ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PSC Ta Kori Jami’an ‘Yansanda 3 Kan Rashin Ladabi Da Biyayya

Ta Kara Wa Manyan Jami'ata 109 Girma

by Khalid Idris Doya
3 years ago
PSC

Hukumar kula da harkokin ‘yansanda ta kasa (PSC), a ranar Laraba ta amince da korar ‘yansanda uku masu mukamin mataimakan Sufuritendan (ASPs) sannan, ta kuma rage mukamin mai taimakawa kwamishina (ACP), babban Sufuritendan, wasu jami’ai biyu masu mukamin Sufuritendan da wani mataimakin Sufuritendan bisa kama su da laifuka daban-daban da suka hada da rashin da’a/ladabi da biyayya hadi da wasu laifukan.

Hukumar ta kuma amince da tsawatarwa/gargadi mai tsanani ga wani mataimakin kwamishinan ‘yansanda, babban Sufuritenda, da Sufuritenda su hudu, da wasu mataimakan Sufuritendan (DSP) su biyu hadi da masu taimaka wa Sufuritendan ‘yansanda su 12 (ASPs).

  • Kasar Sin Ta Yi Kira Da A Gaggauta Tsagaita Bude Wuta A Sudan

Hukumar ta cimma wannan matsayar ne a zamanta karo na 20 da ya gudana a ranar Laraba a shalkwatar hukumar da ke Jabi, Abuja wanda shugaban hukumar kuma tsohon Sufeto-janar na ‘yansanda, Dakta Solomon Arase ya jagoranta.

ADVERTISEMENT

Kakakin hukumar, Ikechukwu Ani, a sanarwar da ya fitar ranar Laraba da daddare, ya shaida cewar hukumar ta kuma amince da hukuncin gargadi mai tsauri ga wasu jami’ai shida da Sufuritenda daya da mataimakan Sufuritendan guda biyar.

Kazalika, hukumar ta kuma amince da karin girma ga wasu manyan jami’an hukumar su 109.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

Shugaban hukumar wanda a karonsa na farko ke nan ya jagoranci zaman hukumar tun bayan nada shi da shugaba Buhari ya yi, ya taya sabbin jami’an da suka samu karin girman murna, sai ya kalubalancesu da su kari ninka kokarinsa domin sauke nauyin da ke rataye a wuyayensu wajen gudanar da aiki yadda ya dace.

Dr. Arase ya ce, dole ne su tashi tsaye su kara azama da himma domin kyautata aikin hukumar PSC.

Ya bada tabbacin cewa karin girma ga Jami’ai na daga cikin muhimman abubuwan da zai sanya a gaba, amma fa sai ya ce dole ne sai kowani jami’i zai ji cewa a shirye yake ya kara kokari wajen sauke nauyin da ke kansa.

Kazalika, shugaban na PSC ya nemi ‘yansanda da a kowani lokaci suke gudanar da ayyukansu biya tafiya kan ka’idar da dokokin da aka gindaya domin kyautata aikinsu.

Ya ce, matakin ladabtarwa zai sauka kan duk jami’an da aka kama da aikata laifuka kuma a hukuntasu daidai da laifukansu domin cigaba da tsarkake bangaren aiki da tabbatar da aikin dan sanda na tafiya bisa kwarewa.

PSC
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
Zaben Gwamnan Adamawa: Kotu Ta Kori Karar Da Binani Ta Kai INEC

Zaben Gwamnan Adamawa: Kotu Ta Kori Karar Da Binani Ta Kai INEC

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.