• English
  • Business News
Monday, July 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daga Gobe 2 Ga Oktoba Farashin Buhun Simintin BUA Ya Koma N3,500 – Kamfanin

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Manyan Labarai
0
BUA
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Gudanarwar Kamfanin Siminti na BUA, ta sanar da cewa, daga ranar 2 ga watan Oktoba farashin buhun siminti zai koma naira dubu uku da dari biyar (N3,500).

Don haka, yanzu kamfanin zai fara sayar da buhun Siminti kan naira N3,500 sabanin yadda ake sayarwa a baya kan naira dubu N5,000 a wasu wurin ma har zuwa N5,500.

  • Ta Ina Talakawa Za Su Mori Rage Farashin Simintin BUA?
  • Kamfanin BUA Ya Tallafawa Asibitoci 15 A Sakkwato

A cewar kamfanin, wannan wani mataki ne na saukaka wa ‘yan Nijeriya samun damar yin gine-gine da kuma saukaka farashin kayan gini. Inda kamfanin ya ce, akwai wani sabon albishiri da zarar an kammala aikin sabbin layukan da kamfanin ke yi a halin yanzu, zuwa sabuwar shekara, kamfanin zai sake duba yiyuwar rage farashin.

A cewar sanarwar: “Dangane da bayanin da muka fitar a baya na niyyar da muke da shi na rage farashin siminti da zarar mun kammala bude sabbin layukanmu a karshen shekara, domin bunkasa kayan gini da sashin gine-gine.

“A cikin yunkurinmu na rage farashin kayayyakinmu da sake nazartar ayyukanmu lokaci zuwa lokaci, hukumar gudanarwa ta kamfanin BUA tana sanar da abokan cinikayyarta da masu ruwa da tsaki hadi da al’umma cewa daga ranar 2 ga watan Oktoban 2023, mun cimma matsayar rage farashin.

Labarai Masu Nasaba

Ranar Talata Mai Zuwa Zan Koma Zauren Majalisar Dattawa – Sanata Natasha

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

“A kan hakan, daga yanzu za a sayar da buhun simintin BUA ne a kan kudi naira 3,500 domin ‘yan Nijeriya su fara cin gajiyar farashin kafin mu kammala tsare-tsarenmu.”

A cewar sanarwar, wani karin tagomashi ma shi ne, dukkanin wadanda suka yi odar sayo simintin a kan tsohon farashi a halin yanzu, za a duba a maida shi zuwa naira 3,500 a bisa tsarin sabon farashin da zai fara aiki daga ranar 2 ga Oktoba.

Kamfanin ya shawarci dillalanta da su tabbatar jama’a sun amfana da wannan sabon farashin kuma kamfanin zai sanya Ido wajen ganin an bi umarnin amfani da sabon farashin ba tare da tangarda ba.

Idan za a iya tunawa dai Shugaban rukunin kamfanin BUA, Abdul-Samad Rabiu, a kwanain baya lokacin da ya ziyarci shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu, ya sanar da cewa, kamfanin ya shirya tsaf domin rage farashin Siminti a Nijeriya zuwa naira N3,500 ko ma kasa da haka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BUADangoteSiminti
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ofishin Jakadancin Kasar Sin Dake Najeriya Ya Shirya Bikin Murnar Cikar Sin Shekaru 74 Da Kafuwa

Next Post

Shugaban Syria: Manyan Tsare-tsare Uku Na duniya Su Ne Jagororin Sabuwar Duniya

Related

Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Ranar Talata Mai Zuwa Zan Koma Zauren Majalisar Dattawa – Sanata Natasha

9 hours ago
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC
Manyan Labarai

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

1 day ago
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

1 day ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

2 days ago
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

2 days ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

2 days ago
Next Post
Syria

Shugaban Syria: Manyan Tsare-tsare Uku Na duniya Su Ne Jagororin Sabuwar Duniya

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

July 6, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

July 6, 2025
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

July 6, 2025
Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

July 6, 2025
Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

July 6, 2025
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

July 6, 2025
Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

July 6, 2025
Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

July 6, 2025
Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

July 6, 2025
Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

July 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.