• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ra’ayoyinku A Kan Halin Da Fasinjojin Jirgin Kasan Da Aka Sace Ke Ciki (Ra’ayi)

by Aisha Seyoji
3 years ago

Barkanmu da sake saduwa a filin Ra’ayi Riga, wannan mako mun kawo muku Ra’ayoyinku ne a kan Bidiyon nan na fasinjojin da ‘yan ta’adda suka sace a jirgin kasan nan da ya fito daga Abuja zuwa Kaduna, inda ake azabtar da su.

Wani matakin gaggawa kuke ganin yakamata gwamnati ta dauka don ceto su?

Ummu Maimuna Yumnah
Gwamnati dai ta nuna gazawarta, sai muci gaba da addu’ar Allah ya kubutar da duk wani wanda yake hannusu cikin aminci, mu kuma Allah ya karemu fadawa hannun wadannan azzaluman da ba su san Allah ba.

Lami S Mudu
Ina addu’ar Allah ya fitar dasu daga hannun wadannan mutane ubangiji Allah ya kawo musu dauki, domin suna cikin wani hali ubangiji ya dube su mu kuma Allah ya dada kare mu amin!

Yøûsüf ẞæ ßæ Sø
Gaskiya yakamta ace gwamnatin Nijeriya ta jajirice wajen kwato wadannan bayin Alhah da aka sace
Sai dai kuma gashi tana nuna gazawarta a kan haka sai dai mu jajirce da addu’a

LABARAI MASU NASABA

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

Matashi Ya Kashe Kakanninsa Kan Abinci A Kano

Widad Isma’il
Gashi dai har yanzu shiru kake ji, Allah ya jikan maza (Abacha) na yi imanin inda yana raye wannan rashin imanin da halin ko in kula da ake nuna wa talaka ba zai yarda ba koda kuwa baya kan mulki.
Amma shuwagabani ku ji tsoron Allah ku sani Allah ba zai barku ba.

Omar Naseer Imam
Mafitanmu guda daya ne, kuma ita ce madogararmu wato addu’a, gaskiya suna cikin musifa, Allah ya kawo masu mafita albarkan Annabi (S.A.W)

Sani Ladan
Tabbass wannan lamarin ya daure wa mutane kai, yanzu dai takai matsayar hatta magoya bayan gwamnati sun amince ta gaza, haka kuma mu talakawan kasa ya dace mu natsu mu dau matakin addu’a da tashi tsaye don kare kanmu da kanmu tunda gwamnati ta kasa muna addua’r Allah ya kubutar dasu, mu dake gidajenmu Allah ya shiga tsakanin mu dasu.

Abdurrashid Ahmad Abubakar
Lamarin sai addu’a, amma duk wani mataki da yakamata a dauka gwamnati ta sani kuma tana ji, sai dai muce Allah ubangiji ya basu Ikon kubuto da mutanen nan, Allah Ya kara kiyayemu

Sameenu Reina Dambatta
Allah ya kawo wa talakan Nijeriya mafita

Idriss Aminudeen
Ai matakin kenan mu kara kaimi wajen yi musu addu’a, amma indai gwamnati muke jira su dauki mataki to mun makara. Allah ya kubutar dasu

Mujitaba Suleiman
Allah ya hada yan ta’adda fada tsakanin su da masu daukar nauyinsu

Nazifi Haruna Iliyasu
Ai sai dai nace Allah ya fitar dasu daga hannun wannnan ‘yan ta’addan domin kuwa gwamnati ta gaza baza ta iya ba.

Bello Bello
Kaicho rayuwar talakan Nijeriya abin tausayi, Allah ya kawo mana dauki

Maman Aisha
Allah ya kawo mana dauki ya kubutar dasu Allah ya saka musu wannan zaluncin

Ummu Ibrahim
To ni abin da yake bani mamaki ta yaya suka tsayar da jirgin kasar har suka kwashe mutanen

Amb Ibrahim Adam Dan-Sarauta
Wannan al’amari babu wani mataki da Gwamnati za ta iya dauka face mu yi ta addu’a Allah ya kawo mana karshen wannan fitina don ta nuna mana ta gaza.
Amma maganar gaskiya gwamnatin Nijeriya ba za ta iya bawa al’umma kariya daga rashin tsaro da yake afkuwa ba.

Shamsi Umar Bakanike Dambatta
Da farko dai mu dage da addu’a dare da rana duk lokacin da mu kayi sallah bawai sai abu ya faru ba muce kai ai wannan abin sai dai addu’a kuma baza mu yi addu’a ba kamar yadda muke fadin idan abu ya faru muke cewa ai abin sai dai addu’a da addu’ar muke yi haka da tuni mun samu mafita a wajen Allah [S.W.T] da fatan al’umma zamu tsaya mu zage dantse wajen yin addu’a dare da rana a kan Allah [S.W.T] ya kawo mana karshen wannan matsala na rashin tsaro da ya addabi wannan kasa tamu Nijeriya dama duniya baki daya.

Sani Bello Kano
Abin akwai ban tausayi da bakin ciki, ita kuma wannan gwamnatin sai dai mu yi ta addu’a, saboda inda ace gwamnati tana da niyar kawo karshen rashin tsaro da tuni abin ya zama labari, amma kullum sai maganar siyasar suce a gaban su, ai sun san inda ‘yan ta’addan suke da zama ba wai basu sani ba, Allah shi ne zai mana maganin duk wani ciwo da yake damun mu, su kuma Allah ya kawo musu mafita

Nuruddeen Muhammad Funtua
A gaskiya ra’ayina shi ne yakamata ace gwamnati tunda ta gaza karbosu to ta bawa iyalasu damar biyan kudin fansar don su fanshi iyalansu

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Al'ajabi

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

October 17, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
Al'ajabi

Matashi Ya Kashe Kakanninsa Kan Abinci A Kano

September 25, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
Al'ajabi

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
Next Post
Fatima

Dole A Hada Kai Don Yaki Da Miyagun Kwayoyi - Hajiya Fatima

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.