• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PSC Ta Kori Jami’an ‘Yansanda 3 Kan Rashin Ladabi Da Biyayya

Ta Kara Wa Manyan Jami'ata 109 Girma

by Khalid Idris Doya
3 years ago
PSC

Hukumar kula da harkokin ‘yansanda ta kasa (PSC), a ranar Laraba ta amince da korar ‘yansanda uku masu mukamin mataimakan Sufuritendan (ASPs) sannan, ta kuma rage mukamin mai taimakawa kwamishina (ACP), babban Sufuritendan, wasu jami’ai biyu masu mukamin Sufuritendan da wani mataimakin Sufuritendan bisa kama su da laifuka daban-daban da suka hada da rashin da’a/ladabi da biyayya hadi da wasu laifukan.

Hukumar ta kuma amince da tsawatarwa/gargadi mai tsanani ga wani mataimakin kwamishinan ‘yansanda, babban Sufuritenda, da Sufuritenda su hudu, da wasu mataimakan Sufuritendan (DSP) su biyu hadi da masu taimaka wa Sufuritendan ‘yansanda su 12 (ASPs).

  • Kasar Sin Ta Yi Kira Da A Gaggauta Tsagaita Bude Wuta A Sudan

Hukumar ta cimma wannan matsayar ne a zamanta karo na 20 da ya gudana a ranar Laraba a shalkwatar hukumar da ke Jabi, Abuja wanda shugaban hukumar kuma tsohon Sufeto-janar na ‘yansanda, Dakta Solomon Arase ya jagoranta.

Kakakin hukumar, Ikechukwu Ani, a sanarwar da ya fitar ranar Laraba da daddare, ya shaida cewar hukumar ta kuma amince da hukuncin gargadi mai tsauri ga wasu jami’ai shida da Sufuritenda daya da mataimakan Sufuritendan guda biyar.

Kazalika, hukumar ta kuma amince da karin girma ga wasu manyan jami’an hukumar su 109.

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

Shugaban hukumar wanda a karonsa na farko ke nan ya jagoranci zaman hukumar tun bayan nada shi da shugaba Buhari ya yi, ya taya sabbin jami’an da suka samu karin girman murna, sai ya kalubalancesu da su kari ninka kokarinsa domin sauke nauyin da ke rataye a wuyayensu wajen gudanar da aiki yadda ya dace.

Dr. Arase ya ce, dole ne su tashi tsaye su kara azama da himma domin kyautata aikin hukumar PSC.

Ya bada tabbacin cewa karin girma ga Jami’ai na daga cikin muhimman abubuwan da zai sanya a gaba, amma fa sai ya ce dole ne sai kowani jami’i zai ji cewa a shirye yake ya kara kokari wajen sauke nauyin da ke kansa.

Kazalika, shugaban na PSC ya nemi ‘yansanda da a kowani lokaci suke gudanar da ayyukansu biya tafiya kan ka’idar da dokokin da aka gindaya domin kyautata aikinsu.

Ya ce, matakin ladabtarwa zai sauka kan duk jami’an da aka kama da aikata laifuka kuma a hukuntasu daidai da laifukansu domin cigaba da tsarkake bangaren aiki da tabbatar da aikin dan sanda na tafiya bisa kwarewa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma
Labarai

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025
tinubu
Labarai

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025
Next Post
Zaben Gwamnan Adamawa: Kotu Ta Kori Karar Da Binani Ta Kai INEC

Zaben Gwamnan Adamawa: Kotu Ta Kori Karar Da Binani Ta Kai INEC

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025
tinubu

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025
Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

November 4, 2025
2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

November 4, 2025
Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

November 4, 2025
Karancin Abinci: Kofar Ofishin Tinubu A Rufe Take, Har Wasu Ministoci Ba Su Iya Ganinsa – Ndume 

Zargin Kisan Kiyashi Ga Kiristoci: Trump Bai San Ƙalubalen Tsaron Da Najeriya Ke Ciki Ba — Ndume

November 4, 2025
Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.