• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NNPP Ba Ta Da Kudin Kalubalantar Nasarar Tinubu A Kotu –Buba Galadima

by Abubakar Abba
2 years ago
in Labarai
0
NNPP Ba Ta Da Kudin Kalubalantar Nasarar Tinubu A Kotu –Buba Galadima
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jigo a jam’iyyar NNPP Buba Galadima ya bayyana cewa, NNPP taki kalubalantar nasarar da zababben shugaban kasa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya samu a zaben shugaban kasa na 2023 a gaban kotu ne, domin ba ta da kudin da za ta yi hakan.

Galadima ya sanar da hakan ne a hirarsa da gidan talabijin na ARISE a kan ganawar sirri da tsakanin Sanata Rabiu Musa Kwankwaso na NNPP da Tinubu a kasar Faransa.

  • EFCC Na Binciken Gwamnan Zamfara Kan Almundahanar Biliyan 70
  • Xi Da Mai Dakinsa Sun Jagoranci Bikin Maraba Da Baki Mahalarta Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

An ruwaito cewa, Tinubu ya yi ganawar sirrin ne da Kwakwaso don ya samar da masahala a tsakanin Kwankwaso da Abdulmumin Jibrin, tsohon jami’in yakin neman zaben Tinubu kuma zababben dan majalisar wakilai da ya sauya sheka zuwa NNPP daga APC kafin zaben 2023.

Sai dai, ba a samun cikakkun bayanai kan ganawar sirrin da Tinubu ya yi da Kwankwaso ba, amma an ce, sun tattauna kan kafa gwamnatin hadin kan kasa a tsakanin jami’iyyun biyu.

Galadima da yake mayar da martani kan ganawar sirrin ta manayn ‘yan siyasar biyu ya ce, babu wani labari domin abu ne da bisa tahirin siyasar Nijeriya, hakan ya saba farauwa.

Labarai Masu Nasaba

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Ya ci gaba da cewa, komai yau a Nijeriya ya na zama labarai, inda ya ce, ganawar a tsakanin jagororin ‘yan siyasar biyu, bai kamata ace ta ja hankalin mutane ba.

Ya ci gaba da cewa, kamar yadda ku ka sani ne, Kwankwaso ya yi takarar shugaban kasa da Tinubu a 2023, inda NNPP ta zo na hudu, inda ya sanar da cewa, NNPP ce kawai ba ta je kotu ba, wanda mune ke da cikakkun dalilan zuwa kotu.

A cewarsa, ganawar sirri irin wannan da kuma tunanin kafa gwmnatin hada kan kasa, ba sabon abu ne a harkar siyasar Nijeriya ba domin irin wannan, ta taba faruwa a jamhuriya ta farko a tsakanin jami’yyun NCNC da NPC a taakanin jam’iyyun Azikiwe da Ahmadu Bello.

Ya bayyana cewa, daga baya sun kafa gwmnatin hada kan kasa a tsakanin NPC da NNDP wadda Cif Samuel Akintola na gabas ya jagoranta.

Ya kara da cewa, har ila yau, a rubuce yake a lokacin gwamnatin Shagari, jami’yyar NPP da Nnamdi Azikiwe ke jagoranta, sun kulla yarjejeniya da gwmnatin NPN.

Galadima ya yi nuni da cewa, wannan tarihi ne ya sake mai-maita kansa, a saboda haka ya na da kyau a ilimantar da matasa kan tarihin kasar su.

Da yake mayar da martani kan abinda yasa NNPP ba ta kalubalanci nasarar Tinubu a kotu kamar yadda PDP da LP da sauran jami’iyyu suka yi, ba Galadima ya ce, NNPP ba ta da wadatattun kudin da za ta yi hakan.

Ya ce, wannan abun a rubuce yake cewa, PDP ce ta kore mu ni da Kwankwaso, ba wai mun shiga takarar don mu dakatar da su daga cin nasara a zaben bane.

Ya ce, muna sane da cewa, zuwa kotu na bukatar kudade masu yawa wanda bamu da su, inda ya ce, duk wanda zai je kotu don kalubalantar zabe, akalla sai ya tanadi Naira biliyan biyar, mu kuma, ba mu da wadannan kudaden.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCBuba GaladimaKwankwasoNNPPTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

EFCC Na Binciken Gwamnan Zamfara Kan Almundahanar Biliyan 70

Next Post

Matsalar Kasa Biyan Basusukan Da Amurka Take Fuskanta Za Ta Kawowa Duniya Asara

Related

UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

3 hours ago
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista
Labarai

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

4 hours ago
gaza
Labarai

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

5 hours ago
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa
Labarai

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

7 hours ago
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja
Labarai

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

8 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

9 hours ago
Next Post
Matsalar Kasa Biyan Basusukan Da Amurka Take Fuskanta Za Ta Kawowa Duniya Asara

Matsalar Kasa Biyan Basusukan Da Amurka Take Fuskanta Za Ta Kawowa Duniya Asara

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.