• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Oyetola Ya Ciwo Bashin Biliyan 18 Bayan Da Ya Fadi Zabe, Ba Mu San Me Zai Yi Da Su Ba – Adeleke

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Al'ajabi
0
Oyetola Ya Ciwo Bashin Biliyan 18 Bayan Da Ya Fadi Zabe, Ba Mu San Me Zai Yi Da Su Ba – Adeleke
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Osun, Ademola Adeleke, ya ce, tsohon gwamnan Jihar da ya bar masa kujera, Gboyega Oyetola, ya yi gaba gadi kawai ya je ya lafto bashin naira biliyan 18 jim kadan bayan da ya fadi a zaben gwaman jihar da aka gudanar a ranar 16 ga watan July na 2022. 

Gwamnan ya ce, kudaden da Oyetola ya ciwo bashinsu bayan fadinsa zabe ba su san ina ya kai ko me ya yi da su ba.

  • Gwamnatin Oyetola Ta Gadar Mana Bashin Biliyan 76 – Adeleke 

Bisa hakan, gwamnan ya ce gwamnatinsa ta gaji bashin biliyan 407.32 zuwa watan Nuwamban 2022.

Adeleke ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis sa’ilin da ke ganawa da sarakunan gargajiya na jihar Osun a Osogbo babban birnin jihar Osun ranar Alhamis.

A cewarsa, “Gwamnatina ta gaji basukan da ake bin jihar kashi-kashi har guda takwas da suka kunshi bashin albashi, tulin basukan fansho da sauransu da Gwamnatin Oyetota ta bar mana.”

Labarai Masu Nasaba

Matashi Ya Kashe Kakanninsa Kan Abinci A Kano

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

“Zuwa yau ana bin jihar Osun bashin biliyan N331.32.

“Idan aka hada da basukan albashi da fansho na naira biliyan 76. Basukan za su kai biliyan N407.32. Kuma har yanzu ba a tantance nawa ‘yan kwangila ke bi ba.

“Iyaka abun da ya shigo lalitar Gwamnatin jihar zuwa ranar Litinin 29 ga watan Nuwamba, kawai albashin watan Nuwamban 2022. Bayan hakan, lalitar jihar ya kasance wayam ba komai a ciki.

“A matsayina na gwamna, zan yi tambaya a madadinku. Kuma gaskiya muna bukatar amsa,” Adeleke ya fada wa sarakuna.

Ya kara da cewa, “Gwamnatin Oyetola dole ya fito ta yi bayanin bashin biliyan 331 da ta ciwo a madadin al’ummar jihar Osun me suka yi da shi da yaya suka kashe, ba tare da wani kwakkwaran aikin bunkasa jihar ba amma an ciwo tulin basuka.

“Kuma tilas ne gwamna Oyetola ya fito ya yi bayanin me ya yi da biliyan 18 da ya ciwo bashinsu bayan fadinsa a zabe ranar 16 ga watan July na 2022. Ya aka yi da su kuma ta yaya aka kashe su.

“Sannan, dole ya fito ya yi bayanin yadda aka yi jihar ya zama ana binta bashin albashin har naira biliyan 76 duk da cewa jihar ta samu kudaden Bail out na naira biliyan 50 daga wajen gwamnatin tarayya.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba Za Mu Bari A Ci Gaba Da Kai Hare-hare Ga Ofisoshin INEC Ba, Cewar Sufeton ‘Yansanda

Next Post

Sin Ta Fitar Da Ka’idojin Fadada Kasuwannin Cikin Gida

Related

Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
Al'ajabi

Matashi Ya Kashe Kakanninsa Kan Abinci A Kano

1 week ago
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
Al'ajabi

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

2 weeks ago
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi
Al'ajabi

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

3 weeks ago
Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi
Al'ajabi

Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi

3 months ago
Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 
Al'ajabi

Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 

4 months ago
Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi
Al'ajabi

Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi

4 months ago
Next Post
Sin Ta Fitar Da Ka’idojin Fadada Kasuwannin Cikin Gida

Sin Ta Fitar Da Ka’idojin Fadada Kasuwannin Cikin Gida

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.