• English
  • Business News
Friday, October 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PRP Ta Tabbatar Da Tattaunawar Hadewa Da Jam’iyyar ADC Gabanin Zaben 2027

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
10 months ago
PRP

Jam’iyyar PRP ta tabbatar da cewa ta fara tattaunawa da wata jam’iyyar adawa ta ADC, kan yuwuwar hadewar jam’iyyun gabanin babban zaben shekarar 2027.

Shugaban jam’iyyar PRP na kasa, Falalu Bello ne ya bayyana hakan a wani taron hadin gwiwa da takwaransa na ADC, Ralph Nwosu a Abuja.

  • Da Rancen Naira Tiriliyan 13 Za A Cike Gibin Kasafin Kudin 2025 — Edun
  • Kisan Jami’an ‘Yansanda 229 A Cikin Wata 22 Babbar Musiba Ce Ga Kasa

Matakin na zuwa ne kwanaki uku bayan da jam’iyyar APC mai mulki ta yi gargadin cewa babu wani hadewar shugabannin ‘yan adawa da suka hada da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar da tsohon gwamnan Anambra, Peter Obi, da zai iya kwace kujerar Shugaban kasa Bola Tinubu a zaben 2027.

Jam’iyyar APC na mayar da martani ne kan kalaman da mai magana da yawun Atiku, Paul Ibe, ya yi cewa shugaban nasa da takwaransa na jam’iyyar LP duk sun koyi darasi a zaben da ya gabata, kuma za su hada kai domin korar jam’iyya APC a kan karagar mulki.

Haka zalika, wasu jam’iyyun siyasa na adawa a karkashin inuwar hadakar jam’iyyun siyasa da jam’iyyar SDP, su ma sun bayyana shirinsu na tattaunawa kan yiwuwar yin kawance, suna masu cewa kasar na bukatar hadakar Atiku da Obi.

LABARAI MASU NASABA

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Shirya Wa Janar Musa Faretin Gama Aiki

Gwamnatin Tarayya Da Stellar Steel, Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Habaka Karafan Cikin Gida

Da yake yi wa manema labarai jawabi a ranar Juma’a, Bello ya tabbatar da cewa tuni suka fara tattaunawa da shugabannin ADC domin fara shirin ceto kasar nan daga hannun jam’iyya mai mulki.

Ya ce, “Eh, mun fara tattaunawa. Ba ma tsoron hadewa gaba daya. Mu duba tarihin zabe. PRP ita ce jam’iyyar siyasa mafi tsufa a yau. Mun kafa gwamnati a Kaduna a shekarar 1979, saboda kawancen siyasa da jam’iyyun UPN, NPP, da PNP a jihar.

“Idan sauran jam’iyyu suna son shiga cikinmu, to muna maraba da su. Kofofinmu a bude suke ga kowa da kowa hatta daidaikun mutane, ba jam’iyyun siyasa kadai ba. Amma idan sun gwammace su shiga jam’iyyar da ba ta son jama’a da maganar kudi kawai, su koma PDP da APC. Abin da suka tsaya a kai kenan.

“Don haka muna cewa mun gaji kuma muna son wani sabon sauyi. Idan kuma hakan ya bukaci ni ko shugaban jam’iyyar ADC ya sauka daga mukaminsa, to haka ya kasance. Wannan kasa ta fi mu muhimmanci. Kundin tsarin mulkin jam’iyyar PRP yana wakiltar ka’ida da akidar da muke tsayawa a kai.”

Nwosu ya kuma ce bukatar a hada kai ta kara samun karbuwa sakamakon gano cewa suna da akida daya.

Shugaban jam’iyyar ADC ya bayyana cewa, a halin da ake ciki wahalhalun da ake fama da su a kasar nan bai kamata a ce jama’a sun gaji ba, kuma suna bukatar sabon sauyi.

“Hadin kai da hadin gwiwa wanda a karshe zai haifar da yuwuwar hadaka yana gudana tsakanin PRP da ADC. Me ya sa muke yin haka? gina akidar siyasa da fayyace hangen inda muka dosa.

“Jam’iyyunmu ne suka fara wannan magana ta kawance, ba wai ta mutanen da ke neman mukami ba ne. Wadannan shugabannin jam’iyyun siyasa ne wadanda suke jin cewa ya kamata a samu sauyi a kasar nan kuma suna son ci gaba. A karshe, idan mutanen da ke neman mukami sun shigo dole ne su bi wasu ka’idojin da ya kamata su bi. Damuwarmu game da dimokuradiyya a fili take,” ya kara da cewa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Shirya Wa Janar Musa Faretin Gama Aiki
Labarai

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Shirya Wa Janar Musa Faretin Gama Aiki

October 31, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP
Labarai

Gwamnatin Tarayya Da Stellar Steel, Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Habaka Karafan Cikin Gida

October 31, 2025
Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa
Labarai

Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa

October 31, 2025
Next Post
Ya Kamata Amurka Ta Janye Cuba Daga Jerin Kasashe Masu Goyon Bayan Ta’addanci

Ya Kamata Amurka Ta Janye Cuba Daga Jerin Kasashe Masu Goyon Bayan Ta’addanci

LABARAI MASU NASABA

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Shirya Wa Janar Musa Faretin Gama Aiki

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Shirya Wa Janar Musa Faretin Gama Aiki

October 31, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Gwamnatin Tarayya Da Stellar Steel, Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Habaka Karafan Cikin Gida

October 31, 2025
Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa

Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa

October 31, 2025
Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar

Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar

October 31, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa

October 31, 2025

Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda

October 31, 2025
Yan Nijeriya Na Ɗanɗana Kuɗarsu Kan Jinkirta Cire Tallafin Mai – Sarki Sanusi

Yan Nijeriya Na Ɗanɗana Kuɗarsu Kan Jinkirta Cire Tallafin Mai – Sarki Sanusi

October 31, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Allah Ya Kai Manzon Allah (SAW) Muƙami Na Babban Yabo A Cikin Komai

October 31, 2025
Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare

Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare

October 31, 2025
Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.