ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Kafa Tarihin Horas Da Jami’ai Inda Ta Yaye 1,800 Lokaci Guda A Kano 

by Abdulrazaq Yahuza
3 years ago
Kano

Hukumar Shige da Fice ta Ƙasa (NIS) ta yaye jami’ai dubu ɗaya da ɗari takwas daga Makarantar Horas Da Jami’an Shige da Fice ta Kano (ITSK) da kuma Kwalejin Horaswa ta Hukumar Kwastam (CTC).

Jami’an da aka yaye waɗanda da suka yi kwas na 23 na share fage, an yaye su ne a makarantar ta ITSK ranar Asabar 14 ga Janairun 2023.

Da yake jawabi, Shugaban NIS, Isah Jere Idris ya taya waɗanda aka yaye murna tare da yin kira a gare su, su yi cikakken aiki da horon da suka samu bisa dokoki da ƙa’idojin aiki na hukumar.

ADVERTISEMENT

CGI Isah Jere wanda Mataimakin Kwanturola Janar, mai kula da sha’anin ma’aikata, Babangida Usman ya wakilta tare da duba faretin waɗanda aka yaye, ya bayyana cewa, mahukuntan hukumar na yanzu na ci gaba da duƙufa ka’in da na’in wajen inganta sha’anin jami’ai ta hanyar horaswa domin samar da ƙwararrun jami’ai da za su iya fuskantar ƙalubalen da ke tasowa a ɓangaren kula da tsaron iyakokin ƙasa da harkar shige da fice.

  • Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

CGI Isah Jere ya kuma nanata buƙatar da ake wa jami’an su kauce wa sakaci da zubar da mutuncin aikin musamman yanzu da ake fuskantar zaɓen 2023, kana ya jaddada cewa hukumar ba za ta lamunci komawa ‘yar gidan jiya ba. Ya buƙace su, su kasance ‘yan ba ruwana tare da tabbatar da cewa babu wani baƙo ɗan ƙasar waje da aka bari ya shiga cikin harkokin zaɓen.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Kano
Wakilin CGI Isah Jere, ACGI Usman s bikin

Ya bayyana cewa, yaye ɗaliban na wannan karon ya kafa tarihi a NIS domin ba a taɓa samun adadin waɗanda hukumar ta horas da suka kai wannan adadin ba a lokaci guda. Ya jinjina Wa kwamandojin Makarantun horaswa na ITSK da NITSOL bisa tsara horaswar kamar yadda ya kamata.

Kano
Jami’an da aka yaye

CGI Isah Jere ya kuma gode wa Ministan Cikin Gida, Ogbeni Rauf Aregbesola da Gwamnatin Tarayya bisa goyon bayan da suke ci gaba da bai wa hukumar a ayyukanta tare da ƙara yawan jami’ai.
Sanarwar da ta fito daga Jami’in hulɗa da jama’a na NIS, Tony Akuneme ta yi ƙarin hasken cewa, cikin manyan baƙin da suka halarci bikin har da jakadan Nijeriya a Benin da Jakadan Nijeriya a Nijer, da Kodinetan Shiyya ta Biyu, Kwamandan Birget ta 3 da ke Kano da sauran manyan jami’an Gwamnatin Kano da sauran wakilan rundunonin tsaro da ke jihar.

 

 

Kano
Abdulrazaq Yahuza
+ postsBio
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana (2)
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Saudiyya Ta Taya Nijeriya Murnar Cika Shekaru 64 Da Samun ‘Yancin Kai
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Majalisar Dinkin Duniya Ta Amince Da Wata Sabuwar Yarjejeniya Domin Inganta Tsarin Shugabancin Duniya

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Ali Rashid Al Nuaimi: Xinjiang Na Tafiya Kan Tafarki Na Gari 

Ali Rashid Al Nuaimi: Xinjiang Na Tafiya Kan Tafarki Na Gari 

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.