ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Tana Bayar Da Babbar Gudummawa Ga Gina Al’ummar Duniya Mai Makomar Bai Daya

by CGTN Hausa
3 years ago
sin

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Takardar bayanin ta yi nuni da cewa, shawarar “ziri daya da hanya daya” wani kyakkyawan misali ne na gina al’ummar duniya mai makomar bai daya, kuma wani dandali ne na amfanar jama’ar duniya da yin hadin gwiwa da kasar Sin ta samar wa duniya.

A cewar takardar, ya zuwa watan Yuli na shekarar 2023, fiye da kashi 3 bisa 4 na kasashen duniya da kungiyoyin kasa da kasa sama da 30, sun sanya hannu kan yarjejeniyoyin hadin gwiwar shawarar “ziri daya da hanya daya” da kasar Sin.
Takardar ta kara da cewa, shawarar raya kasa ta duniya, da shawarar samar da tsaro ta duniya, da shawarar wayewar kai da kasar Sin ta gabatar, duk sun zama wani muhimmin ginshiki na gina al’ummar duniya mai makomar bai daya.
Kasar Sin ta gabatar da shawarar gina al’ummar duniya mai makomar bai daya, tare da yin kira ga dukkan kasashen duniya, da su samar da kyakkyawar fahimtar juna, da daukar matakan da suka dace, don tinkarar batutuwan da suka shafi duniya, ta yadda za a karfafa gwiwa da himma ga yunkurin dan Adam na samun kyakkyawar makoma.

  • Xi Ya Yi Kira Ga Lardin Zhejiang Da Ya Rubuta Sabon Babi Na Inganta Zamanantarwa Ta Sin
  • Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Taimakawa Al’ummar Libya Wajen Yakar Bala’in Ambaliyar Ruwa

Takardar bayanin ta kara da cewa, bisa zurfin tunani, kasar Sin ta fahimci cewa, mabambantan al’adu suna da mabambantan fahimtar yanayin wadannan dabi’u, tana kuma mutunta kokarin da jama’ar kasashe daban-daban suke yi na nazarin hanyoyin ci gaban da ya dace da yanayin kasashensu.
Game da wannan takardar bayani, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Wang Wenbin ya jaddada a wajen taron manema labarai da aka yi a yau cewa, yana fatan takardar bayanin za ta taimaka wa mutane daga bangarori daban-daban da kasa da kasa wajen kara fahimtar ma’anar al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya, da kara sanin babban burin harkokin diflomasiyya masu salon musamman na kasar ta Sin.
Jami’in ya ce, kasar Sin ce ta bada shawara gami da daukar matakai na zahiri, a fannin raya shawarar “ziri daya da hanya daya”, da bullowa gami da aiwatar da shawarwarin da suka shafi ci gaba da tsaro da wayewar kai na duniya, da kara hada kai tare da kasashe da yankuna daban-daban don gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya.

ADVERTISEMENT

Jami’in ya kara da cewa, kawo yanzu, akwai wakilai daga kasashe sama da 130 da suka tabbatar da cewa za su halarci babban dandalin tattaunawa na hadin-gwiwar kasa da kasa kan shawarar “ziri daya da hanya daya” karo na uku, yayin da wakilai na kungiyoyin kasa da kasa da dama su ma suka tabbatar da halartarsu. (Masu Fassarawa: Ibrahim Yaya, Murtala Zhang)

sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

MASU ALAKA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
Daga Birnin Sin

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
Daga Birnin Sin

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
Daga Birnin Sin

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Next Post
Juan Antonio Samaranch Jr.: Shugaba Xi Muhimmin Abokin Tafiya Ne Na Gasar Olympic

Juan Antonio Samaranch Jr.: Shugaba Xi Muhimmin Abokin Tafiya Ne Na Gasar Olympic

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.