• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Putin Ya Gana Da Wang Yi

by CMG Hausa
3 years ago
Putin

Shugaban kasar Rasha Vladimir Putin a jiya Laraba ya gana da mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin kana darektan ofishin hukumar kula da harkokin waje ta kwamitin kolin, a birnin Moscow, babban birnin kasar ta Rasha.

A yayin ganawar, Mr. Wang Yi ya ce, ba domin wani bangare na uku ne Sin da Rasha ke bunkasa huldar da ke tsakaninsu a sabon zamanin da ake ciki ba, haka kuma duk wani bangare na uku ba zai iya haifar da tasirinsa a kan huldar ba, ballantana a ce ya haifar da barazana. Kasar Sin na son hadin kai da Rasha, su karfafa amincewa da juna ta fannin siyasa da ma inganta hadin gwiwa ta fannin tsare-tsare, tare kuma da fadada hakikanin hadin gwiwa a tsakaninsu, don kiyaye halastacciyar moriyarsu, da kuma taka rawar da ta dace ta fannin kiyaye zaman lafiya da ci gaba na duniya.

  • Binciken Ya Nuna Shugaba Putin Bai Da Lalurar Kwakwalwa – CIA

Shugaba Putin a nasa bangaren ya ce, yanzu haka huldar dake tsakanin kasashen biyu na bunkasa kamar yadda ake fatan gani, inda kasashen biyu suka cimma gaggaruman nasarori a hadin gwiwar da ke tsakaninsu ta fannoni daban daban da ma cikin kungiyar hadin gwiwa ta Shanghai da kuma kungiyar BRICS, baya ga kuma yadda suka inganta hadin kai a cikin al’amuran duniya, wanda hakan ke da muhimmiyar ma’ana wajen kiyaye dimokuradiyya a huldar kasa da kasa da kuma daidaito a tsarin kasa da kasa.

Kasashen biyu sun kuma yi musayar ra’ayoyi a kan batun Ukraine, inda Wang Yi ya yaba da yadda Rasha din ta nanata niyyarta ta daidaita batun ta hanyar yin shawarwari.

Wang Yi ya ce, kasar Sin za ta ci gaba da tsayawa a kan matsayin adalci, don ba da gudummawa ta fannin daidaita batun a siyasance. (Lubabatu Lei)

LABARAI MASU NASABA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki
Daga Birnin Sin

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka
Daga Birnin Sin

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Next Post
Tsarin MIDAS Ya Kawo Sauyin Yadda Ake Kula Da Iyakoki —Jere

Tsarin MIDAS Ya Kawo Sauyin Yadda Ake Kula Da Iyakoki —Jere

LABARAI MASU NASABA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

November 5, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.