• English
  • Business News
Wednesday, July 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Qatar 2022: ‘Yan Asalin Afirka Da Tauraruwarsu Ke Haskawa A Wasu Kasashe

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
in Wasanni
0
Qatar 2022: ‘Yan Asalin Afirka Da Tauraruwarsu Ke Haskawa A Wasu Kasashe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A babban taron hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA karo na 70, wanda aka yi a watan Satumbar shekara ta 2020, mambobin hukumar sun amince da wani canji na damar buga wa kasashe wasa.

Sai dai kafin wannan lokacin, doka ta bayyana cewa duk dan wasan da ya bugawa kasa wasa guda daya ba zai sake zuwa wata kasar ya buga mata wasa ba har karshen rayuwar sa wanda a haka aka dade ana tafiya.

  • Pogba Ya Ce Barayi Suna Yi Masa Barazana

Sai dai a babban taron na FIFA karo na 70, an amince cewa idan dan wasa ya buga wasa daya zai iya canja kasar da yake so a gaba har sai idan wasa uku ya buga, hakan yana nufin idan dan wasa ya buga wa kasa wasa uku na wata gasar ba shi da damar zuwa wata kasar ya buga mata wasa.

A gasar cin kofin duniyar da a yanzu haka ake ci gaba da fafata wa a kasar Qatar, akwai ‘yan wasa da dama daga nahiyar Afirka da suke buga wa kasashen da bana Afirka ba:
Dan wasa Musab Kheder: Dan wasan baya, yana buga wa kasar Qatar wasa ne sai dai a birnin Khartoum na kasar Sudan aka haife shi kuma yana buga wasanninsa a kungiyar Al-Sadd ta kasar Qatar.

Ansu Fati: Shima zakakurin dan wasa ne wanda yake wakiltar tawagar ‘yan wasan kasar Spaniya sai dai an haife shi ne a kasar Guinea-Bissau kafin ya koma kasar Spain tun yana dan karamin yaro.

Labarai Masu Nasaba

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

Alphonso Dabies: Matashin dan wasa wanda yake buga wasan sa a kungiyar kwallon kafa ta Bayern Munchen ta kasar Jamus, dan wasan mai shekara 22 a duniya, yana buga wasa a tawagar kasar Canada amma kuma an haife shi ne a birnin Budurburam na kasar Ghana.

Eduardo Camabinga: Kwararren dan wasa ne wanda yake buga wasa a kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid kuma yana wakiltar kasar Faransa ne amma kuma an haife shi ne a sansanin ‘yan gudun hijira na Angola bayan da iyayensa suka gudu daga kasar Congo amma kuma ya girma a Faransa.

Youssoufa Moukoko: Dan wasa ne wanda yake buga wasa a kungiyar kwallon kafa ta Borrusia Dortmund dake kasar Jamus amma kuma an haife shi ne a babban birnin kasar Kamaru wato Yaounde kuma kawo yanzu yana da shekara 18 a duniya.

Danilo Pereeira: Dan wasan na kungiyar kwallon kafa ta Paris Saint German mai shekara 31 a duniya yana wakiltar kasar Portugal ne a wasannin kasashe amma kuma a kasar Guinea-Bissau aka haife shi.
Stebe Mandanda: Mai tsaron ragar kungiyar kwallon kafa ta Rennes ta kasar Faransa yana wakiltar tawagar ‘yan wasan kasar ta Faransa ne amma kuma an haife shi ne a Jamhuriyar Dimokradiyar Congo.

Breel Embolo: Dan wasan da a yanzu yake wakiltar kasar Switzerland a wasannin kasa da kasa kuma yana buga wa kungiyar kwallon kafa ta Monaco ta kasar Faransa, an haife shi a babban birnin kasar Kamaru wato Yaounde.

Mohammed Muntari: Mai shekara 28 a duniya an haife shi ne a kasar Ghana amma kuma yana buga wasa a tawagar ‘yan wasan kasar Qatar tare da kungiyar kwallon kafa ta Al-Duhail dake Qatar.

Amadou Onana: Dan wasan mai shekara 28 a duniya an haife shi ne a babban birnin kasar Senegal wato Dakar amma yanzu yana wakiltar tawagar ‘yan wasan kasar Belgium ne a wasannin kasa da kasa kuma yana buga wasa a kungiyar kwallon kafa ta Eberton ta kasar Ingila.

William Cavalho: Dan wasan yana buga wasa a kungiyar kwallon kafa ta Real Betis ta kasar Spain kuma yana wakiltar tawagar ‘yan wasan kasar Portugal ne a wasannin kasa da kasa amma kuma a kasar Angola aka haife shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Goron Juma’a

Next Post

FIFA Za Ta Hukunta ‘Yan Wasan Uruguay Hudu

Related

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata
Wasanni

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

1 day ago
An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari
Wasanni

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

2 days ago
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa
Wasanni

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

3 days ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Wasanni

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

4 days ago
Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?
Wasanni

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

4 days ago
Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr
Wasanni

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

6 days ago
Next Post
FIFA Za Ta Hukunta ‘Yan Wasan Uruguay Hudu

FIFA Za Ta Hukunta ‘Yan Wasan Uruguay Hudu

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

July 1, 2025
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

July 1, 2025
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

July 1, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

July 1, 2025
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.