• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PDP: Gwamnan Bala Ya Kalubalanci Wike Kan Kunno Wutar Rikicin Jam’iyya A Bauchi

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
PDP: Gwamnan Bala Ya Kalubalanci Wike Kan Kunno Wutar Rikicin Jam’iyya A Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban ƙungiyar gwamnonin PDP kuma gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad, ya ce, babu wata jam’iyyar siyasa da ba ta fuskantar ‘yan rikice-rikice ko da kuwa ta na da cikakken tsarin shugabanci.

 

Kazalika, gwamnan ya kuma maida martani kan iƙirarin baya-bayan nan da ministan birnin tarayya, Nyesom Wike, ya yi da ke cewa zai kunna wuta ga wasu gwamnonin jihohi na PDP kan yunƙurin kwace tsarin jam’iyyar a jihar Ribas, Bala ya ce, babu wanda ya isa ya kunno wuta a jihar Bauchi domin akwai wadatacccen ruwa da zai iya faca-faca da wutar.

  • An Masa Daurin Watanni 4 Kan Satar iPhone Guda 2
  • Ambaliya: Aminu Dantata Ya Bai Wa Maiduguri Tallafin Naira Biliyan 1.5

Gwamnan wanda ke wannan maganar a ranar Talata 17 ga watan Satumba, yayin da ya karɓi bakwancin shugabanni jam’iyyar PDP na ƙasa da suka kawo masa ziyarar mara baya a jihar Bauchi, ya yi tilawar cewa, mafi yawan ayyukan raya ƙasar nan jam’iyyar PDP ce ta yi su.

 

Labarai Masu Nasaba

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

Ya ce: “Ba wata jam’iyya da ta tsira ga kananan rikici na sabani, don haka, ya sa aka samu jagoranci saboda daidaita sabani da ajiye komai a inda ya dace.

 

“Dole ne mu yi abubuwa bisa doka da oda na jam’iyya, dole mu mutunta mutane, dole mu jingine ra’ayinmu a gefe, dole mu mutunta banbance-banbancenmu, kuma dole su ajiye matsayin jam’iyyar a saman kowa da mutunta jimammen tarihin jam’iyyar.”

 

Bala Muhammad ya kuma ce, jagoranci jam’iyyar a ɗinke yake kuma babu mai shigo da ra’ayin ƙashin kansa cikin lamuran.

 

Ya misalta cewa abota daban, mulki daban, kuma lamuran da suka shafi jam’iyya daban, don haka ya yi hannunka mai sanda ga abokin nasa Wike da cewa ba za su bari wani abu ya addabi jam’iyyar ba.

 

Ya kuma sanar da cewa, za su tattauna muhimman abubuwan da suka shafi ci gaban jam’iyyar PDP.

 

Tun da farko a jawabinsa, jagoran tawagar, kuma mai bai wa jam’iyyar shawara kan harkokin Shari’a, Kamaldeen Adeyemi Ajibade SAN, ya ce PDP na alfahari da yadda ta ga gwamnan na gudanar da wakilci na kwarai ta hanyar shimfiɗa nagartattun ayyuka da ya zaman musu abun alfahari a jihar.

 

Ya ce sun kuma zo ne domin nuna goyon baya domin ƙara wa gwamnan karfin gwiwa kan himma da azamarsa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wakilin Kasar Sin Ya Bukaci Amurka Da Ta Matsawa Isra’ila Ta Dakatar Da Ayyukan Soji A Gaza

Next Post

An Kammala Bikin Baje Kolin CIFTIS Tare Da Nasarori Masu Tarin Yawa

Related

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita
Labarai

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

7 hours ago
NNPP
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

9 hours ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

11 hours ago
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

12 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Labarai

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

14 hours ago
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye
Labarai

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

17 hours ago
Next Post
An Kammala Bikin Baje Kolin CIFTIS Tare Da Nasarori Masu Tarin Yawa

An Kammala Bikin Baje Kolin CIFTIS Tare Da Nasarori Masu Tarin Yawa

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.