ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Wakilai Ta Gabatar Da Kudirin Kara Yawan Membobi Daga 360 Zuwa 366

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
2 years ago
majalisar kasa

An gabatar da wani kudirin doka da ke da nufin gyara sashe na 49 na kundin tsarin mulkin kasar nan na shekarar 1999, wanda aka yi wa kwaskwarima, domin ware kujeru shida na musamman ga mata da nakasassu a majalisar wakilai.

Wannan shi ne karon farko da aka taba gabatar da irinsa a majalisar wakilai wanda har ya tsallake kaaratu na farko a ranar Laraba da ta gabata.

  • An Gabatar Da Nagartattun Shirye-Shiryen CMG A Brazil
  • Gwamnatin Tarayya Da EU Sun Kulla Yarjejeniyar Bunkasa Wutar Lantarki

Mai magana da yawun majalisar, Akintunde Rotimi (Ekiti, APC) ne ya gabatar da wannan kudiri na neman a kara yawan wakilai a majalisar daga 360 zuwa 366, na karin kujeru shida musamman na mata nakasassu.
A cewar kudurin dokar, za a raba kujerun na musamman a cikin shiyyoyin siyasa shida na Nijeriya, tare da tabbatar da wakilcin mutum daya daga kowace shiyya. Dole ne ‘yan takarar wadannan kujeru su cika dukkan ka’idar da ake bukata don zama mamba a majalisar wakilan Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Za a gudanar da zaben wadannan mukamai ne ta hanyar kwalejin zabe da ta kunshi mambobi daga kungiyoyin nakasassu na kasa, tare da gudunmawa daga matakan kasa da na yanki a cikin tsarin zabe mai yawa.

Da zarar an zabe su, wakilan za su yi wa’adi daya da sauran ‘yan majalisar kuma za su sami alfanu daidai wa daidai kamar yadda kudirin ya bayyana.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Rotimi ya bayyana cewa kudirin dokar na da nufin bunkasa wakilcin mata da nakasassu, wadanda galibi ke fuskantar cikas ga harkokin siyasa.

“Kirkiro wadannan kujeru na musamman zai tabbatar da cewa ana jin muryoyin kungiyoyin da ba su da wakilci a matakin kasa, tare da samar da daidaito da kuma tsarin majalisar dokokin Nijeriya,” in ji shi.
Idan dai za a iya tunawa, shugaban majalisar wakilai, Abbas Tajudeen, a ranar Litinin ya ba da shawarar yin kwaskwarima ga kundin tsarin mulkin kasar na tanadar kujerun majalisar dokoki ga mata da kuma tabbatar da shigar da su cikin mukamai a majalisar zartarwa.

A wani labarin kuma, Cibiyar Nazarin Dokokin Majalisa da Dimokuradiyya ta Kasa (NILDS), ta bayyana wakilcin mata a majalisar dokokin Nijeriya, wanda a halin yanzu bai kai kashi 10% a matsayin abin kunya ba.

Wakiliyar NILDS, Titilayo Daniel ta bayyana hakan ne a jiya a yayin wani taro da aka gudanar a garin Sagamu na Jihar Ogun, inda aka mayar da hankali kan wayar da kan ‘yan majalisar mata mai taken, “Karfafa wakilcin mata a siyasance.”

Da take jawabi ga ‘yan siyasa mata sama da 100, Daniel ta bayyana muhimmancin daidaita jinsi a majalisar dokoki ta kasa. Ta ce, “Mata ba su kai kashi 10 cikin 100 na ‘yan majalisar dokoki ta kasa ba, ma’ana cewa sama da rabin al’ummarmu ba sa cikin masu yanke hukunci. Wannan kididdigar abin kunya ce ga Nijeriya idan aka kwatanta da sauran kasashen Afirka kamar Rwanda, wacce ke da kashi 61.3% na wakilai.”

Daniel ta kara da cewa matan Nijeriya na ci gaba da fuskantar cikas da dama ga shiga harkokin siyasa, tana mai nuni da cewa tsarin majalisar dokokin na nuna san kai.

majalisa
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027
majalisa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
Next Post
Me Ya Sa Kamfanonin Waje Masu Yawa Suka Fara Nuna Sabbin Kayayyakinsu A CIIE?

Me Ya Sa Kamfanonin Waje Masu Yawa Suka Fara Nuna Sabbin Kayayyakinsu A CIIE?

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.