• English
  • Business News
Thursday, August 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Noman Dabino: Jigawa Ta Yi Hadaka Da Saudiyya

by Abubakar Abba
6 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Noman Dabino: Jigawa Ta Yi Hadaka Da Saudiyya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Biyo bayan hadakar da aka kulla tsakanin wani kamfani na Kasar Saudiyya da Gwamnatin Jihar Jigawa, za a samar da sauyin noman Dabino a jihar.

An kulla wannan yarjejniyar ne tsakanin gwamnatin jihar da kuma kamfanin Saudiyyan, domin kara habaka noman Dabino a jihar.

  • An Bude Cibiyar Tattarawa Da Yada Labarai Ta Taruka Biyu Na Sin
  • Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Janye Bincike Kan Shigo Da Jan Karfe

Ta hanyar hadakar, za a yi amfani da fasahar kimiyya don samar da girbinsa mai dimbin yawa tare da samar da nau’ukansa da dama.

A cewar wasu bayanai da Hukumar Kula da Samar da Wadatccen Abinci da Aikin Gona ta Majalisar Dinkin Duniya ta fitar, Kasar Saudiyya ita ce ta biyu da ke kan gaba wajen noman Dabibo, domin kuwa tana samar da tan miliyan 1.61.

Kazalika, kasar Masar ita ce a kan gaba wajen noman Dabino a fadin duniya baki-daya, ganin cewa a shekarar 2022 kadai, ta noma Dabino kimanin tan miliyan 1.73.

Labarai Masu Nasaba

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

Ita kuwa Kasar Algeria, ita ce ta uku; inda ta noma Dabino kimanin tan miliyan 1.25.

Hadakar tsakanin Gwamnatin Jigawa da Saudiyya da kuma wani kamfanin aikin noma da ke kasar nan, wato ‘Netay Agro-Tech’, za ta kara taimakawa wajen sake habaka noman Dabinon a jihar.

A duk shekara, Nijeriya na noma Dabino kimanin tan 21,000, inda Jigawa ta kasance daga cikin jeren masu noman nasa.

A jawabinsa a gidan gwamnatin jihar da ke Dutse, a lokacin da ya karbi tawagar wata babbar gona da ke Kasar Saudiyya, wadda ta kware wajen noman Dabino tare da ba shi kulawar da ta dace, gwamnan jihar, Umar Namadi ya bayyana cewa, sabuwar hadakar za ta bude sabon babi ga noman Dabino a Jigawa.

Namadi ya kuma ba su tabbacin cewa, gwamnatinsa za ta bayar da goyon bayan cimma burin shirin, inda ya ce, hadakar ta yi daidai da kudurin gwamnatinsa na bunkasa aikin noma a jihar.

“Muna maraba da zuwan ku Jihar Jigawa, sannan kuma a shirye muke mu yi aiki tare da ku duba da cewa, al’ummar jihar za su amfana da wannan hadaka, kuma hadakar za ta taimaka wa Jigawa a bangaren noman Alkama.”

Ya bayar da tabbacin gwamnatinsa, kan samar da dukkanin kayan da ake bukata, domin tabbatar da an wazar da aikin.

Jagoran tawagar, Abdul’aziz Abdurrahman-Al-Awf, ya jaddada goyon bayan kamfanin, ta hanyar amfani da fasahar kimiyyar aikin noma, don habaka noman Dabino a jihar.

“Za mu tabbatar da cewa, an yi noman Dabino sau biyu a shekara, sannan kuma za mu tabbatar da mun horas da matasa a fannin, domin bai wa matasa horo na musamman”, in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DabinoJigawaNoma
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Philippines Za Ta Dandana Kudarta Game Da Gudummawar Soja Da Amurka Ta Ba Ta

Next Post

SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 1

Related

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

5 days ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

6 days ago
Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

2 weeks ago
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya
Noma Da Kiwo

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

2 weeks ago
Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji
Noma Da Kiwo

Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji

2 weeks ago
Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje
Noma Da Kiwo

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

3 weeks ago
Next Post
SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 1

SAHUR [Falalarsa Da Fa'idojinsa] Na 1

LABARAI MASU NASABA

Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

August 21, 2025
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

August 21, 2025
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

August 21, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

August 21, 2025
NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

August 21, 2025
Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

August 21, 2025
Nijeriya Ta Kori Ƙarin ‘Yan Ƙasashen Waje 51 Da Aka Ɗaure Bisa Laifin Ta’addanci Da Zamba A Intanet

Nijeriya Ta Kori Ƙarin ‘Yan Ƙasashen Waje 51 Da Aka Ɗaure Bisa Laifin Ta’addanci Da Zamba A Intanet

August 21, 2025
Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka

Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka

August 21, 2025
Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan 

Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan 

August 21, 2025
Boniface

Ac Milan Na Tattaunawa Da Bayern Leverkusen Akan Yunkurin Daukar Boniface

August 20, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.