• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Qatar 2022: ‘Yan Asalin Afirka Da Tauraruwarsu Ke Haskawa A Wasu Kasashe

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
Qatar

A babban taron hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA karo na 70, wanda aka yi a watan Satumbar shekara ta 2020, mambobin hukumar sun amince da wani canji na damar buga wa kasashe wasa.

Sai dai kafin wannan lokacin, doka ta bayyana cewa duk dan wasan da ya bugawa kasa wasa guda daya ba zai sake zuwa wata kasar ya buga mata wasa ba har karshen rayuwar sa wanda a haka aka dade ana tafiya.

  • Pogba Ya Ce Barayi Suna Yi Masa Barazana

Sai dai a babban taron na FIFA karo na 70, an amince cewa idan dan wasa ya buga wasa daya zai iya canja kasar da yake so a gaba har sai idan wasa uku ya buga, hakan yana nufin idan dan wasa ya buga wa kasa wasa uku na wata gasar ba shi da damar zuwa wata kasar ya buga mata wasa.

A gasar cin kofin duniyar da a yanzu haka ake ci gaba da fafata wa a kasar Qatar, akwai ‘yan wasa da dama daga nahiyar Afirka da suke buga wa kasashen da bana Afirka ba:
Dan wasa Musab Kheder: Dan wasan baya, yana buga wa kasar Qatar wasa ne sai dai a birnin Khartoum na kasar Sudan aka haife shi kuma yana buga wasanninsa a kungiyar Al-Sadd ta kasar Qatar.

Ansu Fati: Shima zakakurin dan wasa ne wanda yake wakiltar tawagar ‘yan wasan kasar Spaniya sai dai an haife shi ne a kasar Guinea-Bissau kafin ya koma kasar Spain tun yana dan karamin yaro.

LABARAI MASU NASABA

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane

Alphonso Dabies: Matashin dan wasa wanda yake buga wasan sa a kungiyar kwallon kafa ta Bayern Munchen ta kasar Jamus, dan wasan mai shekara 22 a duniya, yana buga wasa a tawagar kasar Canada amma kuma an haife shi ne a birnin Budurburam na kasar Ghana.

Eduardo Camabinga: Kwararren dan wasa ne wanda yake buga wasa a kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid kuma yana wakiltar kasar Faransa ne amma kuma an haife shi ne a sansanin ‘yan gudun hijira na Angola bayan da iyayensa suka gudu daga kasar Congo amma kuma ya girma a Faransa.

Youssoufa Moukoko: Dan wasa ne wanda yake buga wasa a kungiyar kwallon kafa ta Borrusia Dortmund dake kasar Jamus amma kuma an haife shi ne a babban birnin kasar Kamaru wato Yaounde kuma kawo yanzu yana da shekara 18 a duniya.

Danilo Pereeira: Dan wasan na kungiyar kwallon kafa ta Paris Saint German mai shekara 31 a duniya yana wakiltar kasar Portugal ne a wasannin kasashe amma kuma a kasar Guinea-Bissau aka haife shi.
Stebe Mandanda: Mai tsaron ragar kungiyar kwallon kafa ta Rennes ta kasar Faransa yana wakiltar tawagar ‘yan wasan kasar ta Faransa ne amma kuma an haife shi ne a Jamhuriyar Dimokradiyar Congo.

Breel Embolo: Dan wasan da a yanzu yake wakiltar kasar Switzerland a wasannin kasa da kasa kuma yana buga wa kungiyar kwallon kafa ta Monaco ta kasar Faransa, an haife shi a babban birnin kasar Kamaru wato Yaounde.

Mohammed Muntari: Mai shekara 28 a duniya an haife shi ne a kasar Ghana amma kuma yana buga wasa a tawagar ‘yan wasan kasar Qatar tare da kungiyar kwallon kafa ta Al-Duhail dake Qatar.

Amadou Onana: Dan wasan mai shekara 28 a duniya an haife shi ne a babban birnin kasar Senegal wato Dakar amma yanzu yana wakiltar tawagar ‘yan wasan kasar Belgium ne a wasannin kasa da kasa kuma yana buga wasa a kungiyar kwallon kafa ta Eberton ta kasar Ingila.

William Cavalho: Dan wasan yana buga wasa a kungiyar kwallon kafa ta Real Betis ta kasar Spain kuma yana wakiltar tawagar ‘yan wasan kasar Portugal ne a wasannin kasa da kasa amma kuma a kasar Angola aka haife shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0
Wasanni

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane
Wasanni

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane

October 7, 2025
Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni
Wasanni

Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni

October 6, 2025
Next Post
FIFA Za Ta Hukunta ‘Yan Wasan Uruguay Hudu

FIFA Za Ta Hukunta ‘Yan Wasan Uruguay Hudu

LABARAI MASU NASABA

Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

October 10, 2025
Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

October 10, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

2027: INEC Ta Nemi A Gaggauta Amincewa Da Ƙudirin Sake Fasalin Tsarin Zaɓe

October 10, 2025
Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari’a Da Inganta Shugabanci A Duniya

Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari’a Da Inganta Shugabanci A Duniya

October 10, 2025
Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya

Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya

October 10, 2025
Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

October 10, 2025
An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi 

An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi 

October 10, 2025
Nijeriya

Haramcin Haƙar Ma’adanai: Majalisa Za Ta Kawo Ƙarshen Asarar Dala Biliyan 9 Duk Shekara

October 10, 2025
Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

October 10, 2025
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)

Yadda Za A Magance Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya – TRCN

October 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.