaci Guda A Kano 

by Abdulrazaq Yahuza
4 years ago
Kano

Hukumar Shige da Fice ta Ƙasa (NIS) ta yaye jami’ai dubu ɗaya da ɗari takwas daga Makarantar Horas Da Jami’an Shige da Fice ta Kano (ITSK) da kuma Kwalejin Horaswa ta Hukumar Kwastam (CTC).

Jami’an da aka yaye waɗanda da suka yi kwas na 23 na share fage, an yaye su ne a makarantar ta ITSK ranar Asabar 14 ga Janairun 2023.

Da yake jawabi, Shugaban NIS, Isah Jere Idris ya taya waɗanda aka yaye murna tare da yin kira a gare su, su yi cikakken aiki da horon da suka samu bisa dokoki da ƙa’idojin aiki na hukumar.

ADVERTISEMENT

CGI Isah Jere wanda Mataimakin Kwanturola Janar, mai kula da sha’anin ma’aikata, Babangida Usman ya wakilta tare da duba faretin waɗanda aka yaye, ya bayyana cewa, mahukuntan hukumar na yanzu na ci gaba da duƙufa ka’in da na’in wajen inganta sha’anin jami’ai ta hanyar horaswa domin samar da ƙwararrun jami’ai da za su iya fuskantar ƙalubalen da ke tasowa a ɓangaren kula da tsaron iyakokin ƙasa da harkar shige da fice.

  • Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

CGI Isah Jere ya kuma nanata buƙatar da ake wa jami’an su kauce wa sakaci da zubar da mutuncin aikin musamman yanzu da ake fuskantar zaɓen 2023, kana ya jaddada cewa hukumar ba za ta lamunci komawa ‘yar gidan jiya ba. Ya buƙace su, su kasance ‘yan ba ruwana tare da tabbatar da cewa babu wani baƙo ɗan ƙasar waje da aka bari ya shiga cikin harkokin zaɓen.

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

Kano
Wakilin CGI Isah Jere, ACGI Usman s bikin

Ya bayyana cewa, yaye ɗaliban na wannan karon ya kafa tarihi a NIS domin ba a taɓa samun adadin waɗanda hukumar ta horas da suka kai wannan adadin ba a lokaci guda. Ya jinjina Wa kwamandojin Makarantun horaswa na ITSK da NITSOL bisa tsara horaswar kamar yadda ya kamata.

Kano
Jami’an da aka yaye

CGI Isah Jere ya kuma gode wa Ministan Cikin Gida, Ogbeni Rauf Aregbesola da Gwamnatin Tarayya bisa goyon bayan da suke ci gaba da bai wa hukumar a ayyukanta tare da ƙara yawan jami’ai.
Sanarwar da ta fito daga Jami’in hulɗa da jama’a na NIS, Tony Akuneme ta yi ƙarin hasken cewa, cikin manyan baƙin da suka halarci bikin har da jakadan Nijeriya a Benin da Jakadan Nijeriya a Nijer, da Kodinetan Shiyya ta Biyu, Kwamandan Birget ta 3 da ke Kano da sauran manyan jami’an Gwamnatin Kano da sauran wakilan rundunonin tsaro da ke jihar.

 

 

Kano
Abdulrazaq Yahuza
+ postsBio
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana (2)
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Saudiyya Ta Taya Nijeriya Murnar Cika Shekaru 64 Da Samun ‘Yancin Kai
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Majalisar Dinkin Duniya Ta Amince Da Wata Sabuwar Yarjejeniya Domin Inganta Tsarin Shugabancin Duniya

MASU ALAKA

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya
Labarai

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa
Manyan Labarai

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa
Manyan Labarai

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Next Post
Ali Rashid Al Nuaimi: Xinjiang Na Tafiya Kan Tafarki Na Gari 

Ali Rashid Al Nuaimi: Xinjiang Na Tafiya Kan Tafarki Na Gari 

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.