ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Binciken Ya Nuna Shugaba Putin Bai Da Lalurar Kwakwalwa – CIA

by Rabi'u Ali Indabawa
4 years ago
Putin

Babu wata hujja da ke nuna cewa Shugaban Rasha Bladimir Putin na da tabin hankali ko kuma yana fama da lalurar kwakwalwa, a cewar Shugaban Hukumar Leken Asiri ta Amurka CIA.

An yi ta samun jita-jita a baya-bayan nan cewa Mista Putin, wanda ke cika shekara 70 da haihuwa a 2022, na fama da rashin lafiya kamar cutar daji, wato kansa.
Sai dai William Burns ya ce babu wata hujja da ke tabbatar da hakan, yana mai cewa “da alama ma lafiya ta yi masa yawa”.

  • Asarar Da Ukraine Ke Tafkawa Duk Wata A Yakinta Da Rasha

Ita ma Fadar Kremlin ta Rasha ta yi watsi da ikirarin rashin lafiyar shugaban a matsayin “labarin boge”.

ADVERTISEMENT

Lamarin na zuwa ne yayin da Amurka ke cewa za ta aika wa Ukraine karin makamai masu dogon zango.

Tun farko Ministan Harkokin Wajen Rasha Sergei Labrob ya ce yanzu muradin Rasha ba wai “kwace gabashin Ukraine ba ne kawai”, yana mai cewa manufarta ta sauya sakamakon ba wa Ukraine irin wadannan makamai.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

‘Mutumin da ya yi imani da karfin iko’
“Akwai jita-jita mai yawa game da lafiyar Shugaba Putin kuma mu dai abin da muka sani shi ne yana cike da koshin lafiya,” a cewar Mista Burns yayin wani taro na tsaro mai taken Aspen Security Forum a Colorado.

Da yake mayar da martani cikin raha, ya kara da cewa kalaman nasa ba su ne karshe ba game da rahoton hukumomin leken asiri.

A ranar Alhamis ta makon jiya ne Fadar Kremlin ta musanta batun rashin lafiyar ta Mista Putin bayan wasu da suka kira kansu “kwararru kan tattara bayanai” sun yada labarai daban-daban kan lafiyar shugaban.

“Amma ba wani abu ba ne illa labarin karya,” kamar yadda kakakin Putin, Dmitry Peskob, ya fada wa manema labarai.

Mista Burns wanda ya yi aiki a matsayin jakadan Amurka a Moscow, ya ce ya sha yin hulda da shugaban na Rasha fiye da shekara 20.

Mista Putin “ya tasirantu da karfin iko, da tilasta wa mutane, da ramuwar gayya” kuma wadannan halaye sun kara tsauri cikin shekara 10 da suka wuce yayin da adadin mashawartansa ke kara raguwa, a cewar shugaban na CIA.

“Ya yi imanin cewa kaddara ce ta shardanta masa a matsayinsa na shugaban Rasha ya mayar da kasar kan turbar iko. Yana ganin babbar hanyar yin hakan ita ce ya fadada iko a makwabtansa kuma ba zai iya yin hakan ba har sai ya samu iko kan Ukraine.”

Mista Burns ya je Moscow a watan Nuwamba don yin gargadi ga Rasha idan ta sake ta afka wa Ukraine bayan sun samu rahotannin shirin yin hakan.
Sai dai Shugaban na CIA ya ce ya bar kasar “cikin damuwa fiye da sanda ya shige ta”.

Ya kara da cewa: “Putin ya yi imani sosai da manufarsa.
Na sha jin sa yana fada a boye tsawon shekaru cewa Ukraine ba cikakkiyar kasa ba ce.
“To, cikakkun kasashe na iya mayar da martani kuma abin da Ukraine ke yi ke nan.”

Amurka ta yi hasashen cewa an kashe dakarun Rasha kusan 15,000 a Ukraine kuma an raunata wasu kusan 45,000, in ji Mista Burns.

Putin
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Sarkin Zazzau Ya Umarci A Soke Wasu Al’adu Da Ke Kawo Wa Aure Cikas

MASU ALAKA

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci
Manyan Labarai

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

July 7, 2026
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz
Manyan Labarai

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano
Labarai

Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

July 7, 2026
Next Post
Tsohon Sakataren Gwamnatin Nijeriya, Babachir Lawal Da Dogara Sun Ziyarci Wike A Ribas

Tsohon Sakataren Gwamnatin Nijeriya, Babachir Lawal Da Dogara Sun Ziyarci Wike A Ribas

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

July 7, 2026
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

July 7, 2026
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

ADC Ta Zargi Gwamnatin Tinubu Da Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 17 Cikin Yunwa

July 7, 2026
Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026
Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

Shugabannin Sin Da Montenegro Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.