ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Okowa Ya Karbi Wadanda Suka Nemi Takarar Gwamnan APC Uku Da Suka Koma PDP A Sakkwato 

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
4 years ago
PDP

Mataimakin Dan Takarar Shugaban Kasa a Jam’iyyar Adawa, PDP a zaben 2023, Ifeanyi Okowa, ya jagoranci karbar manyan jiga-jigan jam’iyyar APC da suka sauya sheka zuwa PDP a Sakkwato tare da bayyana cewar lokaci ya yi da za su ceto Nijeriya daga halin da APC ta jefa ta. 

Mataimakin na Atiku Abubakar a 2023, ya jaddada cewar canza shekar fitattun ‘yan siyasar daga jam’iyyar da ke mulkin kasa zuwa jam’iyyar adawa a karkashin jagorancin, gwamna jihar Aminu Waziri Tambuwal, babbar alama ce ta samun nasarar PDP kamar yadda ya bayyana a yammacin ranar Lahadi a Sakkwato.

  • Shugaba Xi Ya Jaddada Muhimmancin Jin Ra’ayoyin Jama’a Ta Hanyoyi Daban-Daban
  • Zargin Cire Sashen Jikin Yaro: Jami’ar Lincoln Ta Dakatar Da Ekweremadu

Ya ce a shekara mai zuwa mulkin Nijeriya zai koma a hannun jam’iyyar PDP wadda za ta kawar da matsalolin al’umma da inganta jin dadinsu.

ADVERTISEMENT

Kana ya ce PDP za ta dawo da kima da martabar Nijeriya a idanun duniya.

Ya ce a yanzu lokaci ne na ceto Nijeriya kuma lokacin sake gina kasa, don haka ya zama wajibi a yi aiki tare domin kubutar da Nijeriya daga hannun wadanda ke kokarin ruguza ta.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

“Mun yadda da Nijeriya a matsayin kasa daya al’umma daya akasin wasu ‘yan takarar da ko kadan ba su yadda da ci gaba da dorewar kasar nan a matsayin kasa daya ba.

“Ya bayyana tare da cewar a bisa ga kwarewa da gogewa da sanin makamar shugabancin da Atiku Abubakar yake da ita zai jagoranci mulkin da kowa zai yaba a Nijeriya.”

Kusoshin ‘yan siyasar wadanda fitar su ta girgiza APC tare da karya lagonta a Jihar sun hada da uku daga cikin wadanda suka tsayawa jam’iyyar takarar fidda gwani na zaben gwamna, wato tsohon Ministan Wasanni kana Daraktan yakin neman zaben Buhari a 2019 a Sakkkwato, Yusuf Sulaiman, Shugaban Kwamitin Yaki da Fatara a Majalisar Wakilai, Hon. Abdullahi Salame da A.A Gumbi.

Haka ma akwai Kakakin Majalisar Dokoki ta Jihar Sakkwato, Hon. Aminu Achida da tsohon Ministan Al’adu, Sanata Bello Jibril Gada da kuma Hon. Yusuf Kurdula wanda ke wakiltar Tangaza/Gudu a Majalisar Wakilai.

Sauran sun hada da Hon. Murtala Maigona, wanda ke wakiltar Karamar Hukumar Wamakko a Majalisar Dokoki ta Jiha da tsofaffin shugabannin kananan hukumomin Sakkwato ta Arewa da Binji, Abdullahi Hassan da Sayyadi Nuhu Binji da tsofaffin kwamishinoni Aminu Bello Sokoto da Dahiru Maishanu Yabo.

Sai Mataimaki na Musamman ga Sanata Aliyu Wamakko kan Yada Labarai, Hassan Sahabi Sanyinnawal, da Yahaya Dallatu da ‘yan siyasa, ‘yan kasuwa, ‘yan kwangila da dubban daruruwan magoya bayansu.

A jawabinsa, tsohon Ministan Wasanni, Yusuf Sulaiman, ya bayyana cewar canza shekarsu daga APC zuwa PDP abin murna ne kuma za su jajirce domin ganin PDP ta samu nasarar kafa gwamnati daga sama har kasa baki daya.

Ya ce 2023 lokaci ne da jam’iyyar PDP za ta sake komawa fadar mulkin kasa.

Gwamna Aminu Waziri Tambuwal a takaitaccen jawabinsa, ya bayyana cewar a bisa ga kasawar APC na magance matsalolin da suka dabaibaye Nijeriya, wajibi ne a 2023 al’umma su zabi PDP domin kai kasar nan a tudun mun tsira.

Ya ce APC ba ta da tsari da cancantar da za ta kawar da matsalolin ‘yan Nijeriya.

Ya ce sakon da fitar manyan ‘yan siyasar ke nunawa a bayyane yake na kyakkyawar makoma da ke a gaban PDP wadda ya ce ba za ta yi kasa a guiwa ba wajen shimfida ingantaccen mulki na gari wanda ‘yan Nijeriya za su yaba a karkashin jagorancin Wazirin Adamawa.

PDP
Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
+ postsBio
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    A Yayin Da Babban Bankin Ƙasa (CBN) Ke Yaƙi Da Laifukan Intanet
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Halin Da Matsalar Tsaro Ta Jefa ‘Yan Gudun Hijira A Arerwacin Nijeriya
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Sanata Tambuwal Ya Sadaukar Da Takararsa Ga Faruku Yabo
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Dan-Iya Ya Zama Ɗan Takarar Gwamnan ADC A Sakkwato

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Har Yanzu Ina Neman Abokin Takara — Tinubu

Har Yanzu Ina Neman Abokin Takara — Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.