• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Noman Dabino: Jigawa Ta Yi Hadaka Da Saudiyya

by Abubakar Abba
8 months ago
Dabino

Biyo bayan hadakar da aka kulla tsakanin wani kamfani na Kasar Saudiyya da Gwamnatin Jihar Jigawa, za a samar da sauyin noman Dabino a jihar.

An kulla wannan yarjejniyar ne tsakanin gwamnatin jihar da kuma kamfanin Saudiyyan, domin kara habaka noman Dabino a jihar.

  • An Bude Cibiyar Tattarawa Da Yada Labarai Ta Taruka Biyu Na Sin
  • Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Janye Bincike Kan Shigo Da Jan Karfe

Ta hanyar hadakar, za a yi amfani da fasahar kimiyya don samar da girbinsa mai dimbin yawa tare da samar da nau’ukansa da dama.

A cewar wasu bayanai da Hukumar Kula da Samar da Wadatccen Abinci da Aikin Gona ta Majalisar Dinkin Duniya ta fitar, Kasar Saudiyya ita ce ta biyu da ke kan gaba wajen noman Dabibo, domin kuwa tana samar da tan miliyan 1.61.

Kazalika, kasar Masar ita ce a kan gaba wajen noman Dabino a fadin duniya baki-daya, ganin cewa a shekarar 2022 kadai, ta noma Dabino kimanin tan miliyan 1.73.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

Ita kuwa Kasar Algeria, ita ce ta uku; inda ta noma Dabino kimanin tan miliyan 1.25.

Hadakar tsakanin Gwamnatin Jigawa da Saudiyya da kuma wani kamfanin aikin noma da ke kasar nan, wato ‘Netay Agro-Tech’, za ta kara taimakawa wajen sake habaka noman Dabinon a jihar.

A duk shekara, Nijeriya na noma Dabino kimanin tan 21,000, inda Jigawa ta kasance daga cikin jeren masu noman nasa.

A jawabinsa a gidan gwamnatin jihar da ke Dutse, a lokacin da ya karbi tawagar wata babbar gona da ke Kasar Saudiyya, wadda ta kware wajen noman Dabino tare da ba shi kulawar da ta dace, gwamnan jihar, Umar Namadi ya bayyana cewa, sabuwar hadakar za ta bude sabon babi ga noman Dabino a Jigawa.

Namadi ya kuma ba su tabbacin cewa, gwamnatinsa za ta bayar da goyon bayan cimma burin shirin, inda ya ce, hadakar ta yi daidai da kudurin gwamnatinsa na bunkasa aikin noma a jihar.

“Muna maraba da zuwan ku Jihar Jigawa, sannan kuma a shirye muke mu yi aiki tare da ku duba da cewa, al’ummar jihar za su amfana da wannan hadaka, kuma hadakar za ta taimaka wa Jigawa a bangaren noman Alkama.”

Ya bayar da tabbacin gwamnatinsa, kan samar da dukkanin kayan da ake bukata, domin tabbatar da an wazar da aikin.

Jagoran tawagar, Abdul’aziz Abdurrahman-Al-Awf, ya jaddada goyon bayan kamfanin, ta hanyar amfani da fasahar kimiyyar aikin noma, don habaka noman Dabino a jihar.

“Za mu tabbatar da cewa, an yi noman Dabino sau biyu a shekara, sannan kuma za mu tabbatar da mun horas da matasa a fannin, domin bai wa matasa horo na musamman”, in ji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Ɓarayi 13 Tare Da Ƙwato Shanu 27 A Kaduna
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

October 18, 2025
Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI
Noma Da Kiwo

Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI

October 18, 2025
Next Post
SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 1

SAHUR [Falalarsa Da Fa'idojinsa] Na 1

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ɗan Majalisa Na Shekarar 2025: Benjamin Okezie Kalu

October 26, 2025
An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

October 25, 2025
Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

October 25, 2025
An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

October 25, 2025

Daɓid Adeyemi

October 25, 2025
Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.