ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Wakilai Ta Gabatar Da Kudirin Kara Yawan Membobi Daga 360 Zuwa 366

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
2 years ago
majalisar kasa

An gabatar da wani kudirin doka da ke da nufin gyara sashe na 49 na kundin tsarin mulkin kasar nan na shekarar 1999, wanda aka yi wa kwaskwarima, domin ware kujeru shida na musamman ga mata da nakasassu a majalisar wakilai.

Wannan shi ne karon farko da aka taba gabatar da irinsa a majalisar wakilai wanda har ya tsallake kaaratu na farko a ranar Laraba da ta gabata.

  • An Gabatar Da Nagartattun Shirye-Shiryen CMG A Brazil
  • Gwamnatin Tarayya Da EU Sun Kulla Yarjejeniyar Bunkasa Wutar Lantarki

Mai magana da yawun majalisar, Akintunde Rotimi (Ekiti, APC) ne ya gabatar da wannan kudiri na neman a kara yawan wakilai a majalisar daga 360 zuwa 366, na karin kujeru shida musamman na mata nakasassu.
A cewar kudurin dokar, za a raba kujerun na musamman a cikin shiyyoyin siyasa shida na Nijeriya, tare da tabbatar da wakilcin mutum daya daga kowace shiyya. Dole ne ‘yan takarar wadannan kujeru su cika dukkan ka’idar da ake bukata don zama mamba a majalisar wakilan Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Za a gudanar da zaben wadannan mukamai ne ta hanyar kwalejin zabe da ta kunshi mambobi daga kungiyoyin nakasassu na kasa, tare da gudunmawa daga matakan kasa da na yanki a cikin tsarin zabe mai yawa.

Da zarar an zabe su, wakilan za su yi wa’adi daya da sauran ‘yan majalisar kuma za su sami alfanu daidai wa daidai kamar yadda kudirin ya bayyana.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Rotimi ya bayyana cewa kudirin dokar na da nufin bunkasa wakilcin mata da nakasassu, wadanda galibi ke fuskantar cikas ga harkokin siyasa.

“Kirkiro wadannan kujeru na musamman zai tabbatar da cewa ana jin muryoyin kungiyoyin da ba su da wakilci a matakin kasa, tare da samar da daidaito da kuma tsarin majalisar dokokin Nijeriya,” in ji shi.
Idan dai za a iya tunawa, shugaban majalisar wakilai, Abbas Tajudeen, a ranar Litinin ya ba da shawarar yin kwaskwarima ga kundin tsarin mulkin kasar na tanadar kujerun majalisar dokoki ga mata da kuma tabbatar da shigar da su cikin mukamai a majalisar zartarwa.

A wani labarin kuma, Cibiyar Nazarin Dokokin Majalisa da Dimokuradiyya ta Kasa (NILDS), ta bayyana wakilcin mata a majalisar dokokin Nijeriya, wanda a halin yanzu bai kai kashi 10% a matsayin abin kunya ba.

Wakiliyar NILDS, Titilayo Daniel ta bayyana hakan ne a jiya a yayin wani taro da aka gudanar a garin Sagamu na Jihar Ogun, inda aka mayar da hankali kan wayar da kan ‘yan majalisar mata mai taken, “Karfafa wakilcin mata a siyasance.”

Da take jawabi ga ‘yan siyasa mata sama da 100, Daniel ta bayyana muhimmancin daidaita jinsi a majalisar dokoki ta kasa. Ta ce, “Mata ba su kai kashi 10 cikin 100 na ‘yan majalisar dokoki ta kasa ba, ma’ana cewa sama da rabin al’ummarmu ba sa cikin masu yanke hukunci. Wannan kididdigar abin kunya ce ga Nijeriya idan aka kwatanta da sauran kasashen Afirka kamar Rwanda, wacce ke da kashi 61.3% na wakilai.”

Daniel ta kara da cewa matan Nijeriya na ci gaba da fuskantar cikas da dama ga shiga harkokin siyasa, tana mai nuni da cewa tsarin majalisar dokokin na nuna san kai.

majalisa
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
majalisa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara
  • Sulaiman
    Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta
  • Sulaiman
    Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita
  • Sulaiman
    Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
Me Ya Sa Kamfanonin Waje Masu Yawa Suka Fara Nuna Sabbin Kayayyakinsu A CIIE?

Me Ya Sa Kamfanonin Waje Masu Yawa Suka Fara Nuna Sabbin Kayayyakinsu A CIIE?

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

June 25, 2026
Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

June 25, 2026
Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.