• English
  • Business News
Wednesday, July 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NNPP Ta Maye Gurbin Dan Takarar Kujerar Dan Majalisa Da Mamba A Yola

by Muh'd Shafi'u Saleh
3 years ago
in Siyasa
0
NNPP Ta Maye Gurbin Dan Takarar Kujerar Dan Majalisa Da Mamba A Yola
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar NNPP ta maye gurbin dan takarar kujerar dan majalisar wakilai Mai wakiltar kananan hukumomin Toungo, Jada, Ganye da Mayo Belwa, Muhammad Bello, da mamba mai wakiltar mazabar Jada-Bulo a majalisar dokokin jihar, Hammatukur Yattasure.

Dama dan majalisar dokokin, shi ne shugaban masu rinjayen majalisar dokokin jihar, da magoya bayansa sun canja sheka daga jam’iyyar PDP mai mulki a jihar zuwa sabuwar jam’iyyar NNPP.

  • Abinda Ya Hana Jam’iyyar NNPP Da LP Hadewa – Kwankwaso

Da yake jawabin karban mamban a Yola, sakataren yanki na jam’iyyar Adamu Hammatukur Ribadu, yace jam’iyyar ta maye gurbin dan takarar kujerar dan majalisar wakilan ne, bisa doka, da tanadin hukumar zabe INEC.

Yace “kasan in ana kamun Kifi, in an kamo Giwan ruwa to sai gidan Sarki, to wannan kamun da mukayi, yasa muka kira wanda ya tsaya mana takara a kananan hukumomin Ganye, Jada Toungo da Mayo-Belwa, mukace ga kamunda mukayi.

“Shi da kansa yace ya sauka, ya rubuta cewa ya janye masa, don haka Honarabul Yettusure kai ne dan takaranmu, a kujerar dan majalisar wakilai mai wakiltar kananan hukumomin Ganye, Jada, Toungo da Mayo-Belwa, don ba zamu barka ka shigo NNPP ka tsaya a mamban jam’iyya kawai ba.

Labarai Masu Nasaba

Tsohon Ɗan Takarar Mataimakin Gwamnan Kaduna Na PDP Ya Koma ADC

Super Falcons Sun Iso Abuja Ɗauke Da Kofin WAFCON

“Me yasa mukace kai mana takara? don mun tabbata Mayo-Belwa, Ganye, Jada, Toungo, idan Allah ya yarda kujerarka ne, wannan muna da tabbaci akai, kamar yadda muka dauki alkawari wanda ya janye maka a takara, jam’iyya kuma ta yarda ta maye gurbinsa da kai” inji Ribadu.

Da shima ke jawabi Honorabul Hammatukur Yattasure, ya gode da karamcin da jam’iyyar ta nuna masa, yace bai shigo jam’iyyar da nufin yaudara ba.

Yace “ina son in tabbatar muku, zuwana wannan jam’iyya bana yaudara bane, na zo ne domin ci gaban Adamawa, Nijeriya da yankin da na fito, idan Allah ya so ya yarda duk wani abu da zamuyi da jama’a zamuyi.

“Domin dama problem din na jama’a ne, dattabai da talakawa, su ne masu shirin, idan za ku bamu cikakken hadinkai da goyon baya da shawarwarinmu ya zama abu daya, to idan Allah ya yarda mu zamu ci zabe” inji Yattasure.

Dama dai mamba mai wakiltar mazabar Jada-bulo a majalisar dokokin kuma shugaban masu rinjayen majalisar Hammatukur Yattasure, ya fadi zaben fidda gwanin kujerar dan majalisar wakilai mai wakiltar kananan hukumomin Ganye, Jada, Toungo da Maye Belwa, da jam’iyarsa ta PDP ta gudanar a kwanan baya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Burin Kasar Sin Shi Ne “A Gudu Tare A Tsira Tare”

Next Post

Sarkin Musulmi Ya Bukaci Yin Addu’o’i Na Musanman Don Magance Matsalar Tsaro

Related

Tsohon Ɗan Takarar Mataimakin Gwamnan Kaduna Na PDP Ya Koma ADC
Siyasa

Tsohon Ɗan Takarar Mataimakin Gwamnan Kaduna Na PDP Ya Koma ADC

22 hours ago
Gwamnatin Sakkwato Ta Ƙaddamar Da Sababbin Motoci 30, Don Bunƙasa Sha’anin Sufuri A Jihar
Da ɗumi-ɗuminsa

Super Falcons Sun Iso Abuja Ɗauke Da Kofin WAFCON

2 days ago
SDP Ta Kori Tsohon Gwamnan Kaduna El-Rufai
Labarai

SDP Ta Kori Tsohon Gwamnan Kaduna El-Rufai

2 days ago
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

4 days ago
Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa
Da ɗumi-ɗuminsa

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

5 days ago
Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100
Manyan Labarai

Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100

1 week ago
Next Post
Sarkin Musulmi Ya Bukaci Yin Addu’o’i Na Musanman Don Magance Matsalar Tsaro

Sarkin Musulmi Ya Bukaci Yin Addu'o'i Na Musanman Don Magance Matsalar Tsaro

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Nada Ribadu Da Wasu A Matsayin Masu Ba Shi Shawara

Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku Miƙa Wuya – Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Bindiga

July 30, 2025
Sin Da Benin Da Thailand Za Su Aiwatar Da Matakan Saukaka Tantance Kaya Na Kwastam

Sin Da Benin Da Thailand Za Su Aiwatar Da Matakan Saukaka Tantance Kaya Na Kwastam

July 29, 2025
Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

July 29, 2025
Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

July 29, 2025
Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

July 29, 2025
Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

July 29, 2025
Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

July 29, 2025
Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

July 29, 2025
An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa

An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa

July 29, 2025
Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

July 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.