ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NNPP Ta Maye Gurbin Dan Takarar Kujerar Dan Majalisa Da Mamba A Yola

by Muh'd Shafi'u Saleh
4 years ago
NNPP

Jam’iyyar NNPP ta maye gurbin dan takarar kujerar dan majalisar wakilai Mai wakiltar kananan hukumomin Toungo, Jada, Ganye da Mayo Belwa, Muhammad Bello, da mamba mai wakiltar mazabar Jada-Bulo a majalisar dokokin jihar, Hammatukur Yattasure.

Dama dan majalisar dokokin, shi ne shugaban masu rinjayen majalisar dokokin jihar, da magoya bayansa sun canja sheka daga jam’iyyar PDP mai mulki a jihar zuwa sabuwar jam’iyyar NNPP.

  • Abinda Ya Hana Jam’iyyar NNPP Da LP Hadewa – Kwankwaso

Da yake jawabin karban mamban a Yola, sakataren yanki na jam’iyyar Adamu Hammatukur Ribadu, yace jam’iyyar ta maye gurbin dan takarar kujerar dan majalisar wakilan ne, bisa doka, da tanadin hukumar zabe INEC.

ADVERTISEMENT

Yace “kasan in ana kamun Kifi, in an kamo Giwan ruwa to sai gidan Sarki, to wannan kamun da mukayi, yasa muka kira wanda ya tsaya mana takara a kananan hukumomin Ganye, Jada Toungo da Mayo-Belwa, mukace ga kamunda mukayi.

“Shi da kansa yace ya sauka, ya rubuta cewa ya janye masa, don haka Honarabul Yettusure kai ne dan takaranmu, a kujerar dan majalisar wakilai mai wakiltar kananan hukumomin Ganye, Jada, Toungo da Mayo-Belwa, don ba zamu barka ka shigo NNPP ka tsaya a mamban jam’iyya kawai ba.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

“Me yasa mukace kai mana takara? don mun tabbata Mayo-Belwa, Ganye, Jada, Toungo, idan Allah ya yarda kujerarka ne, wannan muna da tabbaci akai, kamar yadda muka dauki alkawari wanda ya janye maka a takara, jam’iyya kuma ta yarda ta maye gurbinsa da kai” inji Ribadu.

Da shima ke jawabi Honorabul Hammatukur Yattasure, ya gode da karamcin da jam’iyyar ta nuna masa, yace bai shigo jam’iyyar da nufin yaudara ba.

Yace “ina son in tabbatar muku, zuwana wannan jam’iyya bana yaudara bane, na zo ne domin ci gaban Adamawa, Nijeriya da yankin da na fito, idan Allah ya so ya yarda duk wani abu da zamuyi da jama’a zamuyi.

“Domin dama problem din na jama’a ne, dattabai da talakawa, su ne masu shirin, idan za ku bamu cikakken hadinkai da goyon baya da shawarwarinmu ya zama abu daya, to idan Allah ya yarda mu zamu ci zabe” inji Yattasure.

Dama dai mamba mai wakiltar mazabar Jada-bulo a majalisar dokokin kuma shugaban masu rinjayen majalisar Hammatukur Yattasure, ya fadi zaben fidda gwanin kujerar dan majalisar wakilai mai wakiltar kananan hukumomin Ganye, Jada, Toungo da Maye Belwa, da jam’iyarsa ta PDP ta gudanar a kwanan baya.

NNPP
Muh'd Shafi'u Saleh
+ postsBio
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    Jami’in Tsaro Ya Mayar da Dala 505 Da Riyal 30 Da Ya Tsinta A Yola
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    Shahararren Malamin Addinin Islama A Adamawa Sheikh Ibrahim Abubakar Daware Ya Rasu
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    An Yi Wa ‘Yansanda 110 Ƙarin Girma A Adamawa
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    Gwamna Fintiri Ya Nada Sabbin Sarakuna 7 A Jihar Adamawa

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Sarkin Musulmi Ya Bukaci Yin Addu’o’i Na Musanman Don Magance Matsalar Tsaro

Sarkin Musulmi Ya Bukaci Yin Addu'o'i Na Musanman Don Magance Matsalar Tsaro

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.