• English
  • Business News
Monday, August 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PSC Ta Kori Jami’an ‘Yansanda 3 Kan Rashin Ladabi Da Biyayya

Ta Kara Wa Manyan Jami'ata 109 Girma

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Zargin Yaudara: Wani Tela Ya Kashe Tsohuwar Masoyiyarsa A Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar kula da harkokin ‘yansanda ta kasa (PSC), a ranar Laraba ta amince da korar ‘yansanda uku masu mukamin mataimakan Sufuritendan (ASPs) sannan, ta kuma rage mukamin mai taimakawa kwamishina (ACP), babban Sufuritendan, wasu jami’ai biyu masu mukamin Sufuritendan da wani mataimakin Sufuritendan bisa kama su da laifuka daban-daban da suka hada da rashin da’a/ladabi da biyayya hadi da wasu laifukan.

Hukumar ta kuma amince da tsawatarwa/gargadi mai tsanani ga wani mataimakin kwamishinan ‘yansanda, babban Sufuritenda, da Sufuritenda su hudu, da wasu mataimakan Sufuritendan (DSP) su biyu hadi da masu taimaka wa Sufuritendan ‘yansanda su 12 (ASPs).

  • Kasar Sin Ta Yi Kira Da A Gaggauta Tsagaita Bude Wuta A Sudan

Hukumar ta cimma wannan matsayar ne a zamanta karo na 20 da ya gudana a ranar Laraba a shalkwatar hukumar da ke Jabi, Abuja wanda shugaban hukumar kuma tsohon Sufeto-janar na ‘yansanda, Dakta Solomon Arase ya jagoranta.

Kakakin hukumar, Ikechukwu Ani, a sanarwar da ya fitar ranar Laraba da daddare, ya shaida cewar hukumar ta kuma amince da hukuncin gargadi mai tsauri ga wasu jami’ai shida da Sufuritenda daya da mataimakan Sufuritendan guda biyar.

Kazalika, hukumar ta kuma amince da karin girma ga wasu manyan jami’an hukumar su 109.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

Shugaban hukumar wanda a karonsa na farko ke nan ya jagoranci zaman hukumar tun bayan nada shi da shugaba Buhari ya yi, ya taya sabbin jami’an da suka samu karin girman murna, sai ya kalubalancesu da su kari ninka kokarinsa domin sauke nauyin da ke rataye a wuyayensu wajen gudanar da aiki yadda ya dace.

Dr. Arase ya ce, dole ne su tashi tsaye su kara azama da himma domin kyautata aikin hukumar PSC.

Ya bada tabbacin cewa karin girma ga Jami’ai na daga cikin muhimman abubuwan da zai sanya a gaba, amma fa sai ya ce dole ne sai kowani jami’i zai ji cewa a shirye yake ya kara kokari wajen sauke nauyin da ke kansa.

Kazalika, shugaban na PSC ya nemi ‘yansanda da a kowani lokaci suke gudanar da ayyukansu biya tafiya kan ka’idar da dokokin da aka gindaya domin kyautata aikinsu.

Ya ce, matakin ladabtarwa zai sauka kan duk jami’an da aka kama da aikata laifuka kuma a hukuntasu daidai da laifukansu domin cigaba da tsarkake bangaren aiki da tabbatar da aikin dan sanda na tafiya bisa kwarewa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

NAHCON Ta Bai Wa Jihohi Wa’adin Awa 48 Da Su Tura Kudaden Aikin Hajjin 2023

Next Post

Zaben Gwamnan Adamawa: Kotu Ta Kori Karar Da Binani Ta Kai INEC

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

56 minutes ago
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe
Ra'ayi Riga

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

1 hour ago
Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano
Manyan Labarai

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

2 hours ago
Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara
Labarai

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

3 hours ago
Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa
Labarai

Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

4 hours ago
Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule
Labarai

Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule

5 hours ago
Next Post
Zaben Gwamnan Adamawa: Kotu Ta Kori Karar Da Binani Ta Kai INEC

Zaben Gwamnan Adamawa: Kotu Ta Kori Karar Da Binani Ta Kai INEC

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

August 4, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

August 4, 2025
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

August 4, 2025
Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

August 4, 2025
Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

August 4, 2025
Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

August 4, 2025
Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule

Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule

August 4, 2025
Tsohon Dan Majalisar Taraba Usman Ya Fice Daga APC

Tsohon Dan Majalisar Taraba Usman Ya Fice Daga APC

August 4, 2025
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane Da Dama A Kauyukan Zamfara

August 4, 2025
Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi

Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.