• English
  • Business News
Thursday, October 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PENGASSAN Ta Musanta Janyewa Daga Yajin Aiki, Ta Gargaɗi Dangote

by Abubakar Sulaiman
9 hours ago
in Manyan Labarai
0
PENGASSAN Ta Musanta Janyewa Daga Yajin Aiki, Ta Gargaɗi Dangote
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ƙungiyar ma’aikatan man fetur da iskar gas (PENGASSAN) ta musanta cewa ta rattaɓa hannu kan yarjejeniyar da aka ce ta kawo ƙarshen yajin aikin da ta shiga kan rikicinta da Matatar Man Dangote. Shugaban ƙungiyar, Festus Osifo, ya ce babban abin da suke nema shi ne a dawo da sama da ma’aikata 800 da aka kora, ba wai batun kuɗin ƙungiya ba.

Osifo ya yi watsi da zargin da kamfanin Dangote ya yi cewa ma’aikatan da aka sallama sun yi ƙoƙarin yi wa matatar zagon ƙasa, yana mai cewa wannan iƙirarin “ba gaskiya ba ne kuma yana da illa ga makomar su.” Ya gargaɗi cewa idan ba a dawo da ma’aikatan ba kamar yadda aka yi alƙawari ba, ƙungiyar na iya dawo da yajin aikin ba tare da wani gargadi ba.

  • PENGASSAN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Ta Fara
  • NNPCL Ya Ƙulla Sabuwar Yarjejeniya Ta Samar Da Ɗanyen Mai Na Shekaru Biyu Da Matatar Dangote

Ministan ƙwadago, Mohammed Dingyadi, ya bayyana cewa gwamnati ta matsa lamba har Dangote ya amince da sake ɗaukar ma’aikatan da aka sallama a wasu kamfanonin rukunin Dangote ba tare da asarar albashinsu ba. Ya kuma tabbatar da cewa duk wani ma’aikaci na da ‘yancin shiga ƙungiyar ƙwadago.

Sai dai Osifo ya ce akwai “ruɗani” a yarjejeniyar da aka cimma, ya kuma soki yadda wasu kafafen yaɗa labarai suka damalmala batun. Ƙungiyar TUC ta nuna goyon bayanta ga PENGASSAN, tana mai gargadin cewa ba za a bar kowace ƙungiya ko Kamfani ta tauye haƙƙin ma’aikata ba.

Matatar Dangote ta kare kanta, tana mai cewa sake tsarinta wajibi ne don tsaro da inganci, tare da zargin PENGASSAN da amfani da dabaru marasa dacewa. A halin yanzu, kotun masana’antu ta bayar da umarnin dakatar da ci gaba da yajin aikin har zuwa zaman sauraron ƙarar a ranar 13 ga Oktoba.

Labarai Masu Nasaba

Dubban Matasan Kano Sun Yi Zanga-zangar Lumana Domin Goyon Bayan CP AI Bakori

Wata Mata Ta Banka Wa Kanta Wuta Har Lahira A Bauchi


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DangotePENGASSANStrike
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

Next Post

Wata Mata Ta Banka Wa Kanta Wuta Har Lahira A Bauchi

Related

Dubban Matasan Kano Sun Yi Zanga-zangar Lumana Domin Goyon Bayan CP AI Bakori
Manyan Labarai

Dubban Matasan Kano Sun Yi Zanga-zangar Lumana Domin Goyon Bayan CP AI Bakori

3 hours ago
Wata Mata Ta Banka Wa Kanta Wuta Har Lahira A Bauchi
Manyan Labarai

Wata Mata Ta Banka Wa Kanta Wuta Har Lahira A Bauchi

7 hours ago
Shettima Ya Dawo Abuja Bayan Ziyarar UNGA Da Jamus
Manyan Labarai

Shettima Ya Dawo Abuja Bayan Ziyarar UNGA Da Jamus

12 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kama Ɓarayi A Jihar Neja

12 hours ago
Jami’an Tsaro Sun Kashe Ƙasurgumin Mai Garkuwa Da Mutane, Maidawa Da Wasu A Kwara
Manyan Labarai

Jami’an Tsaro Sun Kashe Ƙasurgumin Mai Garkuwa Da Mutane, Maidawa Da Wasu A Kwara

13 hours ago
Ibtila’in Ambaliyar Ruwa: Halin Da Birnin Maiduguri Ya Tsinci Kansa A Ciki
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Gargaɗi Kan Yiwuwar Aukuwar Ambaliya A Wasu Jihohi

15 hours ago
Next Post
Wata Mata Ta Banka Wa Kanta Wuta Har Lahira A Bauchi

Wata Mata Ta Banka Wa Kanta Wuta Har Lahira A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Jihar Nasarawa Ta Tallafawa Ɗalibai 16,756 Da Naira Miliyan 592

Gwamnatin Jihar Nasarawa Ta Tallafawa Ɗalibai 16,756 Da Naira Miliyan 592

October 2, 2025
Gwamna Lawal Ya Gwangwaje Kamfanin Sufurin Mota Na Zamfara Da Motoci 50 

Gwamna Lawal Ya Gwangwaje Kamfanin Sufurin Mota Na Zamfara Da Motoci 50 

October 2, 2025
Balaguron Fasinjoji Ta Jirgin Kasa A Kasar Sin Ya Kai Matsayi Mafi Girma A Bikin Ranar Kafuwar PRC

Balaguron Fasinjoji Ta Jirgin Kasa A Kasar Sin Ya Kai Matsayi Mafi Girma A Bikin Ranar Kafuwar PRC

October 2, 2025
Dubban Matasan Kano Sun Yi Zanga-zangar Lumana Domin Goyon Bayan CP AI Bakori

Dubban Matasan Kano Sun Yi Zanga-zangar Lumana Domin Goyon Bayan CP AI Bakori

October 2, 2025
Xi Ya Taya Jami’ar Tianjin Murnar Cika Shekaru 130 Da Kafuwa

Xi Ya Taya Jami’ar Tianjin Murnar Cika Shekaru 130 Da Kafuwa

October 2, 2025
‘Yansanda Sun Ƙwato Muggan Ƙwayoyi Na Naira Miliyan 120 A Kano

‘Yansanda Sun Ƙwato Muggan Ƙwayoyi Na Naira Miliyan 120 A Kano

October 2, 2025
Kasar Sin Ta Nuna Takaici Da Matakin Amurka Na Kin Amincewa Da Daftarin Kudurin Gaza

Kasar Sin Ta Nuna Takaici Da Matakin Amurka Na Kin Amincewa Da Daftarin Kudurin Gaza

October 2, 2025
Alaafin Ya Nemi Gwamnatin Tarayya Ta Kama Masu Kashe Kashe A Kwara

Alaafin Ya Nemi Gwamnatin Tarayya Ta Kama Masu Kashe Kashe A Kwara

October 2, 2025
Wata Mata Ta Banka Wa Kanta Wuta Har Lahira A Bauchi

Wata Mata Ta Banka Wa Kanta Wuta Har Lahira A Bauchi

October 2, 2025
PENGASSAN Ta Musanta Janyewa Daga Yajin Aiki, Ta Gargaɗi Dangote

PENGASSAN Ta Musanta Janyewa Daga Yajin Aiki, Ta Gargaɗi Dangote

October 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.