ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NNPP Ta Maye Gurbin Dan Takarar Kujerar Dan Majalisa Da Mamba A Yola

by Muh'd Shafi'u Saleh
4 years ago
NNPP

Jam’iyyar NNPP ta maye gurbin dan takarar kujerar dan majalisar wakilai Mai wakiltar kananan hukumomin Toungo, Jada, Ganye da Mayo Belwa, Muhammad Bello, da mamba mai wakiltar mazabar Jada-Bulo a majalisar dokokin jihar, Hammatukur Yattasure.

Dama dan majalisar dokokin, shi ne shugaban masu rinjayen majalisar dokokin jihar, da magoya bayansa sun canja sheka daga jam’iyyar PDP mai mulki a jihar zuwa sabuwar jam’iyyar NNPP.

  • Abinda Ya Hana Jam’iyyar NNPP Da LP Hadewa – Kwankwaso

Da yake jawabin karban mamban a Yola, sakataren yanki na jam’iyyar Adamu Hammatukur Ribadu, yace jam’iyyar ta maye gurbin dan takarar kujerar dan majalisar wakilan ne, bisa doka, da tanadin hukumar zabe INEC.

ADVERTISEMENT

Yace “kasan in ana kamun Kifi, in an kamo Giwan ruwa to sai gidan Sarki, to wannan kamun da mukayi, yasa muka kira wanda ya tsaya mana takara a kananan hukumomin Ganye, Jada Toungo da Mayo-Belwa, mukace ga kamunda mukayi.

“Shi da kansa yace ya sauka, ya rubuta cewa ya janye masa, don haka Honarabul Yettusure kai ne dan takaranmu, a kujerar dan majalisar wakilai mai wakiltar kananan hukumomin Ganye, Jada, Toungo da Mayo-Belwa, don ba zamu barka ka shigo NNPP ka tsaya a mamban jam’iyya kawai ba.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

“Me yasa mukace kai mana takara? don mun tabbata Mayo-Belwa, Ganye, Jada, Toungo, idan Allah ya yarda kujerarka ne, wannan muna da tabbaci akai, kamar yadda muka dauki alkawari wanda ya janye maka a takara, jam’iyya kuma ta yarda ta maye gurbinsa da kai” inji Ribadu.

Da shima ke jawabi Honorabul Hammatukur Yattasure, ya gode da karamcin da jam’iyyar ta nuna masa, yace bai shigo jam’iyyar da nufin yaudara ba.

Yace “ina son in tabbatar muku, zuwana wannan jam’iyya bana yaudara bane, na zo ne domin ci gaban Adamawa, Nijeriya da yankin da na fito, idan Allah ya so ya yarda duk wani abu da zamuyi da jama’a zamuyi.

“Domin dama problem din na jama’a ne, dattabai da talakawa, su ne masu shirin, idan za ku bamu cikakken hadinkai da goyon baya da shawarwarinmu ya zama abu daya, to idan Allah ya yarda mu zamu ci zabe” inji Yattasure.

Dama dai mamba mai wakiltar mazabar Jada-bulo a majalisar dokokin kuma shugaban masu rinjayen majalisar Hammatukur Yattasure, ya fadi zaben fidda gwanin kujerar dan majalisar wakilai mai wakiltar kananan hukumomin Ganye, Jada, Toungo da Maye Belwa, da jam’iyarsa ta PDP ta gudanar a kwanan baya.

NNPP
Muh'd Shafi'u Saleh
+ postsBio
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    Jami’in Tsaro Ya Mayar da Dala 505 Da Riyal 30 Da Ya Tsinta A Yola
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    Shahararren Malamin Addinin Islama A Adamawa Sheikh Ibrahim Abubakar Daware Ya Rasu
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    An Yi Wa ‘Yansanda 110 Ƙarin Girma A Adamawa
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    Gwamna Fintiri Ya Nada Sabbin Sarakuna 7 A Jihar Adamawa

MASU ALAKA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
Siyasa

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
NNPP
Siyasa

Muna Da Yan Takarar Gwamna A Jihohi 28 Don Shiga Zaben 2027

September 6, 2026
Next Post
Sarkin Musulmi Ya Bukaci Yin Addu’o’i Na Musanman Don Magance Matsalar Tsaro

Sarkin Musulmi Ya Bukaci Yin Addu'o'i Na Musanman Don Magance Matsalar Tsaro

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.