• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PSC Ta Kori Jami’an ‘Yansanda 3 Kan Rashin Ladabi Da Biyayya

Ta Kara Wa Manyan Jami'ata 109 Girma

by Khalid Idris Doya
2 years ago
PSC

Hukumar kula da harkokin ‘yansanda ta kasa (PSC), a ranar Laraba ta amince da korar ‘yansanda uku masu mukamin mataimakan Sufuritendan (ASPs) sannan, ta kuma rage mukamin mai taimakawa kwamishina (ACP), babban Sufuritendan, wasu jami’ai biyu masu mukamin Sufuritendan da wani mataimakin Sufuritendan bisa kama su da laifuka daban-daban da suka hada da rashin da’a/ladabi da biyayya hadi da wasu laifukan.

Hukumar ta kuma amince da tsawatarwa/gargadi mai tsanani ga wani mataimakin kwamishinan ‘yansanda, babban Sufuritenda, da Sufuritenda su hudu, da wasu mataimakan Sufuritendan (DSP) su biyu hadi da masu taimaka wa Sufuritendan ‘yansanda su 12 (ASPs).

  • Kasar Sin Ta Yi Kira Da A Gaggauta Tsagaita Bude Wuta A Sudan

Hukumar ta cimma wannan matsayar ne a zamanta karo na 20 da ya gudana a ranar Laraba a shalkwatar hukumar da ke Jabi, Abuja wanda shugaban hukumar kuma tsohon Sufeto-janar na ‘yansanda, Dakta Solomon Arase ya jagoranta.

Kakakin hukumar, Ikechukwu Ani, a sanarwar da ya fitar ranar Laraba da daddare, ya shaida cewar hukumar ta kuma amince da hukuncin gargadi mai tsauri ga wasu jami’ai shida da Sufuritenda daya da mataimakan Sufuritendan guda biyar.

Kazalika, hukumar ta kuma amince da karin girma ga wasu manyan jami’an hukumar su 109.

LABARAI MASU NASABA

ACF Ta Yi Zargin Shiri Na Musamman Don Rusa Matatar Man Dangote

Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

Shugaban hukumar wanda a karonsa na farko ke nan ya jagoranci zaman hukumar tun bayan nada shi da shugaba Buhari ya yi, ya taya sabbin jami’an da suka samu karin girman murna, sai ya kalubalancesu da su kari ninka kokarinsa domin sauke nauyin da ke rataye a wuyayensu wajen gudanar da aiki yadda ya dace.

Dr. Arase ya ce, dole ne su tashi tsaye su kara azama da himma domin kyautata aikin hukumar PSC.

Ya bada tabbacin cewa karin girma ga Jami’ai na daga cikin muhimman abubuwan da zai sanya a gaba, amma fa sai ya ce dole ne sai kowani jami’i zai ji cewa a shirye yake ya kara kokari wajen sauke nauyin da ke kansa.

Kazalika, shugaban na PSC ya nemi ‘yansanda da a kowani lokaci suke gudanar da ayyukansu biya tafiya kan ka’idar da dokokin da aka gindaya domin kyautata aikinsu.

Ya ce, matakin ladabtarwa zai sauka kan duk jami’an da aka kama da aikata laifuka kuma a hukuntasu daidai da laifukansu domin cigaba da tsarkake bangaren aiki da tabbatar da aikin dan sanda na tafiya bisa kwarewa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Matatar dangote
Labarai

ACF Ta Yi Zargin Shiri Na Musamman Don Rusa Matatar Man Dangote

October 10, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus
Labarai

Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

October 10, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC
Labarai

Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

October 10, 2025
Next Post
Zaben Gwamnan Adamawa: Kotu Ta Kori Karar Da Binani Ta Kai INEC

Zaben Gwamnan Adamawa: Kotu Ta Kori Karar Da Binani Ta Kai INEC

LABARAI MASU NASABA

PSC

Burin ‘Yan Nijeriya Bai Cika Ba Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai

October 10, 2025
Matatar dangote

ACF Ta Yi Zargin Shiri Na Musamman Don Rusa Matatar Man Dangote

October 10, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

October 10, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

October 10, 2025
Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taɓa Yi (2)

Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taɓa Yi (2)

October 10, 2025
Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi

Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi

October 10, 2025
Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

October 10, 2025
Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

October 10, 2025
An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

October 9, 2025
Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.