ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 19, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daga Gobe 2 Ga Oktoba Farashin Buhun Simintin BUA Ya Koma N3,500 – Kamfanin

by Khalid Idris Doya
3 years ago
BUA

Hukumar Gudanarwar Kamfanin Siminti na BUA, ta sanar da cewa, daga ranar 2 ga watan Oktoba farashin buhun siminti zai koma naira dubu uku da dari biyar (N3,500).

Don haka, yanzu kamfanin zai fara sayar da buhun Siminti kan naira N3,500 sabanin yadda ake sayarwa a baya kan naira dubu N5,000 a wasu wurin ma har zuwa N5,500.

  • Ta Ina Talakawa Za Su Mori Rage Farashin Simintin BUA?
  • Kamfanin BUA Ya Tallafawa Asibitoci 15 A Sakkwato

A cewar kamfanin, wannan wani mataki ne na saukaka wa ‘yan Nijeriya samun damar yin gine-gine da kuma saukaka farashin kayan gini. Inda kamfanin ya ce, akwai wani sabon albishiri da zarar an kammala aikin sabbin layukan da kamfanin ke yi a halin yanzu, zuwa sabuwar shekara, kamfanin zai sake duba yiyuwar rage farashin.

ADVERTISEMENT

A cewar sanarwar: “Dangane da bayanin da muka fitar a baya na niyyar da muke da shi na rage farashin siminti da zarar mun kammala bude sabbin layukanmu a karshen shekara, domin bunkasa kayan gini da sashin gine-gine.

“A cikin yunkurinmu na rage farashin kayayyakinmu da sake nazartar ayyukanmu lokaci zuwa lokaci, hukumar gudanarwa ta kamfanin BUA tana sanar da abokan cinikayyarta da masu ruwa da tsaki hadi da al’umma cewa daga ranar 2 ga watan Oktoban 2023, mun cimma matsayar rage farashin.

LABARAI MASU NASABA

Hisbah Ta Kama Maza Da Mata 16 A Samamen Dare Kan Zargin Ayyukan Lalata A Kano

Sarkin Kano Sanusi II Ya Ce Tsauraran Sharuɗɗan Beli Ne Ke Jinkirta Sakin El-Rufai

“A kan hakan, daga yanzu za a sayar da buhun simintin BUA ne a kan kudi naira 3,500 domin ‘yan Nijeriya su fara cin gajiyar farashin kafin mu kammala tsare-tsarenmu.”

A cewar sanarwar, wani karin tagomashi ma shi ne, dukkanin wadanda suka yi odar sayo simintin a kan tsohon farashi a halin yanzu, za a duba a maida shi zuwa naira 3,500 a bisa tsarin sabon farashin da zai fara aiki daga ranar 2 ga Oktoba.

Kamfanin ya shawarci dillalanta da su tabbatar jama’a sun amfana da wannan sabon farashin kuma kamfanin zai sanya Ido wajen ganin an bi umarnin amfani da sabon farashin ba tare da tangarda ba.

Idan za a iya tunawa dai Shugaban rukunin kamfanin BUA, Abdul-Samad Rabiu, a kwanain baya lokacin da ya ziyarci shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu, ya sanar da cewa, kamfanin ya shirya tsaf domin rage farashin Siminti a Nijeriya zuwa naira N3,500 ko ma kasa da haka.

BUA
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

MASU ALAKA

Hisbah Ta Kama Maza Da Mata 16 A Samamen Dare Kan Zargin Ayyukan Lalata A Kano
Manyan Labarai

Hisbah Ta Kama Maza Da Mata 16 A Samamen Dare Kan Zargin Ayyukan Lalata A Kano

June 18, 2026
CBN
Manyan Labarai

Sarkin Kano Sanusi II Ya Ce Tsauraran Sharuɗɗan Beli Ne Ke Jinkirta Sakin El-Rufai

June 18, 2026
Kotu A Birtaniya Ta Wanke Diezani Daga Zargin Cin Hanci
Manyan Labarai

Kotu A Birtaniya Ta Wanke Diezani Daga Zargin Cin Hanci

June 18, 2026
Next Post
Syria

Shugaban Syria: Manyan Tsare-tsare Uku Na duniya Su Ne Jagororin Sabuwar Duniya

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN Ya Nuna Yadda Cimma Yarjejeniya Tsakanin Amurka Da Iran Ta Fallasa Koma Bayan Tasirin Amurka A Harkokin Duniya

Binciken CGTN Ya Nuna Yadda Cimma Yarjejeniya Tsakanin Amurka Da Iran Ta Fallasa Koma Bayan Tasirin Amurka A Harkokin Duniya

June 18, 2026
Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

June 18, 2026
Kasar Sin: Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Fahimtar Juna Tsakanin Amurka Da Iran A Matakin Farko Na Da Matukar Muhimmanci

Kasar Sin: Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Fahimtar Juna Tsakanin Amurka Da Iran A Matakin Farko Na Da Matukar Muhimmanci

June 18, 2026
Tinubu

Rashin Tsaro: CUPP Ta Goyi Bayan Kiran Da Aka Yi Wa Tinubu Na Jagoranci Ko Murabus

June 18, 2026
Sakon Kasar Sin Game Da Ingiza Tsarin Jagorancin Kare Hakkin Bil’adama 

Sakon Kasar Sin Game Da Ingiza Tsarin Jagorancin Kare Hakkin Bil’adama 

June 18, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Wakiliyar Kasar Sin Ta Bayyana Matsayin Kasar A Gun Taron Majalisar Hakkin Dan Adam Ta MDD

Wakiliyar Kasar Sin Ta Bayyana Matsayin Kasar A Gun Taron Majalisar Hakkin Dan Adam Ta MDD

June 18, 2026
Hisbah Ta Kama Maza Da Mata 16 A Samamen Dare Kan Zargin Ayyukan Lalata A Kano

Hisbah Ta Kama Maza Da Mata 16 A Samamen Dare Kan Zargin Ayyukan Lalata A Kano

June 18, 2026
Wakilin Sin Ya Fayyace Matsayin Kasar Game Da Yadda Wasu Kasashe Ke Tada Hankali Kan “Hukuncin Shari’ar Tekun Kudancin Sin”

Wakilin Sin Ya Fayyace Matsayin Kasar Game Da Yadda Wasu Kasashe Ke Tada Hankali Kan “Hukuncin Shari’ar Tekun Kudancin Sin”

June 18, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Iran Ta Ce Shirinta Na Makamai Masu Linzami Ba Ya Cikin Tattaunawa Da Amurka

June 18, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.