• English
  • Business News
Thursday, June 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Okowa Ya Karbi Wadanda Suka Nemi Takarar Gwamnan APC Uku Da Suka Koma PDP A Sakkwato 

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
3 years ago
in Siyasa
0
Okowa Ya Karbi Wadanda Suka Nemi Takarar Gwamnan APC Uku Da Suka Koma PDP A Sakkwato 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mataimakin Dan Takarar Shugaban Kasa a Jam’iyyar Adawa, PDP a zaben 2023, Ifeanyi Okowa, ya jagoranci karbar manyan jiga-jigan jam’iyyar APC da suka sauya sheka zuwa PDP a Sakkwato tare da bayyana cewar lokaci ya yi da za su ceto Nijeriya daga halin da APC ta jefa ta. 

Mataimakin na Atiku Abubakar a 2023, ya jaddada cewar canza shekar fitattun ‘yan siyasar daga jam’iyyar da ke mulkin kasa zuwa jam’iyyar adawa a karkashin jagorancin, gwamna jihar Aminu Waziri Tambuwal, babbar alama ce ta samun nasarar PDP kamar yadda ya bayyana a yammacin ranar Lahadi a Sakkwato.

  • Shugaba Xi Ya Jaddada Muhimmancin Jin Ra’ayoyin Jama’a Ta Hanyoyi Daban-Daban
  • Zargin Cire Sashen Jikin Yaro: Jami’ar Lincoln Ta Dakatar Da Ekweremadu

Ya ce a shekara mai zuwa mulkin Nijeriya zai koma a hannun jam’iyyar PDP wadda za ta kawar da matsalolin al’umma da inganta jin dadinsu.

Kana ya ce PDP za ta dawo da kima da martabar Nijeriya a idanun duniya.

Ya ce a yanzu lokaci ne na ceto Nijeriya kuma lokacin sake gina kasa, don haka ya zama wajibi a yi aiki tare domin kubutar da Nijeriya daga hannun wadanda ke kokarin ruguza ta.

Labarai Masu Nasaba

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

“Mun yadda da Nijeriya a matsayin kasa daya al’umma daya akasin wasu ‘yan takarar da ko kadan ba su yadda da ci gaba da dorewar kasar nan a matsayin kasa daya ba.

“Ya bayyana tare da cewar a bisa ga kwarewa da gogewa da sanin makamar shugabancin da Atiku Abubakar yake da ita zai jagoranci mulkin da kowa zai yaba a Nijeriya.”

Kusoshin ‘yan siyasar wadanda fitar su ta girgiza APC tare da karya lagonta a Jihar sun hada da uku daga cikin wadanda suka tsayawa jam’iyyar takarar fidda gwani na zaben gwamna, wato tsohon Ministan Wasanni kana Daraktan yakin neman zaben Buhari a 2019 a Sakkkwato, Yusuf Sulaiman, Shugaban Kwamitin Yaki da Fatara a Majalisar Wakilai, Hon. Abdullahi Salame da A.A Gumbi.

Haka ma akwai Kakakin Majalisar Dokoki ta Jihar Sakkwato, Hon. Aminu Achida da tsohon Ministan Al’adu, Sanata Bello Jibril Gada da kuma Hon. Yusuf Kurdula wanda ke wakiltar Tangaza/Gudu a Majalisar Wakilai.

Sauran sun hada da Hon. Murtala Maigona, wanda ke wakiltar Karamar Hukumar Wamakko a Majalisar Dokoki ta Jiha da tsofaffin shugabannin kananan hukumomin Sakkwato ta Arewa da Binji, Abdullahi Hassan da Sayyadi Nuhu Binji da tsofaffin kwamishinoni Aminu Bello Sokoto da Dahiru Maishanu Yabo.

Sai Mataimaki na Musamman ga Sanata Aliyu Wamakko kan Yada Labarai, Hassan Sahabi Sanyinnawal, da Yahaya Dallatu da ‘yan siyasa, ‘yan kasuwa, ‘yan kwangila da dubban daruruwan magoya bayansu.

A jawabinsa, tsohon Ministan Wasanni, Yusuf Sulaiman, ya bayyana cewar canza shekarsu daga APC zuwa PDP abin murna ne kuma za su jajirce domin ganin PDP ta samu nasarar kafa gwamnati daga sama har kasa baki daya.

Ya ce 2023 lokaci ne da jam’iyyar PDP za ta sake komawa fadar mulkin kasa.

Gwamna Aminu Waziri Tambuwal a takaitaccen jawabinsa, ya bayyana cewar a bisa ga kasawar APC na magance matsalolin da suka dabaibaye Nijeriya, wajibi ne a 2023 al’umma su zabi PDP domin kai kasar nan a tudun mun tsira.

Ya ce APC ba ta da tsari da cancantar da za ta kawar da matsalolin ‘yan Nijeriya.

Ya ce sakon da fitar manyan ‘yan siyasar ke nunawa a bayyane yake na kyakkyawar makoma da ke a gaban PDP wadda ya ce ba za ta yi kasa a guiwa ba wajen shimfida ingantaccen mulki na gari wanda ‘yan Nijeriya za su yaba a karkashin jagorancin Wazirin Adamawa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCAtiku AbubakarOkowaPDPSakkwatoSauya ShekaTambuwalZaben 2023
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaba Xi Ya Jaddada Muhimmancin Jin Ra’ayoyin Jama’a Ta Hanyoyi Daban-Daban

Next Post

Har Yanzu Ina Neman Abokin Takara — Tinubu

Related

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki
Manyan Labarai

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

2 days ago
Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike
Siyasa

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

3 days ago
Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya
Siyasa

Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

6 days ago
‘Aikin Yan Uba Ne’ — Yahaya Bello Ya Karyata Zargin Sha’awar Takarar Shugaban Kasa A 2027
Siyasa

‘Aikin Yan Uba Ne’ — Yahaya Bello Ya Karyata Zargin Sha’awar Takarar Shugaban Kasa A 2027

2 weeks ago
Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi
Labarai

Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi

2 weeks ago
PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe
Siyasa

PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

3 weeks ago
Next Post
Har Yanzu Ina Neman Abokin Takara — Tinubu

Har Yanzu Ina Neman Abokin Takara — Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

June 4, 2025
Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

June 4, 2025
Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba

Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba

June 4, 2025
Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

June 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

June 4, 2025
Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

June 4, 2025
Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

June 4, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

June 4, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

June 4, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

Mutum 7 Sun Rasu Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Sakkwato 

June 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.