• English
  • Business News
Monday, October 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ofishin Jakadancin Kasar Sin Dake Najeriya Ya Shirya Bikin Murnar Cikar Sin Shekaru 74 Da Kafuwa

by CGTN Hausa
2 years ago
Kasar Sin

A kwanan nan ne, ofisoshin jakadancin kasar Sin dake kasashen waje da dama, suka gudanar da bukukuwa iri-iri, domin murnar cika shekaru 74, da kafuwar Jamhuriyar Jama’ar kasar Sin.

A wajen irin wannan bikin da ofishin jakadancin Sin dake tarayyar Najeriya ya shirya, jakadan Sin a kasar Cui Jianchun, ya yi waiwaye game da yadda Jamhuriyar Jama’ar kasar Sin ta samu ci gaba, da nasarori a shekaru 74 da suka gabata, inda ya jaddada cewa, tun bayan da kasashen biyu suka kulla alakar jakadanci a shekara ta 1971, musamman bayan da suka daga matsayin alakar su, zuwa alakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare a shekara ta 2005, ya zuwa yanzu, hadin-gwiwarsu na kan gaba sosai.

  • Sin Tana Bayar Da Babbar Gudummawa Ga Gina Al’ummar Duniya Mai Makomar Bai Daya
  • Da Dumi-dumi: Kotu Ta Kori Karar Da ADC Ke Yi Kan Gwamnan Gombe

Jakada Cui ya kara da cewa, kasar Sin na fatan yin amfani da damar gudanar da babban dandalin tattauna hadin-gwiwar kasa da kasa kan shawarar “ziri daya da hanya daya” karo na uku, gami da dandalin tattauna hadin-kan Sin da Afirka wato FOCAC a takaice, domin taimakawa ci gaban manufar raya Sin da Najeriya, wadda ake kira 5GIST, da kara habaka hadin-gwiwarsu.

Shi ma a nasa jawabin, mataimakin kakakin majalisar wakilan tarayyar Najeriya Benjamin Kalu, ya taya Jamhuriyar Jama’ar kasar Sin murnar cika shekaru 74 da kafuwa, inda a cewarsa, Sin babbar aminiyar hadin-gwiwa ce ga Najeriya, kuma kasashen biyu sun cimma tudun-dafawa, wajen karfafa hadin-gwiwa, a fannonin da suka shafi samar da muhimman ababen more rayuwar al’umma, da kasuwanci, da musanyar fasahohi, da al’adu da sauransu, al’amarin da ya taimaka matuka ga ci gaban rayuwar al’umma, gami da bunkasar tattalin arzikin Najeriya, da samar mata da dimbin guraban ayyukan yi, da taimakawa ci gaban sana’o’i daban-daban.

Jami’in ya ce, kasar Sin ta dade da yin kira, da a aiwatar da ra’ayin cudanyar bangarori daban-daban a duniya, da samar da ci gaba mai dorewa kuma cikin lumana, kana ta taka muhimmiyar rawa a harkokin duniya.

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Tsakiyar JKS Na 20 A Beijing

Alkaluman GDP Na Sin Sun Fadada Zuwa Kaso 5.2 A Watanni 9 Na Farkon Bana

Daga nan sai ya bayyana fatansa, ga fadadar zumuncin kasashen biyu, da kara samar da damammaki, da alfanu ga al’ummunsu baki daya, da bayar da gudummawa ga shimfida zaman lafiya, da ci gaba a duk fadin duniya. (Murtala Zhang)

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Gudanar Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Tsakiyar JKS Na 20 A Beijing
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Tsakiyar JKS Na 20 A Beijing

October 20, 2025
Alkaluman GDP Na Sin Sun Fadada Zuwa Kaso 5.2 A Watanni 9 Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Alkaluman GDP Na Sin Sun Fadada Zuwa Kaso 5.2 A Watanni 9 Na Farkon Bana

October 20, 2025
Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

October 19, 2025
Next Post
BUA

Daga Gobe 2 Ga Oktoba Farashin Buhun Simintin BUA Ya Koma N3,500 - Kamfanin

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Tsakiyar JKS Na 20 A Beijing

An Gudanar Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Tsakiyar JKS Na 20 A Beijing

October 20, 2025
Gwamna Lawal Ya Jaddada Muhimmancin Haɗin Kai Wajen Yaƙi Da Ƙalubalen Tsaro

Gwamna Lawal Ya Jaddada Muhimmancin Haɗin Kai Wajen Yaƙi Da Ƙalubalen Tsaro

October 20, 2025
Alkaluman GDP Na Sin Sun Fadada Zuwa Kaso 5.2 A Watanni 9 Na Farkon Bana

Alkaluman GDP Na Sin Sun Fadada Zuwa Kaso 5.2 A Watanni 9 Na Farkon Bana

October 20, 2025
Morocco Ta Lashe Kofin Duniya Na Ƴan Ƙasa Da Shekara 20 Karo Na Farko A Tarihinta

Morocco Ta Lashe Kofin Duniya Na Ƴan Ƙasa Da Shekara 20 Karo Na Farko A Tarihinta

October 20, 2025
Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

October 20, 2025
Kotu Ta Yanke Hukuncin Kisa Ga Mutane Biyu Da Suka Kashe Malamin Jami’a

Kotu Ta Yanke Hukuncin Kisa Ga Mutane Biyu Da Suka Kashe Malamin Jami’a

October 20, 2025
Hukumar EFCC Ta Tsare Wasu Jami’anta 10 Bisa Zargin Karkatar Da Kayan Aiki

EFCC Ta Ƙwato Kadarorin Naira Biliyan 500 A Ƙarƙashin Gwamnatin Tinubu – Shettima

October 20, 2025
Kano Pillars Ta Dakatar Da Manyan Masu Horas Da ‘Yan Wasanta Saboda Rashin Nasara

Kano Pillars Ta Dakatar Da Manyan Masu Horas Da ‘Yan Wasanta Saboda Rashin Nasara

October 20, 2025
Bayan Kauce Hanya, Jirgi Ya Afka Cikin Teku A Hong Kong 

Bayan Kauce Hanya, Jirgi Ya Afka Cikin Teku A Hong Kong 

October 20, 2025
Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow A Abuja

Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow A Abuja

October 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.