ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Okowa Ya Karbi Wadanda Suka Nemi Takarar Gwamnan APC Uku Da Suka Koma PDP A Sakkwato 

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
4 years ago
PDP

Mataimakin Dan Takarar Shugaban Kasa a Jam’iyyar Adawa, PDP a zaben 2023, Ifeanyi Okowa, ya jagoranci karbar manyan jiga-jigan jam’iyyar APC da suka sauya sheka zuwa PDP a Sakkwato tare da bayyana cewar lokaci ya yi da za su ceto Nijeriya daga halin da APC ta jefa ta. 

Mataimakin na Atiku Abubakar a 2023, ya jaddada cewar canza shekar fitattun ‘yan siyasar daga jam’iyyar da ke mulkin kasa zuwa jam’iyyar adawa a karkashin jagorancin, gwamna jihar Aminu Waziri Tambuwal, babbar alama ce ta samun nasarar PDP kamar yadda ya bayyana a yammacin ranar Lahadi a Sakkwato.

  • Shugaba Xi Ya Jaddada Muhimmancin Jin Ra’ayoyin Jama’a Ta Hanyoyi Daban-Daban
  • Zargin Cire Sashen Jikin Yaro: Jami’ar Lincoln Ta Dakatar Da Ekweremadu

Ya ce a shekara mai zuwa mulkin Nijeriya zai koma a hannun jam’iyyar PDP wadda za ta kawar da matsalolin al’umma da inganta jin dadinsu.

ADVERTISEMENT

Kana ya ce PDP za ta dawo da kima da martabar Nijeriya a idanun duniya.

Ya ce a yanzu lokaci ne na ceto Nijeriya kuma lokacin sake gina kasa, don haka ya zama wajibi a yi aiki tare domin kubutar da Nijeriya daga hannun wadanda ke kokarin ruguza ta.

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

“Mun yadda da Nijeriya a matsayin kasa daya al’umma daya akasin wasu ‘yan takarar da ko kadan ba su yadda da ci gaba da dorewar kasar nan a matsayin kasa daya ba.

“Ya bayyana tare da cewar a bisa ga kwarewa da gogewa da sanin makamar shugabancin da Atiku Abubakar yake da ita zai jagoranci mulkin da kowa zai yaba a Nijeriya.”

Kusoshin ‘yan siyasar wadanda fitar su ta girgiza APC tare da karya lagonta a Jihar sun hada da uku daga cikin wadanda suka tsayawa jam’iyyar takarar fidda gwani na zaben gwamna, wato tsohon Ministan Wasanni kana Daraktan yakin neman zaben Buhari a 2019 a Sakkkwato, Yusuf Sulaiman, Shugaban Kwamitin Yaki da Fatara a Majalisar Wakilai, Hon. Abdullahi Salame da A.A Gumbi.

Haka ma akwai Kakakin Majalisar Dokoki ta Jihar Sakkwato, Hon. Aminu Achida da tsohon Ministan Al’adu, Sanata Bello Jibril Gada da kuma Hon. Yusuf Kurdula wanda ke wakiltar Tangaza/Gudu a Majalisar Wakilai.

Sauran sun hada da Hon. Murtala Maigona, wanda ke wakiltar Karamar Hukumar Wamakko a Majalisar Dokoki ta Jiha da tsofaffin shugabannin kananan hukumomin Sakkwato ta Arewa da Binji, Abdullahi Hassan da Sayyadi Nuhu Binji da tsofaffin kwamishinoni Aminu Bello Sokoto da Dahiru Maishanu Yabo.

Sai Mataimaki na Musamman ga Sanata Aliyu Wamakko kan Yada Labarai, Hassan Sahabi Sanyinnawal, da Yahaya Dallatu da ‘yan siyasa, ‘yan kasuwa, ‘yan kwangila da dubban daruruwan magoya bayansu.

A jawabinsa, tsohon Ministan Wasanni, Yusuf Sulaiman, ya bayyana cewar canza shekarsu daga APC zuwa PDP abin murna ne kuma za su jajirce domin ganin PDP ta samu nasarar kafa gwamnati daga sama har kasa baki daya.

Ya ce 2023 lokaci ne da jam’iyyar PDP za ta sake komawa fadar mulkin kasa.

Gwamna Aminu Waziri Tambuwal a takaitaccen jawabinsa, ya bayyana cewar a bisa ga kasawar APC na magance matsalolin da suka dabaibaye Nijeriya, wajibi ne a 2023 al’umma su zabi PDP domin kai kasar nan a tudun mun tsira.

Ya ce APC ba ta da tsari da cancantar da za ta kawar da matsalolin ‘yan Nijeriya.

Ya ce sakon da fitar manyan ‘yan siyasar ke nunawa a bayyane yake na kyakkyawar makoma da ke a gaban PDP wadda ya ce ba za ta yi kasa a guiwa ba wajen shimfida ingantaccen mulki na gari wanda ‘yan Nijeriya za su yaba a karkashin jagorancin Wazirin Adamawa.

PDP
Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
+ postsBio
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Zulum Ya Ƙaddamar Da Gidajen Ƴan Gudun Hijira 100 A Sakkwato
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Siyasar 2027: Yadda Ƴan Adawa Ke Ƙara Shiga Tsaka-mai-wuya

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
Har Yanzu Ina Neman Abokin Takara — Tinubu

Har Yanzu Ina Neman Abokin Takara — Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.