ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kisan Jami’an ‘Yansanda 229 A Cikin Wata 22 Babbar Musiba Ce Ga Kasa

by Leadership Hausa and Sulaiman
2 years ago
Yansanda

Ga akasarin ‘yan Nijeriya rahoton da aka wallafa na kashe jami’ian ‘yan sanda 229 a cikin watanni 22, wani abin damuwa ne.

Wadannan alkalumman sun nuna yadda, aka samu raguwar jam’ian da ke rike da manyan mukamai da suka kai kaso goma a cikin wata.

  • Tallafin Wutar Lantarki Ya Kai Naira Biliyan 199.64 A Nijeriya – NERC
  • Yadda Ciniki Ya Habaka Tsakanin Babban Yankin Kasar Sin Da Yankin Macao A Fiye Da Shekaru 25

Wannan ta’addacin da aka yi wa wadannan ‘yan sandan da suka rasa rayukansu, babban abin damuwa ne, kuma abu ne, da ba za a lumunta ba, kuma dole ne, a gudanar da bincke, duk da cewa, duk wanda aka dauke shi aikin wanzar da tsaro, zai iya rasa ransa, ako wane lokaci.

ADVERTISEMENT

Amma wannan zafin rashin na jami’an, duk da cewa, mutuwa wata aba ce, da ba za a iya kaucewa mata ba.

Wasu rahotannin sun bayyana cewa, adadin na wadannan mamatan ‘yan sandan, ko dai ‘yan bindiga daji, ‘yan bindiga, ‘yan kungiyar ta’addan Boko Haram, ‘yan kungiyar asiri da kuma masu fashi da makami ne, suka yi salar salwantar da rayukansu.

LABARAI MASU NASABA

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba

Sun dai, rasa rayukansu ne, a yayin da suke kan gudanar da ayyukansu na kare rayuka da dukiyoyin ‘yan kasa.

Duba da wannan rahoton za a iya yin tunanin irin yawan ‘yan Nijeriya da ba su ji, ba su kuma gani ba, suka rasa nasu rayukan, duk a cikin wadannan watannin 22.

‘Yan Nijeriyar sun rasa rayukansu ne, ba wai domin sun aikata wani laifi ba, sai dai kawai, domin wasu ‘yan siyasa masu rike da madafun iko ne, ke shugabanta su, ba su dauki rayukansu a bakin komai ba.

A Nijeriya abin ba a boye yake ba, domin aikin na ‘yan sandan kasar tamkar sadaukar da rai ne, musamman ma da yadda suke yin artabu da miyagun masu aikata manyan laifuka a yayin gudanar da aikinsu.

Wani abin bakin ciki shi ne, a yayin artabun, miyagun sun kasance suna dauke da manyan makamai ne, da suka fi na ‘yan sandan, wanda a wani lokacin, hakan ke bai wa miyagun galaba, a kan ‘yan sandan a lokacin artabun.

Wannan jaridar ta dade tana maimaita maganar cewa, akwai matukar bukatar a wadata jami’an ‘yan sandan kasar nan, da manyan makamai, idan ka yi la’akari da irin hadarin da ke tattare da aikinsu.

Wani abin takaici shi ne, yadda mahukuntan ‘yan sanda a kasar, ba su bai wa ‘yan sanda wadatattun Albarusai, wanda kuma ake kakaba masu takunkumin dole ne, sai sun sanar da hukumomin ‘yan sandan, adadin Albarusan da suka yi amfan da su a yayin da suke gudanar da aikinsu, na kwantar da duk wata kura, da ta taso.

A rubuce yake a kasar nan cewa, a daukacin bangaren jami’an tsaron kasa, bagaren ‘yan sanda, sune koma baya wajen rashin kula da jin dadinsu da walwalarsu.

Wannan matsalar, ta kasance tana karya masu gwiwa wajen gudanar da aikinsu a cikin nuna kwarewa, domin yiwa alumma aiki yadda ya dace.

A wasu lokutan ma, sune suke sayawa kansu kaki da wasu manyan kayan aiki, domin kawai, su gudanar da aikisnu, na kare rayuka da dukiyoyin ‘yan kasa.

Sai dai kuma, wannan ya tabbatar da maganar mu, duba da yadda ake wadata su da manyan makamai idan an tura zuwa wasu kasashe don tabbatar da zaman lafiya.

Kazalika, wani abin dubi shi ne, yadda ‘yan sandan suke gudanar da aikinsu, ba tare da suna da wata kwarewar kirki ba, koda yake, wasu na cewa, haka irin aikin nasu yake, amma mu ana nan, muna da jayya kan wannan ra’ayin, domin kuwa, ba irin aikin ‘yan sanda bane, a cikin tawargar su, su rinka farautar manyan masu aikita laifi, a cikin motocin su da suka riga suka tsufa ba.

Babban hatsari ne ga ‘yan sanda su fita gudana da aiki da Albarusan da aka kidaya masu, za su yi amfani da su ba.

Hakazalika, bama goyon bayan cewar da ake yi ‘yan sandan su kula da jin dadinsu da walwalarsu da kansu, domin kawai, Babban Sifeta Janar na ‘yan sanda ya amince masu su sanya kaki.

Dole, a a tabbatar da ana kula da sa kishin kasa, musamman a aiki irin na ‘yan sanda, duba da irin barazanar da suke fuskanta a yayin gudanar da aikinsu.

Suma ‘yan Adam ne, kamar kowanne dan kasa kuma suna da iyali da ‘yan uwa, da suka dogara a kansu.

Mun dade muna ankarar da hukumomin tsaro na kasar nan, kan kalubalen da hukumomin tsaron kasar ke ci gaba da fuskanta, wanda irin wadannan kalubalen, an kirkire su ne kawai.

Kazalika, akan kuma samu takardama ko rashin jituwa, a tsakanin wadannan hukumomin tsaron kasar, wanda kamata ya yi a ce, sun hada kansu a waje daya wajen samun bayanai.

Yin amfani da fasahar kimiyyar zamani wajen samun bayanai na sirri, a tsakanin hukumomin tsaron kasar, na daya daga cikin abubuwa masu mahimmanci.

Domin gudanar da aikin, ba tare dayin dabarun samun bayanan sirri ba, tamkar fargar daji ne.

A ra’ayin mu, babu wani dalili da zai sanya a ce, an rasa rayukan ‘yan sandan kasa, a cikin wannan gajeren lokacin.

Muna ganin ya zama wajibi, mahukutan ‘yan sandan kasa, su tabbatar da sun dauki matakan da suka dace, wajen kare rayukan jami’an.

Kazalika, muna son mu kara nanata cewa, aikin ‘yan sandan ba wai aiki ne, na jeka ka kashe kanka ba, kuma bai katama a rinka yiwa aikin kallon haka ba.

Ba da ce, ace aikin ne, na mutuwa domin kare kasa ba, kamata ya yi, aikin ya zamo aiki ne, na kare kasa kuma jami’I ya kasance a raye, domin ya sanar da labarin.

Yansanda
Leadership Hausa
Website |  + posts Bio
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
Yansanda
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi
Ra'ayinmu

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

July 10, 2026
Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba
Ra'ayinmu

Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba

July 3, 2026
sikila
Ra'ayinmu

Buƙatar Mayar Da Hankali Wajen Kawo Ƙarshen Ciwon Sikila A Nijeriya

June 26, 2026
Next Post
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Jami'an Tsaron Nijeriya Sun Hallaka 'Yan Ta'adda 8,034 A 2024 – ONSA

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.