• English
  • Business News
Monday, October 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PDP Ta Lashi Takobin Warware Rikicin Shugabancinta A Watan Agusta

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
PDP Ta Lashi Takobin Warware Rikicin Shugabancinta A Watan Agusta

Sakamakon taron koli na kwamitin zartarwa, PDP ta sha alwashin warware duk wani rikicin shugabanci da ya dabaibaye jam’iyyar a watan Agusta, inda ta bayar da umurnin cewa Umar Damagum ya ci gaba a matsayin mukaddashin shugaba. 

Rahotanni sun bayyana cewa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Atiku Abubakar da ministan Abuja, Nyesom Wike sun kasance a wurin taron amma ba su ce uffan ba bayan kammala taron.

  • Dalilin Da Ya Sa Duniya Ke Bukatar Karfin Sin Na Samar Da Hajoji Masu Alaka Da Makamashi Mai Tsafta
  • Masu Zargin Uba Sani Kan Bashin el-Rufa’i Sun Jahilci Aikin Majalisa – Barista Bello

Da yake ganawa da manema labarai bayan kammala taron, Gwamnan Jihar Bauchi kuma shugaban kungiyar gwamnonin PDP, Bala Muhammad ya bayyana cewa jam’iyyar za ta warware duk wani rikicin shugabanci.

Ya ce, “Nan da watanni biyu, za ku ga ayyukan jam’iyyar sun sauya. Shugabanci nauyi ne mai matukar wahala. A duk lokacin da muka samu nasarar gudanar da babban taro, za mu duba batun rikicin shugabanci, sannan za mu duba kundin tsarin mulkin jam’iyyar.

Sai dai kuma yankin arewa ta tsakiya ya dage wajen ganin ya kammala wa’adin mulkin Iyorchia Ayu wanda aka dakatar da shi. Yankin bai ji dadin yadda aka ce Damagum ya ci gaba da jagorancin jam’iyyar har a samu nasarar gudanar da babban taro.

Labarai Masu Nasaba

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

Sakataren yada labarai na jam’yyar PDP, Debo Ologunagha ya ce saboda a samu damar shulhuntawa, za a warware rikicin shugabanci a watan Agusta lokacin da ake tsammanin kwamitin zartarwa zai sake zama.

“Jam’iyyarmu ta jaddada muhimmancin sulhu da samun daidaito a tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar a wannan lokaci. Kafin warware rikicin shugabanci, Umar Damagum zai ci gaba da rikon mukamin mukaddashin shugaba har zuwa ranar 15 ga Agustan 2024 lokacin da kwamitin zartarwa zai sake zama,” in ji Ologunagba.

ShareTweetSendShare
Yusuf Shuaibu

Yusuf Shuaibu

Related

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

3 days ago
Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar
Tambarin Dimokuradiyya

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

3 days ago
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

1 week ago
Next Post
Liverpool Ta Amince Da Daukar Arne A Matsayin Sabon Kocinta A Kaka Mai Zuwa

Liverpool Ta Amince Da Daukar Arne A Matsayin Sabon Kocinta A Kaka Mai Zuwa

LABARAI MASU NASABA

Karamin Ofishin Jakadancin Sin Da Ke Legas Ya Yi Bikin Bunkasa Al’adu Na Bikin Tsakiyar Kaka

Karamin Ofishin Jakadancin Sin Da Ke Legas Ya Yi Bikin Bunkasa Al’adu Na Bikin Tsakiyar Kaka

October 6, 2025
Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta

Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta

October 6, 2025
Nazari Ya Gano Falalen Dutse Na Yanki Mai Nisa A Duniyar Wata Ya Fi Tsananin Sanyi Fiye Da Na Yanki Na Kusa

Nazari Ya Gano Falalen Dutse Na Yanki Mai Nisa A Duniyar Wata Ya Fi Tsananin Sanyi Fiye Da Na Yanki Na Kusa

October 6, 2025
Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni

Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni

October 6, 2025
Tinubu

Talaucin Da Ya Ninku Fiye Da Sau Biyu A Gwamnatin Tinubu, An Ƙuduri Aniyar Kawar Da Shi Nan Da Shekaru 5

October 6, 2025
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)

TRCN Ta Koka Kan Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya 

October 6, 2025
Rwanda Da Huawei Sun Kaddamar Da Shirin DigiTruck Domin Bunkasa Fasaha A Fadin Kasar

Rwanda Da Huawei Sun Kaddamar Da Shirin DigiTruck Domin Bunkasa Fasaha A Fadin Kasar

October 6, 2025
Sojoji Sun Tarwatsa Maɓoyar ‘Yan Bindiga 11, Sun Ƙwato Makamai A Taraba

Sojoji Sun Tarwatsa Maɓoyar ‘Yan Bindiga 11, Sun Ƙwato Makamai A Taraba

October 6, 2025
Kwallon Hockey: Nijeriya Na Fatan Samun Nasara A Masar

Kwallon Hockey: Nijeriya Na Fatan Samun Nasara A Masar

October 6, 2025
Kwale-kwale

Kifewar Kwale-kwale, Ya Ci Rayukan ‘Yan Uwa 5 A Benuwe 

October 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.