• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ra’ayoyinku A Kan Wa’adin Buhari Ga Jami’an Tsaro Na Kawo Karshen ‘Yan Ta’adda

by Aisha Seyoji
2 years ago
in Labarai
0
Sauran Kwanaki 25 Cikin Wa’adin Kwana 31 Da Aka Ba Wa Jami’an Tsaro Na Kawo Karshen ‘Yan Ta’adda
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yau mun kawo ra’ayoyinku ne a kan wa’adin zuwa ranar 31 ga watan Disamba da Shugaba Buhari ya ba jami’an tsaron na su kawo karshen ayyukan ta’addanci a Nijeriya. Shin akwai yiwuwar cimma wannan wa’adin kuwa? Ga bayanan da mas bibiyar ska yi

Comr Isma’il Ibrahim Gusau
Wannan labarin mun saba jinshi ga bakin shugaban kasa da manyan masu ruwa da tsaki a kan sha’anin tsaro, ba’a biyo hanyar magance matsalar tsaro ba a Nijeriya, tayaya za a ce dan ta’adda yafi gwamnati mallakar makamai kaga harkar tsaron kasar nan akwai lauje cikin nadi.

Kuma idan ka duba ko yaushe magana daya ce suke yi wa ‘yan kasa babu wani sauyi da ake samu itace tun yana danye ake lankwasa shi, amma yanzu kam sunyi sake, duk abinda baka gyara ba shekara bakwai da rabi yanzu wane gyara akeso ayi. Allah dai ya zaba muna shugabanni nagari.

Muhd Basheer Sa’ad
An dade ana ruwa kasa tana shanyewa! Kawo yanzun dai mun san wannan magana ta Shugaban Buhari kanzon kurege ce.
Domin kuwa a baya ya fadi hakan kuma babu abunda ya sauya. Abunda ya kamata kawai mu mika al’amuran mu ga Ubangiji kawai domin shi ne zai yi mana maganin su.

Abubakar Mohammed Joda
Muna fatan alkhairi a kullum ga jami’an tsaronmu, muna kuma addu’ar Allah ya kawo mana karshen ta’addanci a yankunanmu. Amma dai karya da farfagandar gwamnatin nan babu wanda bai ganeshi ba izuwa yanzu.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Real Miftahu Ahmad Panda
Ni dai ina ganin, abu ne mawuyaci hakan ya iya yiwuwa (ma’ana a iya kawo karshen ayyukan ta’addanci, a cikin wannan wa’adi), duba da yadda a baya ma, shugaban ya sha bada irin wannan umarni ga hafoshin tsaron kasar nan, amma shiru ka ke ji. Sai dai kuma, ba ma ce mun yanke kauna baki daya da yiwuwar hakan ba.

Fatan mu dai, Allah ya kawo mana karshen wadannan matsalolin tsaro da su ka ta’azzara, musamman ma a yankin Arewacin Nijeriya.

Amb Ibrahim Adam Dan-Sarauta
Ai ko wanda ba dan Nijeriya ba idan ya samu wannan labari ya san cewa abu ne da ba zai yiwu ba.

Balle mu da ke rayuwa cikin kasar kuma yankunan da ta’addancin ya ke faruwa.
Maganar Gaskiya ko da Buharin da kansa zai fito ya yi aikin tare da Jami’an tsaro ina mai tabbatar miki da cewa ba za a iya kawo karshen abin a wa’adin da aka diba ba.
Abin da ya fi dacewa da mu shi ne Addu’a. Allah ya kawo mana karshen wannan ta’addanci ya ba mu shuwagabanni na gari. Wanda za su nuna jin zafin abin ta yadda za a magance matsalar.

Khadija Muhammad
Da ikon Allah mu kasance masu fatan nasara ba màganganun banza ba

Mohammed Inuwa
Wannan mataki da Shugaban Kasa ya dauka ya yi daidai. Domin kadan akwi kayan aiki da hakan zai yiwu InshaaAllah. Kuma muna addu’a da kara bawa gwamnati hadin kai. Allah kawo kasarmu zaman lafiya.

Comr Hassan S Umar
Idan kin san abinda ake cewa shifcin Gizo! To wannan shi ne Shifcin Gizo, magance matsalar tsaro yana daya daga cikin 3 majors na abubuwan da suka kafa gwamnatin Buhari A 2015 saboda tsananin takura da harin ‘yan ta’adda a Nijeriya musamman Arewa. Amma gashi yau shekara kusan 8, an kusa kamala wa’adi na biyu amma.

Kar ku manta a wannan gwamnatin aka samu kungiyar ikirarin jihadi ta (ISWAP) a yankin arewa maso gabas.
Kar ku manta a wannan gwamnatin aka samu harkokin garkuwa da mutane a yankin arewa maso yamma da arewa ta tsakiya, haka kuma a wannan lokacin ne aka samu ayyukan ‘yan tawayenh Biyafra ya kara karuwa. Muna dai rokon Allah ya taimaka wa jami’antsraomu donj su samju nasarar da ake bukata a kan ayyukan ‘yanta’adda a sassan Nijeriya

Sulaiman Muhammad
Gaskiya mai girma shugaban kasa yasha fadin haka saboda babu wani abu da zai canza.
Domin matsalar tsaron Nijeriya akwai Turawan yamma da Amurka da ‘yan Nijeria da masu mulkin Nijeria duk sun san komai basu yi niyar gyaran ba ne

Widad Isma’il
Allah ya basu ikon aiwatar da abinda zamu yi masu shi ne addua, amma gaskiya al’amarin tsaro abin dubawa ne tunda har za a iya kamo wanda suke cin zarafin manya a hukuntasu, a ganina kamo wadanda suke ta’addanci binciko su abu me sauki, inda gaske ake yi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Man Kolmani: Yaushe Za A Fara Cin Moriyarsa?

Next Post

Gwamnatin Kano Ta Kulla Yarjejeniya Da Makarantar Morocco Kan Harkar Noma

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

2 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

3 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

4 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

9 hours ago
Jami'an tsaro
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

9 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

10 hours ago
Next Post
Jami'an tsaro

Gwamnatin Kano Ta Kulla Yarjejeniya Da Makarantar Morocco Kan Harkar Noma

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.