ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Qatar 2022: ‘Yan Asalin Afirka Da Tauraruwarsu Ke Haskawa A Wasu Kasashe

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
Qatar

A babban taron hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA karo na 70, wanda aka yi a watan Satumbar shekara ta 2020, mambobin hukumar sun amince da wani canji na damar buga wa kasashe wasa.

Sai dai kafin wannan lokacin, doka ta bayyana cewa duk dan wasan da ya bugawa kasa wasa guda daya ba zai sake zuwa wata kasar ya buga mata wasa ba har karshen rayuwar sa wanda a haka aka dade ana tafiya.

  • Pogba Ya Ce Barayi Suna Yi Masa Barazana

Sai dai a babban taron na FIFA karo na 70, an amince cewa idan dan wasa ya buga wasa daya zai iya canja kasar da yake so a gaba har sai idan wasa uku ya buga, hakan yana nufin idan dan wasa ya buga wa kasa wasa uku na wata gasar ba shi da damar zuwa wata kasar ya buga mata wasa.

ADVERTISEMENT

A gasar cin kofin duniyar da a yanzu haka ake ci gaba da fafata wa a kasar Qatar, akwai ‘yan wasa da dama daga nahiyar Afirka da suke buga wa kasashen da bana Afirka ba:
Dan wasa Musab Kheder: Dan wasan baya, yana buga wa kasar Qatar wasa ne sai dai a birnin Khartoum na kasar Sudan aka haife shi kuma yana buga wasanninsa a kungiyar Al-Sadd ta kasar Qatar.

Ansu Fati: Shima zakakurin dan wasa ne wanda yake wakiltar tawagar ‘yan wasan kasar Spaniya sai dai an haife shi ne a kasar Guinea-Bissau kafin ya koma kasar Spain tun yana dan karamin yaro.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Alphonso Dabies: Matashin dan wasa wanda yake buga wasan sa a kungiyar kwallon kafa ta Bayern Munchen ta kasar Jamus, dan wasan mai shekara 22 a duniya, yana buga wasa a tawagar kasar Canada amma kuma an haife shi ne a birnin Budurburam na kasar Ghana.

Eduardo Camabinga: Kwararren dan wasa ne wanda yake buga wasa a kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid kuma yana wakiltar kasar Faransa ne amma kuma an haife shi ne a sansanin ‘yan gudun hijira na Angola bayan da iyayensa suka gudu daga kasar Congo amma kuma ya girma a Faransa.

Youssoufa Moukoko: Dan wasa ne wanda yake buga wasa a kungiyar kwallon kafa ta Borrusia Dortmund dake kasar Jamus amma kuma an haife shi ne a babban birnin kasar Kamaru wato Yaounde kuma kawo yanzu yana da shekara 18 a duniya.

Danilo Pereeira: Dan wasan na kungiyar kwallon kafa ta Paris Saint German mai shekara 31 a duniya yana wakiltar kasar Portugal ne a wasannin kasashe amma kuma a kasar Guinea-Bissau aka haife shi.
Stebe Mandanda: Mai tsaron ragar kungiyar kwallon kafa ta Rennes ta kasar Faransa yana wakiltar tawagar ‘yan wasan kasar ta Faransa ne amma kuma an haife shi ne a Jamhuriyar Dimokradiyar Congo.

Breel Embolo: Dan wasan da a yanzu yake wakiltar kasar Switzerland a wasannin kasa da kasa kuma yana buga wa kungiyar kwallon kafa ta Monaco ta kasar Faransa, an haife shi a babban birnin kasar Kamaru wato Yaounde.

Mohammed Muntari: Mai shekara 28 a duniya an haife shi ne a kasar Ghana amma kuma yana buga wasa a tawagar ‘yan wasan kasar Qatar tare da kungiyar kwallon kafa ta Al-Duhail dake Qatar.

Amadou Onana: Dan wasan mai shekara 28 a duniya an haife shi ne a babban birnin kasar Senegal wato Dakar amma yanzu yana wakiltar tawagar ‘yan wasan kasar Belgium ne a wasannin kasa da kasa kuma yana buga wasa a kungiyar kwallon kafa ta Eberton ta kasar Ingila.

William Cavalho: Dan wasan yana buga wasa a kungiyar kwallon kafa ta Real Betis ta kasar Spain kuma yana wakiltar tawagar ‘yan wasan kasar Portugal ne a wasannin kasa da kasa amma kuma a kasar Angola aka haife shi.

Qatar
Abba Ibrahim Wada
+ postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Har Yanzu Nijeriya Tana Fatan Zuwa Kofin Duniya Na 2026
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Mece Ce Matsalar Real Madrid? 
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Ko Ka San Dalilin Da Zai Bai Wa Nijeriya Damar Zuwa Gasar Cin Kofin Duniya?

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
Wasanni

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
Wasanni

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

June 2, 2026
Next Post
FIFA Za Ta Hukunta ‘Yan Wasan Uruguay Hudu

FIFA Za Ta Hukunta ‘Yan Wasan Uruguay Hudu

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.