ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ra’ayoyinku A Kan Halin Da Fasinjojin Jirgin Kasan Da Aka Sace Ke Ciki (Ra’ayi)

by Aisha Seyoji
4 years ago

Barkanmu da sake saduwa a filin Ra’ayi Riga, wannan mako mun kawo muku Ra’ayoyinku ne a kan Bidiyon nan na fasinjojin da ‘yan ta’adda suka sace a jirgin kasan nan da ya fito daga Abuja zuwa Kaduna, inda ake azabtar da su.

Wani matakin gaggawa kuke ganin yakamata gwamnati ta dauka don ceto su?

Ummu Maimuna Yumnah
Gwamnati dai ta nuna gazawarta, sai muci gaba da addu’ar Allah ya kubutar da duk wani wanda yake hannusu cikin aminci, mu kuma Allah ya karemu fadawa hannun wadannan azzaluman da ba su san Allah ba.

ADVERTISEMENT

Lami S Mudu
Ina addu’ar Allah ya fitar dasu daga hannun wadannan mutane ubangiji Allah ya kawo musu dauki, domin suna cikin wani hali ubangiji ya dube su mu kuma Allah ya dada kare mu amin!

Yøûsüf ẞæ ßæ Sø
Gaskiya yakamta ace gwamnatin Nijeriya ta jajirice wajen kwato wadannan bayin Alhah da aka sace
Sai dai kuma gashi tana nuna gazawarta a kan haka sai dai mu jajirce da addu’a

LABARAI MASU NASABA

EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas

Yadda Aka Gano Ƙasusuwan Dabba Mai Shekara Miliyan 100 A Nijar

Widad Isma’il
Gashi dai har yanzu shiru kake ji, Allah ya jikan maza (Abacha) na yi imanin inda yana raye wannan rashin imanin da halin ko in kula da ake nuna wa talaka ba zai yarda ba koda kuwa baya kan mulki.
Amma shuwagabani ku ji tsoron Allah ku sani Allah ba zai barku ba.

Omar Naseer Imam
Mafitanmu guda daya ne, kuma ita ce madogararmu wato addu’a, gaskiya suna cikin musifa, Allah ya kawo masu mafita albarkan Annabi (S.A.W)

Sani Ladan
Tabbass wannan lamarin ya daure wa mutane kai, yanzu dai takai matsayar hatta magoya bayan gwamnati sun amince ta gaza, haka kuma mu talakawan kasa ya dace mu natsu mu dau matakin addu’a da tashi tsaye don kare kanmu da kanmu tunda gwamnati ta kasa muna addua’r Allah ya kubutar dasu, mu dake gidajenmu Allah ya shiga tsakanin mu dasu.

Abdurrashid Ahmad Abubakar
Lamarin sai addu’a, amma duk wani mataki da yakamata a dauka gwamnati ta sani kuma tana ji, sai dai muce Allah ubangiji ya basu Ikon kubuto da mutanen nan, Allah Ya kara kiyayemu

Sameenu Reina Dambatta
Allah ya kawo wa talakan Nijeriya mafita

Idriss Aminudeen
Ai matakin kenan mu kara kaimi wajen yi musu addu’a, amma indai gwamnati muke jira su dauki mataki to mun makara. Allah ya kubutar dasu

Mujitaba Suleiman
Allah ya hada yan ta’adda fada tsakanin su da masu daukar nauyinsu

Nazifi Haruna Iliyasu
Ai sai dai nace Allah ya fitar dasu daga hannun wannnan ‘yan ta’addan domin kuwa gwamnati ta gaza baza ta iya ba.

Bello Bello
Kaicho rayuwar talakan Nijeriya abin tausayi, Allah ya kawo mana dauki

Maman Aisha
Allah ya kawo mana dauki ya kubutar dasu Allah ya saka musu wannan zaluncin

Ummu Ibrahim
To ni abin da yake bani mamaki ta yaya suka tsayar da jirgin kasar har suka kwashe mutanen

Amb Ibrahim Adam Dan-Sarauta
Wannan al’amari babu wani mataki da Gwamnati za ta iya dauka face mu yi ta addu’a Allah ya kawo mana karshen wannan fitina don ta nuna mana ta gaza.
Amma maganar gaskiya gwamnatin Nijeriya ba za ta iya bawa al’umma kariya daga rashin tsaro da yake afkuwa ba.

Shamsi Umar Bakanike Dambatta
Da farko dai mu dage da addu’a dare da rana duk lokacin da mu kayi sallah bawai sai abu ya faru ba muce kai ai wannan abin sai dai addu’a kuma baza mu yi addu’a ba kamar yadda muke fadin idan abu ya faru muke cewa ai abin sai dai addu’a da addu’ar muke yi haka da tuni mun samu mafita a wajen Allah [S.W.T] da fatan al’umma zamu tsaya mu zage dantse wajen yin addu’a dare da rana a kan Allah [S.W.T] ya kawo mana karshen wannan matsala na rashin tsaro da ya addabi wannan kasa tamu Nijeriya dama duniya baki daya.

Sani Bello Kano
Abin akwai ban tausayi da bakin ciki, ita kuma wannan gwamnatin sai dai mu yi ta addu’a, saboda inda ace gwamnati tana da niyar kawo karshen rashin tsaro da tuni abin ya zama labari, amma kullum sai maganar siyasar suce a gaban su, ai sun san inda ‘yan ta’addan suke da zama ba wai basu sani ba, Allah shi ne zai mana maganin duk wani ciwo da yake damun mu, su kuma Allah ya kawo musu mafita

Nuruddeen Muhammad Funtua
A gaskiya ra’ayina shi ne yakamata ace gwamnati tunda ta gaza karbosu to ta bawa iyalasu damar biyan kudin fansar don su fanshi iyalansu

Aisha Seyoji
+ postsBio
  • Aisha Seyoji
    https://hausa.leadership.ng/author/aisha-seyoji/
    Mata Mu Kara Hakuri A Zamantakewar Aure -Aisha Seyoji
  • Aisha Seyoji
    https://hausa.leadership.ng/author/aisha-seyoji/
    Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
  • Aisha Seyoji
    https://hausa.leadership.ng/author/aisha-seyoji/
    Ra’ayoyinku A Kan Ba Da Bashi Ga Daliban Manyan Makarantu
  • Aisha Seyoji
    https://hausa.leadership.ng/author/aisha-seyoji/
    Abin Haushi, Mata Sun Mayar Da Maza Tamkar Bola

MASU ALAKA

EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas
Al'ajabi

EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas

April 21, 2026
Yadda Aka Gano Ƙasusuwan Dabba Mai Shekara Miliyan 100 A Nijar
Al'ajabi

Yadda Aka Gano Ƙasusuwan Dabba Mai Shekara Miliyan 100 A Nijar

March 8, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Al'ajabi

Ɓata-gari Sun Kashe Matar Aure Da ’Ya’yanta 3 A Kano

January 21, 2026
Next Post
Fatima

Dole A Hada Kai Don Yaki Da Miyagun Kwayoyi - Hajiya Fatima

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.