• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ofishin Jakadancin Faransa Da Hadin Gwiwar IITA Sun Horar Da Mata 500 Kasuwancin Noma

by Sani Anwar and Sulaiman
8 months ago
in Labarai
0
IFAD
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ma’aikatar Turai da Harkokin Wajen Faransa tare da hadin gwiwar Cibiyar Kula da Ayyukan Noma ta Duniya (IITA), sun kaddamar da wani shiri na horar da dalibai 500 kan harkokin noma a Kwalejin Aikin Gona ta Audu Bako da ke Danbatta a Jihar Kano.

 

Shirin, wani bangare ne na koyar da fasahar aikin gona da koyar da aikin noma (WATEA), wanda aka shirya shi don agaza wa mata, shi yasa kashi 80 na na masu cin gajiyar shirin ma, mata ne.

  • Majalisar Wakilai Ta Gabatar Da Kudirin Kara Yawan Membobi Daga 360 Zuwa 366
  • Makarantar Nazarin Al’adun Gargajiya Da Wayewar Kai Ta Kasar Sin Dake Athens Za Ta Habaka Musayar Al’adu

Horon, ya kunshi muhimman fannoni da suka hada da kwarewar fasaha, dabarun koyon sana’a da kuma samun tallafin kasuwan a harkar aikin gona.

 

Labarai Masu Nasaba

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

An yi wannan yunkuri ne, domin wadata dalibai da kayan aikin da suka dace; don bunkasa wannan aiki na gona tare kuma da cike guraben da aka rasa na kwarewa, musamman wadanda aka gano.

 

A nata jawabin, Jami’ar Cibiyar Kula da Ayyukan Noma a Jihar Kano (IITA), Hajiya Munnira Jibrin ta bayyana cewa; Gwamnatin Faransa ta kudiri niyyar tallafa wa matasa wajen bunkasa sana’o’i masu matukar muhimmanci, domin samun nasara a harkar noma.

 

Jami’ar ta jaddada cewa, “Wannan horarwa, an samar da ita ne; don tallafa wa mata a harkokin kasuwancinsu,”.

 

Har ila yau, M. Ado Rabo; wakilin shugaban kungiyar ta IITA a Kano, ya bayyana aniyar shirin na samar da dogaro da kai a tsakanin matan da suka halarci taron.

 

“An tsara wannan shiri ne, domin horar da mata sama da maza; ta yadda ba za su dogara da kowa ba, kudirin shi ne; karfafa wa mata a wannan fanni na noma,” in ji Rabo.
Haka zalika, Kwamishinan Ilimi Mai Zurfi; Dakta Yusif Ibrahim Kofar Mata, ya bayyana jin dadinsa dangane da yadda shirin ya mayar da hankali a kan mata.

 

Ya kuma ja hankalin daliban da su yi amfani da wannan dama wajen bunkasa sana’o’insu.
“Gwargwadon yadda kuka rike kasuwancinku, gwargwadon darajar da za ku samu a cikin al’umma”, in ji Kofar mata.

 

AgroNigeria, ta ba da rahoton cewa; fitowar daliban na nuni da cewa, an samu hadin kai; don inganta ilimin aikin gonad a kuma tallafa wa mata a jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sarkin Musulmi Ya Nemi A Daina Tsine Wa Shugabanni

Next Post

An Kaddamar Da Cibiyar ‘Yan Jarida Ta Afirka Masu Amfani Da Harshen Hausa A Nijar

Related

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato
Labarai

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

36 minutes ago
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu
Manyan Labarai

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

2 hours ago
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki
Manyan Labarai

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

13 hours ago
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa
Ilimi

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

14 hours ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

15 hours ago
Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS
Labarai

Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

18 hours ago
Next Post
Faransa

An Kaddamar Da Cibiyar ‘Yan Jarida Ta Afirka Masu Amfani Da Harshen Hausa A Nijar

LABARAI MASU NASABA

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

June 28, 2025
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

June 28, 2025
Hoton Tallan Taliyar Indomie

Indomie Ta Kaddamar Da Shirin Gangamin Abinci Mai Gina Jiki Na ‘Ingantaccen Abinci Domin Nasara’

June 28, 2025
Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

June 27, 2025
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

June 27, 2025
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

June 27, 2025
Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

June 27, 2025
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

June 27, 2025
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

June 27, 2025
Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.