ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, November 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NNPP Ta Maye Gurbin Dan Takarar Kujerar Dan Majalisa Da Mamba A Yola

by Muh'd Shafi'u Saleh
3 years ago
NNPP

Jam’iyyar NNPP ta maye gurbin dan takarar kujerar dan majalisar wakilai Mai wakiltar kananan hukumomin Toungo, Jada, Ganye da Mayo Belwa, Muhammad Bello, da mamba mai wakiltar mazabar Jada-Bulo a majalisar dokokin jihar, Hammatukur Yattasure.

Dama dan majalisar dokokin, shi ne shugaban masu rinjayen majalisar dokokin jihar, da magoya bayansa sun canja sheka daga jam’iyyar PDP mai mulki a jihar zuwa sabuwar jam’iyyar NNPP.

  • Abinda Ya Hana Jam’iyyar NNPP Da LP Hadewa – Kwankwaso

Da yake jawabin karban mamban a Yola, sakataren yanki na jam’iyyar Adamu Hammatukur Ribadu, yace jam’iyyar ta maye gurbin dan takarar kujerar dan majalisar wakilan ne, bisa doka, da tanadin hukumar zabe INEC.

ADVERTISEMENT

Yace “kasan in ana kamun Kifi, in an kamo Giwan ruwa to sai gidan Sarki, to wannan kamun da mukayi, yasa muka kira wanda ya tsaya mana takara a kananan hukumomin Ganye, Jada Toungo da Mayo-Belwa, mukace ga kamunda mukayi.

“Shi da kansa yace ya sauka, ya rubuta cewa ya janye masa, don haka Honarabul Yettusure kai ne dan takaranmu, a kujerar dan majalisar wakilai mai wakiltar kananan hukumomin Ganye, Jada, Toungo da Mayo-Belwa, don ba zamu barka ka shigo NNPP ka tsaya a mamban jam’iyya kawai ba.

LABARAI MASU NASABA

Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

“Me yasa mukace kai mana takara? don mun tabbata Mayo-Belwa, Ganye, Jada, Toungo, idan Allah ya yarda kujerarka ne, wannan muna da tabbaci akai, kamar yadda muka dauki alkawari wanda ya janye maka a takara, jam’iyya kuma ta yarda ta maye gurbinsa da kai” inji Ribadu.

Da shima ke jawabi Honorabul Hammatukur Yattasure, ya gode da karamcin da jam’iyyar ta nuna masa, yace bai shigo jam’iyyar da nufin yaudara ba.

Yace “ina son in tabbatar muku, zuwana wannan jam’iyya bana yaudara bane, na zo ne domin ci gaban Adamawa, Nijeriya da yankin da na fito, idan Allah ya so ya yarda duk wani abu da zamuyi da jama’a zamuyi.

“Domin dama problem din na jama’a ne, dattabai da talakawa, su ne masu shirin, idan za ku bamu cikakken hadinkai da goyon baya da shawarwarinmu ya zama abu daya, to idan Allah ya yarda mu zamu ci zabe” inji Yattasure.

Dama dai mamba mai wakiltar mazabar Jada-bulo a majalisar dokokin kuma shugaban masu rinjayen majalisar Hammatukur Yattasure, ya fadi zaben fidda gwanin kujerar dan majalisar wakilai mai wakiltar kananan hukumomin Ganye, Jada, Toungo da Maye Belwa, da jam’iyarsa ta PDP ta gudanar a kwanan baya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP
Siyasa

Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP

November 12, 2025
Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja
Labarai

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

November 7, 2025
Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha
Siyasa

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
Next Post
Sarkin Musulmi Ya Bukaci Yin Addu’o’i Na Musanman Don Magance Matsalar Tsaro

Sarkin Musulmi Ya Bukaci Yin Addu'o'i Na Musanman Don Magance Matsalar Tsaro

LABARAI MASU NASABA

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

November 12, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

November 12, 2025
Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 12, 2025
Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

November 12, 2025
Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

November 12, 2025
'yansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutane 4 Kan Zargin Fashi Da Makami A Bauchi

November 12, 2025
Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci

Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci

November 12, 2025
Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki

Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki

November 12, 2025
Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista

Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista

November 12, 2025
Majalisar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Bisa Zargin Rashin Ɗa’a

Majalisar Jihar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Kan Laifin Rashin Ɗa’a

November 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.