• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PDP: Gwamnan Bala Ya Kalubalanci Wike Kan Kunno Wutar Rikicin Jam’iyya A Bauchi

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
1 year ago
Bala

Shugaban ƙungiyar gwamnonin PDP kuma gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad, ya ce, babu wata jam’iyyar siyasa da ba ta fuskantar ‘yan rikice-rikice ko da kuwa ta na da cikakken tsarin shugabanci.

 

Kazalika, gwamnan ya kuma maida martani kan iƙirarin baya-bayan nan da ministan birnin tarayya, Nyesom Wike, ya yi da ke cewa zai kunna wuta ga wasu gwamnonin jihohi na PDP kan yunƙurin kwace tsarin jam’iyyar a jihar Ribas, Bala ya ce, babu wanda ya isa ya kunno wuta a jihar Bauchi domin akwai wadatacccen ruwa da zai iya faca-faca da wutar.

  • An Masa Daurin Watanni 4 Kan Satar iPhone Guda 2
  • Ambaliya: Aminu Dantata Ya Bai Wa Maiduguri Tallafin Naira Biliyan 1.5

Gwamnan wanda ke wannan maganar a ranar Talata 17 ga watan Satumba, yayin da ya karɓi bakwancin shugabanni jam’iyyar PDP na ƙasa da suka kawo masa ziyarar mara baya a jihar Bauchi, ya yi tilawar cewa, mafi yawan ayyukan raya ƙasar nan jam’iyyar PDP ce ta yi su.

 

LABARAI MASU NASABA

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Ya ce: “Ba wata jam’iyya da ta tsira ga kananan rikici na sabani, don haka, ya sa aka samu jagoranci saboda daidaita sabani da ajiye komai a inda ya dace.

 

“Dole ne mu yi abubuwa bisa doka da oda na jam’iyya, dole mu mutunta mutane, dole mu jingine ra’ayinmu a gefe, dole mu mutunta banbance-banbancenmu, kuma dole su ajiye matsayin jam’iyyar a saman kowa da mutunta jimammen tarihin jam’iyyar.”

 

Bala Muhammad ya kuma ce, jagoranci jam’iyyar a ɗinke yake kuma babu mai shigo da ra’ayin ƙashin kansa cikin lamuran.

 

Ya misalta cewa abota daban, mulki daban, kuma lamuran da suka shafi jam’iyya daban, don haka ya yi hannunka mai sanda ga abokin nasa Wike da cewa ba za su bari wani abu ya addabi jam’iyyar ba.

 

Ya kuma sanar da cewa, za su tattauna muhimman abubuwan da suka shafi ci gaban jam’iyyar PDP.

 

Tun da farko a jawabinsa, jagoran tawagar, kuma mai bai wa jam’iyyar shawara kan harkokin Shari’a, Kamaldeen Adeyemi Ajibade SAN, ya ce PDP na alfahari da yadda ta ga gwamnan na gudanar da wakilci na kwarai ta hanyar shimfiɗa nagartattun ayyuka da ya zaman musu abun alfahari a jihar.

 

Ya ce sun kuma zo ne domin nuna goyon baya domin ƙara wa gwamnan karfin gwiwa kan himma da azamarsa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma
Labarai

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal
Labarai

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Next Post
An Kammala Bikin Baje Kolin CIFTIS Tare Da Nasarori Masu Tarin Yawa

An Kammala Bikin Baje Kolin CIFTIS Tare Da Nasarori Masu Tarin Yawa

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

October 28, 2025
Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

October 28, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.