• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PDP Ta Lashi Takobin Warware Rikicin Shugabancinta A Watan Agusta

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
PDP

Sakamakon taron koli na kwamitin zartarwa, PDP ta sha alwashin warware duk wani rikicin shugabanci da ya dabaibaye jam’iyyar a watan Agusta, inda ta bayar da umurnin cewa Umar Damagum ya ci gaba a matsayin mukaddashin shugaba. 

Rahotanni sun bayyana cewa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Atiku Abubakar da ministan Abuja, Nyesom Wike sun kasance a wurin taron amma ba su ce uffan ba bayan kammala taron.

  • Dalilin Da Ya Sa Duniya Ke Bukatar Karfin Sin Na Samar Da Hajoji Masu Alaka Da Makamashi Mai Tsafta
  • Masu Zargin Uba Sani Kan Bashin el-Rufa’i Sun Jahilci Aikin Majalisa – Barista Bello

Da yake ganawa da manema labarai bayan kammala taron, Gwamnan Jihar Bauchi kuma shugaban kungiyar gwamnonin PDP, Bala Muhammad ya bayyana cewa jam’iyyar za ta warware duk wani rikicin shugabanci.

Ya ce, “Nan da watanni biyu, za ku ga ayyukan jam’iyyar sun sauya. Shugabanci nauyi ne mai matukar wahala. A duk lokacin da muka samu nasarar gudanar da babban taro, za mu duba batun rikicin shugabanci, sannan za mu duba kundin tsarin mulkin jam’iyyar.

Sai dai kuma yankin arewa ta tsakiya ya dage wajen ganin ya kammala wa’adin mulkin Iyorchia Ayu wanda aka dakatar da shi. Yankin bai ji dadin yadda aka ce Damagum ya ci gaba da jagorancin jam’iyyar har a samu nasarar gudanar da babban taro.

LABARAI MASU NASABA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

Sakataren yada labarai na jam’yyar PDP, Debo Ologunagha ya ce saboda a samu damar shulhuntawa, za a warware rikicin shugabanci a watan Agusta lokacin da ake tsammanin kwamitin zartarwa zai sake zama.

“Jam’iyyarmu ta jaddada muhimmancin sulhu da samun daidaito a tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar a wannan lokaci. Kafin warware rikicin shugabanci, Umar Damagum zai ci gaba da rikon mukamin mukaddashin shugaba har zuwa ranar 15 ga Agustan 2024 lokacin da kwamitin zartarwa zai sake zama,” in ji Ologunagba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
Next Post
Liverpool Ta Amince Da Daukar Arne A Matsayin Sabon Kocinta A Kaka Mai Zuwa

Liverpool Ta Amince Da Daukar Arne A Matsayin Sabon Kocinta A Kaka Mai Zuwa

LABARAI MASU NASABA

Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

November 5, 2025
Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

November 5, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

Majalisar Dattawa Ta Amince da Naira Tiriliyan 1.1 Don Biyan Bashin ‘Yan Kwangila – Akpabio

November 5, 2025
An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Sanata Barau Ya Tsaya Takarar Shugaban Majalisar Dattawa

Ba Na Jin Tsoron Trump – Martanin Sanata Barau Ga Akpabio

November 5, 2025
CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

November 5, 2025
Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.